← Book details Sadaukarwa So Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 54 OF 94

Sashe 54

Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 4 min read

Mommy ta karisa ta Zauna Dukkansu suka Ramkwafa suna gaisheta ta amsa Cikim kulawa Daddy ya kalleta yana Fadin"Mastur zai koma bakin aiki gobe..Shima Mansur goben Abuja zai tafi Taron su na Siyasa.."
Mommy ta washe baki Tana Fadin"Masha Allahu..Allah ya kiyaye Hanya kace duka zaku bar ya"yan nawa da kewa kenan..? Tafada Tana yar Dariya Daddy yace"A"a ai itama Rumana gobe Zata je Chan asibitin Chika din ko..? Yafada yana kallon Rumana Dake Zaume kasa gefen kafafun Mommy Kai ta gyada Tana Fadin"Eh Daddy..."Daddy ya kada kai yana Fadin"Ai munyi mgana da Abban naki dazu yace ya baki Lambar Dr Hambali da zaki nema in kinje Chan asibitin ko..? Rumana tace"Eh ya Turomin Daddy..Zan nemeshi da Zaran na Shiga asibitin Insha Allahu.."Daddy ya jinjina kai yana Fadin"Shikenan Allah bada sa"a..Ki kirani indai gobem kikaje kika ga akwai wani mtssla kin ji ko..? Rumana tace"Insha Allahu Daddy.."Mommy tace"Allah ya Taimaka Ruma..Ita Diza ai inaga sai ta kara Hutawa Saboda Tana da Ma"aikata sosai a wajen.."Daddy yace"Ai nata aikin ba wani mtsala bane ba kamar na Rumana ba ita Data karancin Harkan Lafiya.."Diza Ta Fito keman Taji Daddy na Fadin sai taji kamar ta koma ammh ba Hali wato ita Bata da wani Feature mai kyau tunda batayi karatu ba sai Rumana ya zama Dole itama Gobe ta koma Catering dinta ba wanda zata ma gadin gida.
Ita bazata zauna akasa ba Gefen Mommy ta zauna tana wani Yamusta Fuska nan Daddy Shima da Mommy suka kara Musu Nasiha kafin su tashi suyi Shirin Tafiya,ba wanda ya Taba wani abu sai Mansur Daya sha Ruwa Har Haraban Gidan Mommy da Daddysuka Rakosu suna musu Fatan alheri Dayake Motar a wajen suka barta Kofar gidan su Hajja Mommy nayi ta yi ma Rumana Godiya Bayan ta gayama Daddy gabansu Mansur Shima sai saka mata albarka yake Dalilin Da Yasa Diza taji ta kara Tsanar wannan Fitan da sukayi yau tare da Rumana.

Gidan su Hajja suka koma sukayi musu sallama Bayan Mastur ya Shiga Shashensu Dake kulle yanszu ya Dauki wasu Takardu suka wuce sun bar anguwan Misalin 10:30pm na Dare wannan karon ba wanda ke mgana Harta Mamsur din yayi gum ganin Diza ma ta Hade rai duk sai ya Shiga Damuwa Suna komawa Gidan Bayan Mansur yayi parking a parking Space Suka Firfito Mastur wucewa yayi Dauke da Takardun Hannunsa Rumana ne ta Tsaya tana cema Mansur sai da Safe da Sauri yace mata"Ai shiga zamu yi Shashen ku tare da Diza..Bamu taba Shigowa tare ba.."Rumana kamar ta sani ta kalli Diza sai ta kamata Tana Hararan Mansur kamar idonta zai Fado kasa,baki kawai ta Tabe ta wuce Tana Fadin"Maraban ku.."Mansur yabi Bayanta Yana Rike da Hannun Diza Dake bankamai Harara yayi kamar bai ganta ba..
Mastur ya riga ya Bude kofar Shashen shiga kawai sukayi Wlh Diza Kin zama Tayi mansur ya zauna yana ce mata ta Zauna Daga Tsaye ta Coge tana karw ma Falon kallo Take fadin"Bafa zama zamu yi ba..Ni kam barci nake ji.."Rumana Dake tsaye da kamar Zataje ta kawo musu Ruwa sai ta Fasa Kawai jin Abunda Diza tace Mastur Daman koda suka Shigo ya Shige Ciki ko yana Jinsu ma bai leko ba.
Mansur da kunyan Abunda Diza Tayi ya Ishesa sai ya Mike yana kallon Rumana yace"Anty Rumana bari muje sai da safe..Tunda tana jin barci in na Dawo Duk Ranar dana Dwo nan zamu yi Dinner ranar."Rumana ta saki Mirmishi Tana Fadin'"Is ok..Allah ya kaimu Allah ya kiyaye hanya."Ya amsa da Ameen Yana Fadin"Yaya Mastur ya Shiga Ciki ko..? Rumana ta gyada kai kawai Mansur sai ya kama Hannun Diza yana Fadin"Shikenam zamu hadu gobem kafin ya tafi..Sai da Safe.."Rumana tabi bayansu Har suka Fice ta maida Kofa ta Rufe aranta tana ayyana Diza Da ta Koyo wasu mugayen Hallayar me ta mata ta Tsaneta ta rasa Dalilin haka itama ta Gaji Hasken Falom kadai ta Rage ta Shige Bedroom dinta gyalen da Jakar kan gado ta watsar ta Fada tiolet ta Rage mara Tayo wanka tazo ta saka Kayan Barci tabi Lafiyan gado Tana ganin Missedcall din Basma Ta kirata Lokacin suna gidan Su Diza sai bata Daga ba sai taace bari zuwa Safe sai ta Kirata.

*Shakira...*
1/1/22, 18:54 - Maryam Badmsi: *SS....25*

*Ki biya ki karanta cikin salama 09069067488 Mace mai aji mallakan komai nata take yi bata jiran abun sata*

"Rumana ta kwanta da Sanin cewa gobe zata Fara zuwa Aikinta Shiyasa barcin nata ya zama Ragagge ne Karfe 5:30pm tatashi Daga Barci ta Fara Shiryan Shiryanta ta Fito da Kayan da zata saka tare da Karamar jakarta Hadi da Takalmin Jakar ta saka Takardan da suka bata a Uduth Saboda kada ta manta,Bata manta da cewa yau Mastur zai koma Wajen aikinsa ba ko bakomai Miji yake gareta kuma akwai hakkinsa akanta Shiyasa ta Fita Zuwa Kitchen ta Dibo masa Cake da Cincin da Donut,Ta samu wani Roba Duka ta Cika mai kananan Wasu Robobi ne masu kyau Duka ukun Ta saka su ta Mai rapping dinsu,Sai tayi Tunanin tayi mai Miya wanda in yaje zai Dinga Dafa wani abu yana ci Tunda chan bai da kowa kuma Girki kamar zai mai Wahala.
Chapter 54 · 0% Book details