← Book details Sadaukarwa So Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 72 OF 94

Sashe 72

Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tana Kokarin kwanciya Mastur ya Shigo Dakinta Tana Sanye da Rigar barci iyakarta Gwiwa mai karamin Hannu,Idanuwanta sun kumbura tayi kuka Har tagaji Tayi mamakin ganin Mastur acikin Dakinta Cikin wani yanayi Take kallonsa Tama manta a wani Hali Take Ciki Shima Din kallonta yake Tundaga Sama Har kasa Cikin Wani yanayi wanda bazai iya Fassara shi ba.
Cikin Sanyinsa ya fara Takowa Zuwa gabanta Sai da suka zo Gabda kana ya Dakata yana Sauke Numfashi Cikin Dakiya da Raunin muryab Data kamashi Bayan Rasuwar Mansur yace"Kiyo alwala muyi Sallah..!
Yafada Lokaci Daya yana Nufar ma"ajiyar Dardumanta ya Dauka ya Daidaici gabas ya Shinfida kana ya waigo yana kallon Rumana Data kasa Motsi Idanuwanta ya Ciko da kwallah ita duk a Tunaninta,Salla da addu"an neman ma Mansur Gafaran Allah yau zaku kwana yi ita da Mastur.
Shi kuwa ganinta Tsaye yasa ya kara gyaran Murya yana Fadin"Baki ji bane Rumana..?
Sai alokacin Ta iya Motsawa tana Fadin"Ina da alwalata.."Lokaci Daya Tana juyawa ga Wardrope dinta ta Bude ta Dauko Dogon Hijabinta ta isa garesa ganinta yasa ya Daidaita Sahu ya Tada Sallah itama ta Daidaita ta Bishi Basu Tsawaita ba abun mamaki Raka"a Biyu sukayi Yayi musu addu"an Zaman Lafiya Daga karshe ya Rokar ma Mansur Gafara da Rahma wajen Allah.
Kana ya Juyo yana kallon Rumana Cikin wani yanayi da kuma Rasa ta ina Zai fara ita kuma kanta na kasa Tana wasa da gefen Hijabinta ganin sun Zauna Shuru yasa ta Dago kanta Ta gansa yayi Zuru kawai yana kallon Gabansa kamar mai nazarin wani abu Tun bayan Rasuwar yau suka samu kadaicewa su kadai yasa ta Bude baki Cikin Wani irin Rauni tace"Ya hakurin Hakuri kuma..? Allah jikan Mansur Allah yamai Rahma..!
Tafada Lokaci Daya Kwallah Suna Zubo mata.
Cikin wani irin Sarewa ya Bude baki yace mata"Hakuri namu ne Duka Rumana..Bamu kadai muka yi Rashin Mamsur ba Mutane Da Dama sun yi Rashi..Allahu albar..Allah ya Rahamaheka Mansur Allah ya Kyautata makwancinka..!
Yake fada Cikin karaya kamar zai Fashe da kuka Cikin kuka Rumana ke amsawa da Ameen Mastur Cikin Wani irin Duba ya Dubi Rumana yana Fadin"Gani nake kamar ba gaskiya ba..Gani nake kamar Mansur yayi Wata Tafiya ne zai Dawo Watarana..Na ji Rauni ya kamani na Tsorata Rumana naji kamar na Fadi kasa ina Birgima Lokacin Dana ga gawan Dan"uwana Cikin Jini..Wlh kullim sai nayi mafarkinsa Bana iya barci bana iya Runtsawa Rumana na Rasa kanina Dan"uwana mafi Soyuwa gareni Na kasa Duka na kasa Wannan Dauriyan ina Neman wata Kafada inda Zan kwanta nayi kuka..Kuka na Dacin daya Kwanta acikin Zuciyata yana Sukani Tamkar Nima zai yi Sanadiyar Ajalina haka nake ji Rumana..Taba kirjina kinji yadda Zuciyata ke Bugawa da Sauri da Sauri ko..? To wlh Tana Bugawa da ambaton sunan Mansur na kasa yarda Mansur ya Tabi ya Barmu Ru...ma...na..!
Mastur ya karishe Fada muryansa ta karyewa Lokaci Daya kuma ya Damki Hannunta Guda Daya ya Damke Saman kirjinsa Tana jin irin Bugun Zuciyarsa Cikin Sauri da Sauri Bata ankara ba Taga Hawayensa Masu Zafi suna Zuba saman hannunta Cikin Razana take kallonsa ganinsa yana kuka karon Farko a Rayuwarta sai taji itama bata da karfin gwiwan Rike Rauninta bata san sanda ta Karisa garesa da Rarrafe ba sai ji Tayi ta Fada Jikinsa ta Rumgumesa kamkam Tana Fadin"Yi kuka..Ka Zubar da Hawaye ya Mastur..Kayi kuka a kafadana ni Rumana har sai kaji Zuciyarka Tayi Sanyi.."Take Fada Cikin kuka itama Da karfi ya Kamkameta kamar wani Zai kwaceta ya Saki kukan Dayake ta Rikewa Wajen kwana Goma Haka ya Dinga kuka yana kamkame da ita,itama kukan take tana Shafa Bayansa alamun Lallashi Tun Suna Zaune har dai basu san Lokacin da sukayi malale Saman Cafet din Bedroom din ba Mastur Tusa kansa yake saman Kirjin Rumana yana kuka kamar wani karamin yaro ita kuma Tana Shafa Sumar kansa Cikin Tsausayi da Soyayyah mai Tsanani.
Rumana bazata iya Fadin yaushe ne Da wani Lokacin ne Lamarin ya Fara ba..? Sai da ta Tsinci kanta Hannun Mastur Dumu Dumu yana Sarrafata Cikin Zafi Lokaci Daya kuma Idanuwansa na Zubar kwallah Tana cikin Dimuwa na karon na Farko Jin wannan bakon Lamarin ga kuma Jikinta da ba karfi ga Yanayin Mastur Daya kara Sakata ta Sakamar Duka Ragaman Rayuwarta ta Mika wuya ita dai baxata iya cewa komai ba Tadai jita Saman Kafadan Mastur ya Mikar da ita kafin taji ya Dagata sama Lokaci Daya kuma Taji su sun Fada Saman gado Abubuwan da suka Faru Dukkansu sun Faru ne yadda Basu yi Tsammani ba Mastur ya karbi Budurci Rumana Cikin Fitan Hayyaci da kuma Dacin Mutuwa da Nadaman hakkinta Dake kansa ita kuma Rumana bazata iya Dora komai sai dai Abu Daya ta sani Lamarin yazo mata A bazata Domin batayi Tsammani ba, bata Zata ba kuma bata ma kawo ma kanta nan kusa ba sai ta Sanya hakan a wani Lamari da Allah ya Kaddara Zasu zamonta Daya ita da Mastur koma yane Koma wani yanayi ne abun ya Faru ta Daukeshi ta kuma Rikeshi a ranta ta kuma sakashi Cikin Jerin Ranakinta masu matukar Muhimmanci a Rayuwarta.
Mastur kuwa wani irin yanayi yajisa acikinsa wanda bai taba Shiga ba iya Tsawon Rayuwarsa Daman Tuni Rauninsa ya Bayyana Shiyasa yayi ta kuka Tunda Farkon Dare har Zuwa asubahi yanayin da baki Baxai iya Fadansa ba sai dai Zuciya ta Kisima ko ta auna ko ta kwatantan Bayan komai ya Lafa Haka Mastur ya kamkame Rumana yana kuka,kukan Farinciki Rahma da Raunin Rashin Tade tare dashi ammh Hakan bai Hanasa Tashi ya Taimaka ma Rumana ta Tsabtace Jikinta ba Shima haka ya Sauya musu Zanin gado suka koma suka kwanta Duk da Zazzabin Dake jikinsa da asuba ma Dakyar ya iya tashi yayi Salla ya koma sai gashi Rumana ce ta Mike Tana Taimakamishi ta bashi mgani yasha ya koma ya kwanta Duk da Halin Datake Ciki haka ta Rarrafa ta sama musu abun karyawa Gabadaya Ranar daga ita Har Mastur wuni sukayi suna Jinyar Juna Shi Jinyar Zuciya da na Rauni Hade da na gangar Jiki,ita kuma Rumana Jinyar Jikinta wanda Mastur yayi Sanadiyar Faruwarsa
Daga chan gida ba wanda ya Nemesu sai washegari ne Baba Habibu ya kira Mastur din awaya Lokacin ne yace baya jin Dadi Nan Baba Habibu yamai Sannu yace Daman Zasu je gaisuwa Gidan Direban Marigayi Mansur ne Mastur yace su tafi kawai in yaji sauki zai je kafin ya Tafi da yardan Allah.
Haka kuwa akayi Cikin kwana uku yaji Sauki Tunda Rumana na kula dashi Itama taji Sauki Tunda Tana kula da kanta Bakin aiki ne bata koma ba Har yanzu ammh Takai Report.
Ranar sukaje gaisuwan Shida Rumana Daganan suka yada Zango wajen Diza Allah Sarki Ta na nan Jiya iyau Mommy Dai ke kula da ita da komai nata Diza bata mgana sai kuka kawai Abun Tsausayi,Mastur ne ya Zauna yana ta Lallashinta da Nasihu Duk da Shima yana Bukatar hakan sai dai gwara shi Rumana ta Zage dantse wajen ganin Mastur bai Raunana Da yawa ba Duk da Ramin Dayake Cikin Zuciyarsa mai Zurfi ne Lokaci Daya Rumana bazata Taba Cikeshi ba.
Mastur ya sauya kamar bashi ba Ya Roki Rumana gafaran Abubuwan suka Gudana Bayan auransu kuma ta yafemai,Sun Fara Shimfida Rayuwarsu cikin Kyautatama Juna,da kuma Kiyaye Hakkin Juna Duk Kokarin Rumana na Mastur ya samu karfin Gwiwa sai dai Abunda bata sani ba Tuni ya Sare kuma ya gama Raunana Tun Lokacin Daya Tabbatar da ya raasa Mansur..

Haka Rayuwa ta Cigaba da gangarawa har Tsawon Sati Biyu da Rasuwar Mansur,Duka makusantan sun fara Saduda sai dai banda Diza hankula suka Fara komawa kanta Domin ta Lalace ta Fita Hayyacinta bata cin Abinci bata mgana bata wanka sai Mommy Ta matsa mata Tun Abun ana ganin Radadin Mutuwar ne har dai aka Fahinci Diza na Bukatar Taimako Sosau Mastur Dayaji haka Shi ya Dauki Diza da kansa zuwa asibiti aka Dubata batare da tayi gaddama ba Domin shi batamai gaddama,ko Abinci ne taki karba Mommy na kiransa yazo Yana cewa ta karba Zata Fara ci,kuma bata iya Hada ido Dashi Shikuwa yanzu duk Duniya tafi kowa bashi Tsausayi.
Likita ya Dubata har awon Ciki anyi mata Cikinta watansa Biyar Zata Fara zuwa awo nan da Lokaci kadan,shawarwari ya bata Domin ya aunata jininta ya yi sama Sosai ta saka Damuwa ga Cikin jikinta ya bata Shawarwari sosai na cin Abinci domin karin Lafiya ga ita kanta sa Jaririnta.
An bata mgangunan karin jini Dana Sanya Cin Abinci kana suka Dawo Gida Mastur ya Zaunar da ita yayi mata Lallashi tare da Rokonta ta Rika cin Abinci ta kuma Rika shan mgani Ta Daina yawan Tunani da kuka ko Saboda Jaririn Cikinta Zata Rasshu In tacigaba da yin haka Tamkar yadda ta rasa Mastur Diza sai Kuka ba mgana Daman Gobe zai koma bakin aiki nan yayi musu Sallama bai kuma Tafi ba sai da ya Tabbatar da Diza bata raasa komai ba taci abinci Rumana ta Taimaka mata tayi wanka Tasha mgani Har Tayi barci.
Gida ya isa nan ma yayi ma su Hajja Sallama sai kukan Mutuwan Mansur ta Dawo Sabuwa Allahu akbar,Koda suka koma Gida Mastur ya kara Damka Amanar Diza a hannun Rumana ta kuma mai alkawarin Kulawa da Diza da Abunda ke Cikinta da yardan Allah sun kwana suna Raya wannan Daren mai Cike da Tarihi Washegari Tun Safe ya tafi kaduna ya Hau Jirgi Cikin Rauni da wani Sarewwa Itama Aranar ta koma Bakin aiki ko yaya akayi mata gaisuwan Mansur sai taji kwallah Ballatana Mastur da har yakai Headquater dinsu baya Cikin Natsuwarsa Tabbas ya Sare..Wannan karon Rauninsa ya Bayyana Rashin Mansur garesa Tabbatar Rashin wani Gibi ne garesa Babba.
Sai washegarin Daya koma ya kira Chan Maruka Domin jin Jikin Baba Sule Tunda suka koma yake kwance bayajin Dadi jinJikin Har yanzu yasa ya Tura kudi a acctount din maryama masu yawa yace su kai Baba Sule asibitin Sauran suyi Hidiman Gida Hakika Baba Sule yayi kukan Rashin Dansa Mansur sai dai ya Fada afidi Da"ansa Daya ya Rasa Ammh bai Rasa Dayan D"an nashi ba wato Mastur.

*Shakira...*
1/1/22, 18:55 - Maryam Badmsi: *SS....32*

*Kibiya ki karanta cikin Salama da Aminci 09069067488*
Chapter 72 · 0% Book details