Sashe 12
Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kamar Daga sama sukaji Sallama Daga saman kansu Kusan alokaci Daya Hajja da Aiya suka Juyo zuwa ga Kofar Shigowa gidan suna kallom mai Sallama Idanuwansu ya sauka kan Wata Mata kyakyawa Fara yar Duma Duma Da ita bata da Tsawo kuma ba Gajera ba mai Fadin Fuska Tana Sanye da wani Leshi Daga ganinsa kasan bana kananan kudi bane sai Babban Mayafin Data saba akanta Kafarta Fara cikin wani Takalmi baki mai Tudu Fuskarta Cike da Fara"a Hannunta kuma rike da wata karamar Farar yarinya ce Jajir kamar atabata Jini ya Fito mai kama da Matar sai dai ita yarinya Doguwar Fuska gareta kuma bata da kiba Lange lange Take kamar ta Balle Tana Sanye Cikin Bulawis din yara Doguwar Riga Ja Iyakarta Gwiwanta kafanta sanye da Sandal na yara mai kyau Harda Safa mai kyau sai kanta da akayi mata Kitso Chuku Wanda aka Tufke mata Daga Tsakiyar kan da wasu Ribhon masu kyau Hannunta kuma na Dauke da wata katuwar Teddy Mai kyau ta Yar Bby kamar Tayi mgana itama an Chaba mata ado Kamar yadda Yarinya taci ado kamar Zata Gasan kyawawan mata.
Fuskar Mata ta washe da Fara"a ganin su Hajja Aiya ce ta amsa Sallaman Tana mata maraba Hakoranta ta Bude Farare Har da Hakorin makkanta wanda ya karaa mata kyau da kwarjini,Hajja ta Tsame Hannunta Daga wanke wanken Datake yi Ta Mike Tana Mata Maraba Dukkansu suna mata kallon Rashin Sani Daki Hajja ta Shiga ta Dauko karamar Tabaarma ta Shinfida mata Lokaci Daya tana mata Maraba Takalminta ta Cire ta zauna Tana Zaunar da yarinyar agefenta wacce take ta kalle Kalle Lokaci Daya tana ta wasa da Teddy ta Mansur Dake Tsaye gabadaya Hankalinsa na kan yarinyar da yar gunkin Bby Dake Hannunta gabadaya Tatafi Dashi Sabanin Mastur da Tunda suka Shigo Sau Daya ya Dago kai ya kallesu ya maida kansa yana Cigaba da karatunsa bai kara Dago kansa ba.
Hajja ta zauna gefenta Tana Fadin"Sannu da zuwa.."Lokaci Daya tana ijiye mata ruwa awani kofin Silba Mai kyau Amsa mata tayi Cikin Fara"a Lokaci Daya tana gaisheta kana ta Juya suna gaisawa da Aiya Ganin kamar suna mata kallon Rashin Sani yasa tace"Sunana Hajiya Asiya..Wannan yata ce Khadija muna kiranta da Diza..Daga nan gidan makotan ku da muka Tare kwanaki.."
Daga Hajja Har Aiya sai suka washe Baki Aiya tace"Allah Sarki..Sannu da zuwa.."Hajiya Asiya ta amsa Tana kallon Mansur Daya tsaya yana kallonsu Hannu ta Mikamai Tana Fadin"Sannu Boy..Taho mai sunanka..? Da sauri Mansur ya isa gareta Lokaci Daya yana gayamata sunansa Mansur Sulaoman Doguwa Dariya Hajiya Asiya Tayi tana Fadin"Wow...primary nawa kake..? Kai ya daga yana kallon Mastur Dake Zabga masa Harara sai Hajiya Asiya ta Daga kanta suka Hada ido da Mastur da Sauri ya kauda kai Cikin Sanyin Muryansa yace"Ina wuni Hajiya..? Mirmishi ta saki kafin tace"Lafiya lau..Ammh ni ba Hajiya sunana ba Inda Zaka kirani da Mommy kamar da yadda Diza Take Kirana Danaji Dadi.."Mamakinta ya kama su Aiya basu samu Zarafin mgana Ba Mansur yace"Mommy Mommy.."Har sau Biyu kumatunsa Ta shafa Tana Fadin"Eh..Daz my Boy..Mansur.."Tafada Cikin Fara"a Diza ce ta Tureshi Tana Fadin"Ba Mommy ka bace..Is my Mom.."Hajiya Asiya na Dariya Tace"Ke Diza abokin ki ne..Na yi muku Abota ko baki son Abokin wasa..? Da sauri ta Daga kai Tana Washe baki Kallon Mansur Hajiya Asiya Tayi Tana Fadin"Yauwa toh kaima ga kawa nayi maka Daman Halin ku yazo Daya...Diza itama akwai mgana Sosai kamar aku.."Hajja tayi Dariya Tana Fadin"Kice Zamu ce ta Tatar da muje mu..Mansur Surutunsa Har ya baci da son wasa.."Hajiya Asiya tace"Itama Hakan take..Diza akwai som wasa Sosai barin ma in taga yara Dayake Sokoto da muka Fara zama muna zuwa Gidajen Yan"uwa tana samun abokan wasa Buh Tunda muka Dawo kaduna Sai ta zama sai ita kadai Daga Sch sai gida gata da son wasa fa Toh nan din ma Hakane naji Dadi Dana Shigo naga kuma da yara Diza Taji Dadi sosai.."
Daga Aiya har Hajja Mirmishi Sukayi Hajja Tace"Allah Sarki.."Shuru ya Biyo baya kafin Aiya tace"Hajiya baki sha Ruwan ba.."Hajiya Asiya tayi Dariya kafin tace"Wlh nasha Ruwa Daga gida..Ammh bari nasha ko Kadan ne.."Lokaci Daya Tana Daukan Ruwan ba kyama bakomai Tasha kadan ta Ijiye Daidai Lokacin da Mastur ya Mike Dauke da Littafinsa ya Shiga Ciki Ta bisa da kallo kafin ta Dawo da kallonta kan Hajja Tana Fadin"wacece Matar Mallam Habibun mai mana karatu..?Nima Daga cikin gida ina Karuwa sosai Alhaji ma nata Godiya yace akara muku Godiya Allah ya saka.."
Wannan karon Aiya ce tace"Gata nan Hajara sunanta Ya'yanta na kiranta Hajja..'Ta fada Tana nuna Hajja Lokaci Daya tacigaba da Fadin"Ni kakarsu ce Danake Zaune dasu Aiya suke Kirana Daga Doguwa ta kano muka Dawo nan da zama Shekaru Biyar da suka gabata.."Hajiya Asiya tace"Allah Sarki..Haka Alhaji yace ku Mutanen kano ne ni kuma haifaffiyar garin Sokoto ce Mijina ma Haka sai dai shi Dan Tureta ne Dake Sokoto.."
Aiya Tace"Masha Allah Tureta ai babban gari ne.."Hajiya Asiya tace"Sosai ma Aiya garin nata samun Cigaba.."Aiya ta karkace Zama tama bar Tankaden Datakeyi Tana Fadin"Wannan yarinyar ita kadai ce Diyarki kenan Hajiya..? Hajiya Asiya ta juya Tana kallon Diza da Mansur Dake wasa da Teddy kamar sun Shekara tare Ta Murmusa kafin tace"Ita kadai gareni Aiya..Shekararmu Goma sha Biyar da Aure sannan Allah ya bamu ita Nasha Wahala wajen Haihuwarta kamar ban yi Rai ba..Sai kuma Allah ya Takaita abun Mahaifta ta samu Mtsala Tun lokacin aka Ciremin ita Diza ita kadai ce yarmu kuma Sanyin Idaniyanmu.."Aiya da Hajja Fuskarsu ta Nuna Jimani suka Hada baki wajen Fadin"Allah sarki..Allah ya rayata.."Ta amsa da Ameem kafin Ta kalli Hajja tana Fadin"Wanchan Daya shiga Dakin chan shima Da'n ki ne..?
Da Sauri Aiya tace"Itama Shi kadai ne D'anta Data Haifa..Itama kamar kece Tana da mtsala a Mahaifinta Tun wani bari Datayi Likitoci achan Doguwa sukace da wuya ta kara Haihuwa.."Hajja ta Sunkuyar Dakai bata so So Aiya ta Fadi haka ba ganin ai yau suka Taba Haduwa da Hajiyar Cikin Wani Jimami Hajiya Asiya tace"Kai..Allah ka bamu Ikon cin wannan Jarabawan..Shi Mansur fa..?
Tafada Tana Nuna Mansur da suke ta waasa da Diza da Sauri Hajja Ta tare Aiya Tana Fadin"Shima kamar D"a yake garemu..Maryama kanwar Mallam ita ta Haifesa bata ga ma abunda ta Haifa ba ta bar Gidan Duniya Ni na Shayar dashi Nice kamar makwafin Mahaifiyarsa.."Hajiya Asiya tace"Wayyo..Allah ya Jikanta..Aikuwa uwa kike garesa Domin Nonon Uwa Tankar wani Sinadarin Soyayyane Tsakanin uwa da Abunda ta Haifa Allah ya Raya mana su..Ammh Shi wanchan din sam bai da mgana ne..?
Aiya tace"Mastur kenan..Baban Mutum..Baya mgana kuma bata Dameshi ba Kirarinsa kenan Miskili kafi mahaukaci ban Haushi..Wlh sai yaron chan ya wuni bai cema kowa Kanzil ba Shi dai barsa ina zashi karatu ina ya Fito karatu kamar wani Baturen Ingila.."Hajiya Asiya da Hajja sukayi Dariya kai ta kada kafin tace"Allah sarki..Daman haka Allah ke Hallitan wasu Mutanen sam zaki ga mgana bata Damunsu.."
Hajja Tace"Shi kam Mastur abun nashi kamar cuta..Ka wuni Shuru baka mgana.."Tafada Cikin bayanna Jimaminta Hajiya Asiya tace"Ba fa Cuta bane..Haka suke irinsu Nature su ne haka.."Daganan sai Hira ta tsinke a tsakaninsu har Hajja tatashi tayi Talge,ta Dawo suka Cigaba da Hiransu sai ana gabd da kiran mangariba Tayi Shirin Tafiya Diza kuma tace bazata Bita ba Taga abokin waasa ganin haka yasa Hajiya Asiya ta kalli Hajja Tana Fadin"Hajja bari na barta Wajen Mansur..anjuma zan aiko Fadime mai aikina Tatafi da ita.."
Hajja Tace"Bakomai Hajiya.."Ta saka Takalminta Lokaci Daya Tana gyara zaman mayafinta Tana Fadin"Sai anjuman ku..Ammh fa Aiya zaku sha Fama da ita Bata jin mgana Ku kwabata kada tayi muku Barna.."Aiya tace"Ai muna da irinta Shima wannan da kike ganin ba jin mgana yake yi ba.."Dariya sukayi gabadayansu Har Kofar gida Hajja ta Rakata Tana Gayamata sai sun shigo Kafin ta Dawo Ta samu Aiya na kallon su Mansur Dake ta waasa Diza akwai baki sai Bashi Labarin Kaduna take da makarantansu da Daddyta dinta yayi mata kaza yayi mata kaza Hajja ta Dauki Sauran garin Tuwonta Tana Fadin"Gaskiya Daga Megidan har Matan gidan suna da Kirki..Jifa bamu shiga ba ita ta Shigo mana.."
Aiya Tace"Nima Zencen da nake yi kenan araina..Matar ta Burgeni ba Ruwanta Kalli yarinyar mana ki gani Daga gani bata da bakunta ballatana kyama ace wacce ke Rayuwa awannan gidan ne zaune anan Gidan Tana wasa cikin kasa.."Hajja Tace'"Irin Mansur ne ba Ruwansu..Ba irin megidan ki ba mai Tsoron mutane ba Yana jin anyi baki zai Shige Ciki yaki Fitowa kamar za"a yanka sa..Ka Fito Bakuwar Tatafi.."Ta Karishe Fada Tana Daga Murya Aiya na gefe Tana Dariya.
Yana Daga Cikin Dakin yana Jinta bai Fito ba sai da ya Kimta Littafan karatunsa waje Daya kana ya Fito Aiya ta Kallesa Tana Fadin"Har an fito Megidana..? Kai ya gyada mata bai yi mgana ba Mansur yake kallo da Diza Dake wasa kafin ya Isa bakin Rijiya ya isa ya saka Guga ya jawo Ruwa ya Ciccika Butoci Da Ruwa ya Dauki Daya ya kai ma Aiya Har gabanta ta karba tana sakamai albarka kallon Hajja yayi yana Fadin"Hajja ga ruwa nan in zaki yi alwala.."Zata Shiga Madafa da Garin Masara a Faranti tace"Tom Babban Mutum.."
Mirmishi yayi kafin ya Dauki Butan Dake da Ruwa ya Fada Makewayi Bai Dade ba ya Fito yana Tsugunnawa Lokaci Daya yana kallon Mansur yace Cikin Kakkuran murya kamar wani Babba"Mansur kabar wasan nan Baka ji an kira sallah bane..?
Dagowa yayi yana kallonsa bai basa Daman mgana ba ganin Diza Itama ta waigo Tana kallonsa Kansa ya Kada kawai yace"Kai da ita Duk ku zo ku Dauki Buta kuyi alwala.."Ayadda yake mgana kamar wani Babba Hatta Aiya Dake gefe sai da ta kara Jinjina ma Jarumtan Mastur Hajja na Madafi kuwa Sai da taMurmusa Miskilin Dan nata Jajirtattace ne Sosai kamar Ubansa.
Fuskar Mata ta washe da Fara"a ganin su Hajja Aiya ce ta amsa Sallaman Tana mata maraba Hakoranta ta Bude Farare Har da Hakorin makkanta wanda ya karaa mata kyau da kwarjini,Hajja ta Tsame Hannunta Daga wanke wanken Datake yi Ta Mike Tana Mata Maraba Dukkansu suna mata kallon Rashin Sani Daki Hajja ta Shiga ta Dauko karamar Tabaarma ta Shinfida mata Lokaci Daya tana mata Maraba Takalminta ta Cire ta zauna Tana Zaunar da yarinyar agefenta wacce take ta kalle Kalle Lokaci Daya tana ta wasa da Teddy ta Mansur Dake Tsaye gabadaya Hankalinsa na kan yarinyar da yar gunkin Bby Dake Hannunta gabadaya Tatafi Dashi Sabanin Mastur da Tunda suka Shigo Sau Daya ya Dago kai ya kallesu ya maida kansa yana Cigaba da karatunsa bai kara Dago kansa ba.
Hajja ta zauna gefenta Tana Fadin"Sannu da zuwa.."Lokaci Daya tana ijiye mata ruwa awani kofin Silba Mai kyau Amsa mata tayi Cikin Fara"a Lokaci Daya tana gaisheta kana ta Juya suna gaisawa da Aiya Ganin kamar suna mata kallon Rashin Sani yasa tace"Sunana Hajiya Asiya..Wannan yata ce Khadija muna kiranta da Diza..Daga nan gidan makotan ku da muka Tare kwanaki.."
Daga Hajja Har Aiya sai suka washe Baki Aiya tace"Allah Sarki..Sannu da zuwa.."Hajiya Asiya ta amsa Tana kallon Mansur Daya tsaya yana kallonsu Hannu ta Mikamai Tana Fadin"Sannu Boy..Taho mai sunanka..? Da sauri Mansur ya isa gareta Lokaci Daya yana gayamata sunansa Mansur Sulaoman Doguwa Dariya Hajiya Asiya Tayi tana Fadin"Wow...primary nawa kake..? Kai ya daga yana kallon Mastur Dake Zabga masa Harara sai Hajiya Asiya ta Daga kanta suka Hada ido da Mastur da Sauri ya kauda kai Cikin Sanyin Muryansa yace"Ina wuni Hajiya..? Mirmishi ta saki kafin tace"Lafiya lau..Ammh ni ba Hajiya sunana ba Inda Zaka kirani da Mommy kamar da yadda Diza Take Kirana Danaji Dadi.."Mamakinta ya kama su Aiya basu samu Zarafin mgana Ba Mansur yace"Mommy Mommy.."Har sau Biyu kumatunsa Ta shafa Tana Fadin"Eh..Daz my Boy..Mansur.."Tafada Cikin Fara"a Diza ce ta Tureshi Tana Fadin"Ba Mommy ka bace..Is my Mom.."Hajiya Asiya na Dariya Tace"Ke Diza abokin ki ne..Na yi muku Abota ko baki son Abokin wasa..? Da sauri ta Daga kai Tana Washe baki Kallon Mansur Hajiya Asiya Tayi Tana Fadin"Yauwa toh kaima ga kawa nayi maka Daman Halin ku yazo Daya...Diza itama akwai mgana Sosai kamar aku.."Hajja tayi Dariya Tana Fadin"Kice Zamu ce ta Tatar da muje mu..Mansur Surutunsa Har ya baci da son wasa.."Hajiya Asiya tace"Itama Hakan take..Diza akwai som wasa Sosai barin ma in taga yara Dayake Sokoto da muka Fara zama muna zuwa Gidajen Yan"uwa tana samun abokan wasa Buh Tunda muka Dawo kaduna Sai ta zama sai ita kadai Daga Sch sai gida gata da son wasa fa Toh nan din ma Hakane naji Dadi Dana Shigo naga kuma da yara Diza Taji Dadi sosai.."
Daga Aiya har Hajja Mirmishi Sukayi Hajja Tace"Allah Sarki.."Shuru ya Biyo baya kafin Aiya tace"Hajiya baki sha Ruwan ba.."Hajiya Asiya tayi Dariya kafin tace"Wlh nasha Ruwa Daga gida..Ammh bari nasha ko Kadan ne.."Lokaci Daya Tana Daukan Ruwan ba kyama bakomai Tasha kadan ta Ijiye Daidai Lokacin da Mastur ya Mike Dauke da Littafinsa ya Shiga Ciki Ta bisa da kallo kafin ta Dawo da kallonta kan Hajja Tana Fadin"wacece Matar Mallam Habibun mai mana karatu..?Nima Daga cikin gida ina Karuwa sosai Alhaji ma nata Godiya yace akara muku Godiya Allah ya saka.."
Wannan karon Aiya ce tace"Gata nan Hajara sunanta Ya'yanta na kiranta Hajja..'Ta fada Tana nuna Hajja Lokaci Daya tacigaba da Fadin"Ni kakarsu ce Danake Zaune dasu Aiya suke Kirana Daga Doguwa ta kano muka Dawo nan da zama Shekaru Biyar da suka gabata.."Hajiya Asiya tace"Allah Sarki..Haka Alhaji yace ku Mutanen kano ne ni kuma haifaffiyar garin Sokoto ce Mijina ma Haka sai dai shi Dan Tureta ne Dake Sokoto.."
Aiya Tace"Masha Allah Tureta ai babban gari ne.."Hajiya Asiya tace"Sosai ma Aiya garin nata samun Cigaba.."Aiya ta karkace Zama tama bar Tankaden Datakeyi Tana Fadin"Wannan yarinyar ita kadai ce Diyarki kenan Hajiya..? Hajiya Asiya ta juya Tana kallon Diza da Mansur Dake wasa da Teddy kamar sun Shekara tare Ta Murmusa kafin tace"Ita kadai gareni Aiya..Shekararmu Goma sha Biyar da Aure sannan Allah ya bamu ita Nasha Wahala wajen Haihuwarta kamar ban yi Rai ba..Sai kuma Allah ya Takaita abun Mahaifta ta samu Mtsala Tun lokacin aka Ciremin ita Diza ita kadai ce yarmu kuma Sanyin Idaniyanmu.."Aiya da Hajja Fuskarsu ta Nuna Jimani suka Hada baki wajen Fadin"Allah sarki..Allah ya rayata.."Ta amsa da Ameem kafin Ta kalli Hajja tana Fadin"Wanchan Daya shiga Dakin chan shima Da'n ki ne..?
Da Sauri Aiya tace"Itama Shi kadai ne D'anta Data Haifa..Itama kamar kece Tana da mtsala a Mahaifinta Tun wani bari Datayi Likitoci achan Doguwa sukace da wuya ta kara Haihuwa.."Hajja ta Sunkuyar Dakai bata so So Aiya ta Fadi haka ba ganin ai yau suka Taba Haduwa da Hajiyar Cikin Wani Jimami Hajiya Asiya tace"Kai..Allah ka bamu Ikon cin wannan Jarabawan..Shi Mansur fa..?
Tafada Tana Nuna Mansur da suke ta waasa da Diza da Sauri Hajja Ta tare Aiya Tana Fadin"Shima kamar D"a yake garemu..Maryama kanwar Mallam ita ta Haifesa bata ga ma abunda ta Haifa ba ta bar Gidan Duniya Ni na Shayar dashi Nice kamar makwafin Mahaifiyarsa.."Hajiya Asiya tace"Wayyo..Allah ya Jikanta..Aikuwa uwa kike garesa Domin Nonon Uwa Tankar wani Sinadarin Soyayyane Tsakanin uwa da Abunda ta Haifa Allah ya Raya mana su..Ammh Shi wanchan din sam bai da mgana ne..?
Aiya tace"Mastur kenan..Baban Mutum..Baya mgana kuma bata Dameshi ba Kirarinsa kenan Miskili kafi mahaukaci ban Haushi..Wlh sai yaron chan ya wuni bai cema kowa Kanzil ba Shi dai barsa ina zashi karatu ina ya Fito karatu kamar wani Baturen Ingila.."Hajiya Asiya da Hajja sukayi Dariya kai ta kada kafin tace"Allah sarki..Daman haka Allah ke Hallitan wasu Mutanen sam zaki ga mgana bata Damunsu.."
Hajja Tace"Shi kam Mastur abun nashi kamar cuta..Ka wuni Shuru baka mgana.."Tafada Cikin bayanna Jimaminta Hajiya Asiya tace"Ba fa Cuta bane..Haka suke irinsu Nature su ne haka.."Daganan sai Hira ta tsinke a tsakaninsu har Hajja tatashi tayi Talge,ta Dawo suka Cigaba da Hiransu sai ana gabd da kiran mangariba Tayi Shirin Tafiya Diza kuma tace bazata Bita ba Taga abokin waasa ganin haka yasa Hajiya Asiya ta kalli Hajja Tana Fadin"Hajja bari na barta Wajen Mansur..anjuma zan aiko Fadime mai aikina Tatafi da ita.."
Hajja Tace"Bakomai Hajiya.."Ta saka Takalminta Lokaci Daya Tana gyara zaman mayafinta Tana Fadin"Sai anjuman ku..Ammh fa Aiya zaku sha Fama da ita Bata jin mgana Ku kwabata kada tayi muku Barna.."Aiya tace"Ai muna da irinta Shima wannan da kike ganin ba jin mgana yake yi ba.."Dariya sukayi gabadayansu Har Kofar gida Hajja ta Rakata Tana Gayamata sai sun shigo Kafin ta Dawo Ta samu Aiya na kallon su Mansur Dake ta waasa Diza akwai baki sai Bashi Labarin Kaduna take da makarantansu da Daddyta dinta yayi mata kaza yayi mata kaza Hajja ta Dauki Sauran garin Tuwonta Tana Fadin"Gaskiya Daga Megidan har Matan gidan suna da Kirki..Jifa bamu shiga ba ita ta Shigo mana.."
Aiya Tace"Nima Zencen da nake yi kenan araina..Matar ta Burgeni ba Ruwanta Kalli yarinyar mana ki gani Daga gani bata da bakunta ballatana kyama ace wacce ke Rayuwa awannan gidan ne zaune anan Gidan Tana wasa cikin kasa.."Hajja Tace'"Irin Mansur ne ba Ruwansu..Ba irin megidan ki ba mai Tsoron mutane ba Yana jin anyi baki zai Shige Ciki yaki Fitowa kamar za"a yanka sa..Ka Fito Bakuwar Tatafi.."Ta Karishe Fada Tana Daga Murya Aiya na gefe Tana Dariya.
Yana Daga Cikin Dakin yana Jinta bai Fito ba sai da ya Kimta Littafan karatunsa waje Daya kana ya Fito Aiya ta Kallesa Tana Fadin"Har an fito Megidana..? Kai ya gyada mata bai yi mgana ba Mansur yake kallo da Diza Dake wasa kafin ya Isa bakin Rijiya ya isa ya saka Guga ya jawo Ruwa ya Ciccika Butoci Da Ruwa ya Dauki Daya ya kai ma Aiya Har gabanta ta karba tana sakamai albarka kallon Hajja yayi yana Fadin"Hajja ga ruwa nan in zaki yi alwala.."Zata Shiga Madafa da Garin Masara a Faranti tace"Tom Babban Mutum.."
Mirmishi yayi kafin ya Dauki Butan Dake da Ruwa ya Fada Makewayi Bai Dade ba ya Fito yana Tsugunnawa Lokaci Daya yana kallon Mansur yace Cikin Kakkuran murya kamar wani Babba"Mansur kabar wasan nan Baka ji an kira sallah bane..?
Dagowa yayi yana kallonsa bai basa Daman mgana ba ganin Diza Itama ta waigo Tana kallonsa Kansa ya Kada kawai yace"Kai da ita Duk ku zo ku Dauki Buta kuyi alwala.."Ayadda yake mgana kamar wani Babba Hatta Aiya Dake gefe sai da ta kara Jinjina ma Jarumtan Mastur Hajja na Madafi kuwa Sai da taMurmusa Miskilin Dan nata Jajirtattace ne Sosai kamar Ubansa.