← Book details Sadaukarwa So Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 63 OF 94

Sashe 63

Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 8 min read

Anyi haka da Sati Daya Diza ta tashi da zazzabi Har sai da Sukaje asibiti Shi da Mansur Rumana bata gida Tun Safe tatafi asibiti,Dalilin haka yasa Bayan sun Dawo Daga asibiti ya kira Hajja ya gayamata Diza Bata da Lafiya sunje asibiti an yi mata Text Zuwa gobe zasu je su karbo Tana Fama da Zazzabi mai Zafi da Ciwon kai tazo ta Taimaka mata Rumana bata nan,Hajja batayi kasa a gwiwa ba ta Ce ma Mardiya ta Shirya ta bata kudin Mashin tace taje Gidan su Diza Yayanta na Nenanta Jin haka yasa ta Shirya Tatafi ta iske Diza na kwance ba Lafiya Bayani yayi mata yace ta Zauna ta kula da ita kuma ta gyara Gidan Tayi Girki Shi zai Fita Fatan dawowa Lafiya Tayi mai ya Fita.
Maryama ita tayi komai Har girki Ita tayi Domin ta kware Rumana ta Koyamata komai,Diza Tashi kawai Tayi Taga Mardiya Tagama Komai taji Sauki Wanka Tayi tazo taci Abinci ta Dauki wayarta Tana kiran Missedcalls.
Rumana bata Dawo ba sai da yammah kuma Gidan ta Biya ta gaida su Hajja nan nema Ayya ke Fadamata Mardiya na Gidansu Wajen Diza ba Lafiya Tana jin haka bata Tsaya ba Tayi musu Sallama ta Wuce gida Ko Mommy bata biya ta gaidata ba Tana zuwa Gidan ko Shashenta Bata Shiga ba ta Shiga Shashen Diza ta Iskesu Dukkansu ita da Mardiya afalo suna kallo Mardiya na ganin Rumana Ta tareta da Fara"a Tana ta Rawan Jiki akanta Diza na zaune kamar ta Fashe Rumanan na mata ya ajiki Dakyar ta amsa,Saboda Rumanan ta Tura mata Haushi ta Dinga Jan Mardiyan da Hira wacce har abinci ta Zubo mata da lemo Jin ita ta Dafa yasa Rumana taci aikuwa Diza kamar ta Mutu tatashi Fuu kamar Zata tashi Sama ta Shiga ciki ba Dadewa ta Kwalama Mardiya kira Tana zuwa tace wai Ta mata Fentin Dankali Shi take Sha"awa Saboda bata son ganinsu Tare Mardiya na Fitowa ta Fadama Rumana Abunda Diza tace batayi mamaki ba sai ma Tayi Dariya Ta Mike ta mata sallama ta Fice Zuwa Shashenta Duk da Mardiya din ta mata akawarin Zuwa Wajen bayan ta gama Girkin bata zo ba Har washegari sai bata Damu ba Ranar Ta kama Lahadi bata da zuwa asibiti Barcinta taci sai chan bayan azahar tatashi Tayi gyaran Gida Ta Hada Tea ta sha ta zo Falo ta zauma Tana kallo,Sai La"asar ta Shiga Kitchen ta Dora Girki Dambu Take Sha"awa Daman Tazo da Bushashiyar Zogalenta da Aisha Bala ta zo mata dashi Daga gidansu Kuma Tana da Barjen Shinkafa wacce ta Kai gidan Hajja aka Kai mata Barje Shine yau tayi Dambu Dashi Domin shi take Sha"awa.
Bayan Ta gama komai Tayi wanka Tayi sallar mangariba ta Shiga wajen Diza ta Dubata da Jiki Sai Ta iske tana Salla Nan suka zauna suna Hira da Mardiya ta gayamata Tayi Dambu tace Za taci bata Tafi ba sai da Diza ta idar da Sallah har Cikin Bedroom dinta ta Bita ta gaisheta ta amsa tana wani cin ngani ita dai Rumana bata Tsaya bi ta kanta ba ta Fice ta barta.
Ashe tunda Diza taji Mardiya tace zata shiga wajen Rumana ta kasa ta Tsare ta Shiga sakata aiki Ta Hanata sakat Rumana kuma Tagaji da jiranta taji Shuru sai ta yanke Shawaran kiran Mardiya din Taji Lafiya Tajita Shuru.
Lokacin da Wayar Rumana ya Shigo Wayar Mardiya suna zaune afalo ita da Diza Tana shan Faten Dankalin Datayi mata Taji kiran wayar Kallo Ta sakarma Mardiya din Cikin alamun Zargi Dayasa ta kasa Daga wayar cokalin Hannunta ta ijiye Kafin Tace"Rumana ce ke kiran ki ko..?

Kai Mardiya ta Daga mata Lokaci Daya Tana Daga kiran Kafin Takai ga Karata a kunnenta Diza ta saki wani Dogon Tsaki Ta Fara Fadin"Wai ni binbin nin na miye Matar nan ke miki ne Mardiya..? Tafada Cikin gatsala da wani Rainin wayau wanda ya Dakatar da mardiya daga mgana da Rumana awaya sam ta manta ta Dauki wayar ta Bude baki Tana Fadin"Kamar ya Anty Diza..? Anty Ruma ce ke kirana Kuma Dambu tacemin Tayi nace mata Zan zo naci Hakan laifi ne..?

Dawani kallon ke baki isa ba Diza Ta Narkama Mardiya Haushinta ya kara kamata Kamar Rumanan ne ke gabanta tace"Aikin banza..Munafunci dai in Dambun kike Sha"awa bani da kayan yinsa ne ko kuwa Tsabar ita akomai sai ta Nuna Tafi kowa..? Daman ta saba nuna min Iko kan Komai nawa ina kyaleta Yanzu ai sai ta Kyale min ke ko banza Nice Dolenki Matar Yayanki Shakiki nake ita fa..? Matar Mastur ce ita ba Matar Mansur Sulaimam Doguwa bace.."
Ta KarisheFada kanta Tsaye ko ajikinta Mardiya ta saki baki Tana kallon Diza Cikin Firgici tace"Innalillahi yanzu sai kika sake maimaita wannan mganar..?
Tafada tana waige waige ko Mansur ya shigo sai idonta ya Fada kan wayarta daidai Lokacin Da Rumana tagama jin komai ta Datse kiran da Sauri Mardiya ta Dauki wayan ta Duba Kiran Minti 1har da wani abu Mikewa Tayi ta Dora Hannu akai Tana Fadin"Na shiga uku ni Mardiya Diyar Sule..!
Diza ta Datacigaba da Shan Fenten ta ta Dago Tana kallonta Bata samu Zarafin mgana ba Kamar Yaki sukaci Buga Kofar Shashen Falon Diza Sai mardiya ta Zabura Tana Fadin"Shikenan ta Faru ta kare..Gata nan ta zo.."Diza ta kalleta da mamaki kafin tace"Ke wai lafiyan ki kuwa..?ita waye tazo kuma?
Mardiya da Idamuwanta suka kawo kwallah tace"Anty Ruma ce..Itace wlh.Duk taji mganar da kikayi ashe na Dauki kiran ban sani ba ita kuma Bata kashe ba.."Gaban Diza ya fadi ammh sai ta Dake ta Mike tsye Tana kare Hade ranta kafin tace"Bude mata Kofa..Daduk Abunda Tazo. Dashi.Diza Diyar Sunusi Tureta na Daidai da ita.."Tafada tana Kara Tamke Fuska Tana kara Bude Hamci duk mardiya ta Rude Bata kaunar Wata Fitina tatashi ace sanadinta ne Ta karisa Jikin Kofan Tana addu"an Allah sa ba Ruman bace sai dai Bata karbu ba Domin Tana Budewa taci karo da Rumana wacce Fuskarta ba Annuri ko kadan kana Hango Tsabar Bacin rai da Fushi atare da ita Ko Gyale bata Yafo ba Daga ita sai Wata Doguwar riga da mayafinta Mardiya Tayi kasake Tana kallonta Kafin ta Bude baki Tace"Tsaya kiji Anty Ru."Bata karisa ba Rumana ta Tureta ta Shige Ciki,Tana Fadin"Ina Dizar Take..? Nazo ne ta kalli Idanuwana ta kara Maimaita min Mardiya Kanwar Mansur ce kadai ban da Mastur in gani in kina da kunya.."Ta Karishe Fada Cikin Fushi da Daga Murya Mardiya taja Salati bata karisa ba Ta karisa ga Diza Zata tare ta wacce ta Tsaya gaban Rumana kyam suna aika ma da juna kallon kallon Mardiya Zata yi mgana Rumana ta Daga mata Hannu Tana Fadin"Koma gefe Mardiya..Ba Fada nazo nayi da ita ba so nake naji da kunnena ta maimaita abunda ta Fada Domin awaya sai naji kamar ban ji Daidai ba."
Wata yar iskar Dariya Diza tasaki Kafin tace"Kunnen ki na Ciwo ne..?ko ke kurma ce Dr Rumana...?Tobari na gayamiki da amon Muryata yaddazata kiji Dakyau cewa nayi da kike wani Shishshigewa Mardiya kamar yadda kike Shigema kowa kanwar Mijin kice..?Ko kun Hadawani abu ne..? Inace Mardiya Kamwar Mansur ce kuma Nice nan Matarsa ba ke ba.."Rumana ta Sanadare Tana kallon Ikon Allah bata Taba zaton Diza bata Hankali ba sai yau.
Mardiya ce ta Fashe da kuka Tana Fadin"Haba Diza..Meyasa kike tamaimaita mgana Daya ne..? Ina kika Tabaganin Bambamcin Tsakanin ya Mansur da Ya mastur..?waya baki ikon Nuna wannan Bambamcin..?

Wani Dogon Tsaki Diza Taja Tana Fadin"Dole nagayamata..Naga ta Fara wuce iyaKarta.."Rumana ta Katse ta Da Fadin"Mardiya kanwar Mansur ce banda Mastur ko..?Diza ta karkace kai tace "Me suka Hada..? Goggonsa ce Mahaifiyar mansur kuma ta Rasu..? Mardiya Tatsaon Inna Zainabace sai ki gayamin ta inda kuka Hada dasu Rahma Sarkin Zumunci Ke..."
DIZA..."Bata karisa ba taji Muryan Mansur Cikin kaushi ya kirata Da amo mai karfi Dukkansu sai da suka Rude suka juya suna kallonsa Ashe ya Dade Tsaye yana jinta Idamuwansa sun yi Jajir Tunda takeda Mansur bata Taba ganinsa Cikim wannan yanayin ba bai tsaya neman Mgama ba ya Taka Cikin Zafin Nama gabam Diza bai yi wata wata ba ya Cira Hannu ya Zabga mata Tafin Daya Rudata ya Ruda Rumana da Mardiya suka ja baya suna Rawan Jiki Diza kuwa Hannunta Dafe da kunci Tana Shatatan Hawaye Mansur ya nunata Cikin wani irin Fushi yace"Akul dinki...Kada ki kuskura ki kara Fadin wannan mganar Daga bakin ki..Mastur Shakikin Da yake ga BabaSule..Haka Zalika Tsayayyen yaya yake ga Mansur da Maryama da Mardiya da Sakina..Ina nace Tsayayye wanda ko Bayan Raina zai iya Rike ki Da kedasu gabadaya.."Daga haka bai kara cewa komai ya Taka ya Shige Ciki kamar zai tashi sama.
Diza kuwa kunya Nadama Da komai sun Rufeta ganin marin ma gabam Rumana uwa uba ga Mansur wanda bata Ta aganinsa haka ba Yasa takwashi kuka zuwa Dakinta Key din Motarta ta Dauko da Mayafi ta bar su Rumaman nan Tsaye afalonta ta Fice koda suka Fito Tuni ta tsshi Mota Tayi Ribas tayo Hon megadi ya Bude mata ta Fice Rumana suka Kalli juna ba wanda yayi mgana Rumana tawuce Shashenta Jikinta yayi sanyi ita kuma Mardiya ta koma Cikin Falon Diza Tana jin Kamar kafafunta Bazasu iya Daukamta ba.
Tana shiga Mamsur na Fitowa Tana neman kwaso Rantsuwa ya Dakatar da ita da Fadin'"Basai kim ce komai ba..Naji komai..Gwara Datafi Gida Ta Fada ma su Mommy abunda ta aikata da kanta Domin ni kaina ina jim kunyar Fada kamar diza ta Fara Shaye Shaye.."
Yafada Lokaci Daya yana Ficewa bayan yasauya kayan jikinsa tana ji Shima ya Fice Daga gidan ta koma ta zauma kan kujera Tana Fadin"Allah ya kyauta..."

*Shakira...*
1/1/22, 18:55 - Maryam Badmsi: *SS....29*

*Ki biya ki karanta cikin Salama 09069067488 Mace mai aji mallakan komai nata takeyi bata jiran abun sata*

"Diza Tana Fita Gida ta wuce Tana kuka sosai,Mommy Hankalinta ya tashi gsshi kuma Tayi Tambayan Duniyanan Diza taki mgana sai dai kuka Ranta ya baci ta fita Batunta,ta kama Harkan Gabanta.
Chapter 63 · 0% Book details