← Book details Sadaukarwa So Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 84 OF 94

Sashe 84

Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 7 min read

Sai da Motarsu ta Fice daga Haraban gidan kana suka koma Cikin gida suna Shiga Falon Mastur ya kama Rumana da Mansur Tare ajikinsa Kamkam Lokaci Daya yana sakin Numfashi Cikin wata murya yace"Kada Allah ya kamani da Laifin kuntata miki Rumana..Allah ya bani ikon kwatanta miki Dimbin Alherinki gareni..Nagode..!
Yake fada sai ga Hawaye Itama Kukan take ammh Jinsa yana kuka yasa ta Dago Tana Share masa Hawaye tana Fadin"Soyayyar da nike maka ta gaskiya ce..Shiyasa nake Zaban Farincikin ka saman nawa akoda yaushe..!
Kara riketa kawai yayi ya kasa mgana har na tsawon wani Lokaci,kafin ta Zare Jikinta Tana Fadin"Muje ka Shirya Lokaci ya kusa..!
Daganan bedroom suka Nufa,duk yadda taso ta Zille bai barta ba sai da yaja Ra"ayinta suka Mori junansu Aranar Rumana Tayi kuka sosai
Soyayyar da Mastur ya nuna mata bata Dauketa anata ba,ta Dauketa a Saboda samun Diza ne ya Raba Farincikinsa da ita ayau shiyasa tana wanka Tana kukan,kukan tsausayin kanta da kishin Diza.
Ammh haka ta Daureshi ta Tayashi Shiryawa cikin Sabbin Kaya Shadda Fara Tazarce Dinkin Zamani,Da Hula zanna Bukar sai Agoginsa baki na Fata,da Rufaffan Takalminsa na Fatar Damisa baki,Ita ta Feshe shi da Turaransa na azzro Visit.
Tana kokarin maida kwallarta Ta shirya Mansur karami Cikin Kananan kaya masu kyau wanda ta Siyamai da kudinta,itama taci Wani Rantattsen Leshi Riga da Zani Tayi kyau duk da batayi kwalliya ba.
Duk kokarin Mastur Daya Fahinci Halin da Rumana take ciki bata bashi Dama ba Har suka bar gidan zuwa Hanwa.
Koda sukaje sunga abun mamaki Yan maruka har sun iso su Sakina da Mariya da Inna Zainaba da Baba Sule da yayyinsa guda Biyu ashe Daddy ya kirasu ya gaya musu Mutane anguwa ma duk sun Taru saboda Baba Habibu ya kira Kawu Usman ya gayamai shi kuma ya dunga gayama Mutane.
Gidan Mommy ma Makota duk sun Shigo Mommy ta kira kawar Diza Meena ita ta Taimaka mata tayi wanka ta kira Hauwa tazo Tayi mata Simple makeup,Diza gani take kamar karya ne,yau ita Zata zama matar Mastur Rumana sai da ta shiga ta gaida yan maruka kana ta kariso gidan Mommy kowa ya ganta sai sska mata albarka yake yi,Ta saki Jikinta Ita ke ma kara Lallashin Diza Ta Fuskarta bata nuna wani Hali take ciki ba.
1:30pm na Ranar Laraba aka Daura auran Mastur da Diza kan Sadaki Dubu Hamsin Daddy ya zama Waliyin ango Baba Habibu ya zama waliyin Diza abun mamaki hatta da Sagir ya Hallaci Daurin auran kuma ya mikama Mastur hannu sukayi musabaha ya tashi murna yana Fadin"Daddy ya kirani yana bani Hakuri..Yana gayamin kai ne..Nace na janye zaka fini Xama wani Jigo ga Hadiza Allah baku zaman lafiya..!
Ya amsa mai da Ameen Daganan Cikim gida kuwa Rumana tana jin an Daura aure ta shige Tiolet din Diza Tana Boye kukanta itama Dizan sai ga hawayen Farinciki suna kwaranyomata,
Kiran Umma ne ya Sa ta Fito Daga Tiolet bayan ta wanko fuskarta ta Daga kiran Umma Nasiha tayi mata tare da alfahari da ita sun Dade suna mgana kafin suyi sallama tace zata zo In Dizan zata tare nan da Sati Daya Inji Daddy daya kira Abba ya Fadamai komai Rumana sai taji ta cire komai aranta Tana da yakinin Abunda Tayi shine Daidai.
Wayarta ta Duba taga sakon Mastur

*Tanque..Thanks so Much Mrs Dcp Mastur Habib Dogowa..Zuciyata tana Girmama Karaminciki..Allah yayi miki albarka Rumanata..*

Sakon ya sakata Dariya da kuka Lokaci Daya acikin Ranta ta Furta.."Naji Dadi..Ko bakomai nasami Albarkacin Diza..!

*Shakira..*
1/1/22, 18:55 - Maryam Badmsi: *SS....38*

*Kibiya ki karanta Cikin Salama da Aminci Mace mai aji bata jiran Abun sata mallakan komai nata take yi,09069067488*

"Rumana Tayi kokarin Danne Abunda take ji yana kokarin Taso mata acikin zuciyarta,Ta nuna komai ba komai ba ta Fito aka Cigaba da Hidima da ita ta Rumgume Diza Tana Share mata Hawaye Kowa awajen Sha"awan Rumana yake yana saka mata albarka.

Ba laifi anyi Sha"ani Sosai duk da ba Ranar Diza zata tare ba ammh yan"uwan da suka zo an taru an Taya Diza da Mastur Murna Mommy da Hajja duk sun gayyaci Makota saboda Daddy yace Biki Daya za"ayi daga wannan bazaka akara Taruwa ba Ko Mutum Dayane zata raka Diza Dakin Mijinta Sati Dayan ma Dayace Kafin ta taren Shi Mastur din ne ya roka saboda yana soyayi ma Dizan kaya ya kuma bata Lokaci Tayi nata Shirin sai kuma mganar inda Zata Zauna wanda Tunda ya kawo mganar Daddy yace Sashenta zata zauna inda Ta zauna da Mansur ba Bukatar wani abu kuma
Daddy ya riga ya yanke Hukunci bamai jadashi..Mastur ma bai ce komai ba Sanin baida wani Muhalli a Hannunsa ammh yana saka Ran nan gaba Zai mallaki gidansa Inda Zai Hada matansa waje Daya da yardan Allah.
Aranar anan ya bar Rumana ta kwana tunda tace ya barta ta kwana Duk da yaso su tafi gida ammh Ta Nuna ya kyaleta ta kwana sai ya barta ita kuma ta Gujemai ne saboda bata son Gangar Jikinta da Zuciyarta ta saba da wannan Sabon Mastur din Bata son ta Rika Raban Alfarman Soyayyar Diza Zuciyarta tana Raunana sosai.
Tare da Diza suka kwana,Mansur karami kuwa yana gidan Hajja wajen su Sakina Tunda suka zo yana Hannunsu.
Sai washegarin Rumana ta koma Gida ta Shirya Mastur ya kaita Wajen aiki ssi nan nan yake da ita ko Kuda baya so ya Tabata Mgana Daya Biyu sai yace Nagode Rumana Allah yayi miki albarka Sai dai Tayi Mirmishi kawai tace Ameen.
Bata san a ina Aisha bala ta samu Labari ba Tana zuwa tayi mata Zencen abun ya bata mamaki sai kuma batayi mamaki ba abun Duniya Baya Boyewa Data Tambayi Aishan a ina taji ba, sai tace mata a Social media Tagani Matar marigayi Honourble Mansur Sulaiman ta Sake Auran Dan"uwansa Dcp Mastur Habib Doguwa,Rumana batayi mamaki ba Tunda yanzu komai ya koma Social media.
Bata gama mamaki ba sai da Basma ta kirata Tana Fadin"Ruma me nake gani haka.
? Mastur mijinki ya auri Diza Matar marigayi..?
Rumana Tayi kokarin Danne Abunda ke Damunta tace"Ke kuma a ina kika ji Labari...?
Basma Tace"A shafin Diza na gani kinsan ina Following dinta a Intergram,yanzu naga posting dinta ta saka Alhamdulillah Finally Mrs Dcp Mastur Habib  Doguwa..!
Rumana ta Runtse ido Tana kokarin Daidaita kanta bata ji mamaki ba saboda Taji labarin Daman chan Diza Mastur taso ba Mansur ba kuma Ta karanta a Diary din Mastur Daman kukan Datakeyi ai ta sani na Farinciki ne bana Bakinciki ba ammh bakomai ita Tayi haka ne saboda Soyayyarta da Mastur in batayi haka ba kila Daga ita Har dizan Zasu iya rasa Mastur din.

Rumana tace"Da gaske ne..Jiya aka Daura auran Zata tare nan da kwana Shida ina Fata zadai ki zo ko Kawata..? Wani Dogon Tsaki Basma Taja Kafim tace"Allah ya kyauta..Ke kam kiyi ta wani abu kamar wata sakara..Yanzu kika yarda akayi miki kishiya ko Haihuwa baki Taba yi ba Rumana... ? Gaskiya hatta da iyayen Dizan basu kyauta ba da iyayensa da suka kasa Nuna mai hakan bai dace ba..!
Rumana na jin haka Tayi saurin Dakatar da Basma Tana Fadin"Eh naji ni Sakaryace..Saboda na bama Mijina Dama yayi abunda Allah ya Hallitamai..? Ba ruwansu Mommy a wannan mganar ballatana su Hajja Kuma kada ki manta Bayan Mastur banga wanda ya Chanchanta Ya auri Diza ba shine yafi Dacewa..Koda ace yau Mansur Zai Dawo Duniya zuciyarsa Zata fi samun Salama akan Diza ta auri wani na waje..!
Daga haka kawai Rumana ta Datse kiran Tana kokarin maida kwallarta Bata so Tayi kuka Saboda Aisha na wajen ita kanta sai kallon Rumanan take batadai yi mata mgana ba ammh ita,kanta taga Wautan Rumana da zata bama Namiji goyon bayan yayi mata Kishiya.
Har ta tashi bata bama Aisha Fuskan da Zatayi mata wata mgana ba Ko Mastur Dayace ta kirashi in sun tashi bata kirashi ba Motar Haya ta hau zuwa gida.
Koda ta koma Baya gidan acikin Ranta tasan yana Hanwa Wata Zuciya tace yana wajen Diza dai Rumana ta kasa Sarrfa kanta bata san sadda Ta fada kan gado Tana gunjin kuka ba Zuciyarta TaRaunana sai take jin Nadaman meyasa ma ta Fadi mganar Batayi Shuru da bakinta ba Tunda Shi yaki ya Furta..?Shedan nata saka mata Wasi wasi Ganin haka yasa ta Daga waya ta kira Umma ta saka mata kuka,Umma tasan Zafim Kishi ita kanta Datake uwar Rumana Har kawo yanzu ba"ayi mata Kishiya ba Tana matukar Tsausayama Rumana Sai bata nuna mata ba Ta Shiga Lallashinta da bata baki da Nasihu har tayi shuru Zuciyarta Tayi sanyi Tayi ma Umma alkawarin bazata kara Sakama kanta Damuwa ba.
Wayar da sukayi da Umma ita ta Taimaketa taji ta Wasai Tashi Tayi ta Shiga Kitchen Tayi Dinner kana tazo Tayi wanka ta Fito kenan Taji kiran Mastur Har ta katse sai tabi bayan kiran Tana Dagawa yace yana Asibitin Chika ta Fito su tafi yana ta kiranta Bata Daga ba sai kuma taji bata kyauta ba Cikin Sanyin murya tace Ta dawo Gida Tunda bata jin Dadi Dan jim yayi kafin ya kada kai ya yanke kiran duk sai taji ba Dadi.
Chapter 84 · 0% Book details