← Book details Sadaukarwa So Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 35 OF 94

Sashe 35

Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 8 min read

Duk yadda Mastur yaso Zillema Zuwa Zaria hakan bai samu ba Domin Bayan Kiran Daddy Baba Habibu ma ya kirashi yakaramai mgana bashi da Wata Mafita na Shiryawa ya Tafi Zaria Ranar Friday yabi Jirgi Zuwa kaduna Daga chan ya Kira wani Sargent Dake aiki nan Headquater yan sanda ta Jahar kaduna ya Daukeshi amotar Aikinsu Zuwa Zaria,wajen 9pm na Dare ya iso bai gayama kowa ba sai da suka gansa kwatsam Adaran Sargent din ya koma Kaduna.
Mansur da Hajja Haka suka Tasa Mastur gaba suna Tambayansa Wani irin Ciwo yayi ya Rame haka..? Yayu baki kamae wanda yaShekara yana wata Cuta Aiya ma ta kasa mgana Baba Habibu ma bai ce komai ba ammh Shi kanshi yasan Dan nashi ya Rame duk ya Lalace sai kashin Wuya da kwarmin Idanuwa ammh Dai bai yi mgama ba Mastur kuma Sai yace yanayin aiki ne ammh Lafiyarsa kalau ko da Gigi bai Fada musu ya kamu da Hawan Jini Saboda baya son a Mtsamai sai an ji Dalilin kamuwarsa da Ciwon yana Matashinsa mai kananan Shekaru.

Sai da asuba suka Hadu da Daddy a masallaci Shi kansa sai da yayi mganar Ramar Mastur yace Gaskiya zai bincika in za"a iya mai Trasfer ya bar kudu ya Dawo arewa ammh Mastur yace A"a domin abaya ne yake son Zama kusa da gida banda yanzu da komai ya Riga ya Lalace Daddy yayi mgana da Baba Habibu kan zuwa anjuma zasu Hadu dukkansu nan Falon gidansa su Tattaauna da Haka suka Rabu Shi kanshi Mansur bai ji Dadin Ganin yayan nashi haka ba Duk da ya san sa Miskili ne ammh wannan karon Miskilancin nashi ya karu Sosai Sai ya Shige Daki baya Fitowa Ko Falon Hajja Daya kan Zauna wannan karon ko Sau Daya bai Zauna ba suna gaisawa yake Mikewa ya koma Shashensu Mansur kuma Baya samun Zama Saboda Zabe ya kusa suna ta Shirye Shirye in ya Dawo kuma da Daddare Domin su zanta Daya Fara mgana sai Mastur din ya Fara Hamman karya kamar yana jin barcin in yaga haka sai ya kyaleshi yana mai Uzuri saninsa agogo ne Sarkin aiki Shi kuwa Mastur gujema mganar Diza yake bayason Ya bar wata alama da Za"a Fahimci wani abu.

Aranar Diza bata nan Tana kaduna sun je wani Training ne na Koyon Wasu Snack din kayan Fulawa Wajen Kwana uku anayi kullum sai taje kaduna ta Dawo Ranar ne na Karshe sai Gabda mangariba ta iso Gida ita bata ma san Mastur yazo ba Mansur ne ke gayamata kuma suna Dan Jumawa basu Hadu ba Zabe ya kusa kansa yayi Zafi baya zama agida,Watarana ma Baya kwana agida yakan kwana agidansa Dake GRA wanda ya mallakeshi Lokacin Daya Zama kansila Sai da sukayi mgana ta waya sama sama Shima din Ba Lokaci basu yi mgana ba kwana Biyunan sai Bayan tayi wanka Tayi Sallar mangariba ta Fito Falo ta Haura Saman Wajen Mommy Tayi mata Sannu da gida anan ne Mommy ke Fadamata akwai Zama Yau da Daddare inji Daddynta.."

Diza ta kada kai Cikin mamaki Tana Fadin"Mommy wani irin Zama kuma..?kuma dawa dawa..? Mommy tace"Kanmganar ku ne keda Mansur..Sai Mastur..Zama Kuma da Duka Iyayanki mana.."Diza Taji mamakin abunda Mommy Tace Cikin Dubanta Saka saka tace"Mganata ni da Mansur kuma Mommy..? Wata mgana..?
Mommy Data ga Kamar Diza na Raina mata wayau ta Harareta Lokaci Daya ta Mike Tana Fadin"Bansani ba..Kinga In kin Sauka kasa ki Fada Fadime ta Shirya komai da wuri Alhaji ya kusa Karisowa.."Tafada Lokaci Daya tana Shiga Cikin Bedroom Dinta.

Galala Diza ta Bita da kallon Bata gane inda ta Dosa ganin ba wanda zai gayamata yasa ta Zakuda Kafada ta Fice Zuwa Falon kasa,Tana Latsa wayarta,Kitchen ta Shiga suka Gaisa da Mama Fadime ta gayamata sakon Mommy kana ta Fice Zuwa Dakinta Duk yadda Taso ta manta da mganar ta kasa Lokaci Bayam Lokaci abun na Fado mata sai da Merry ta Kiratanr suka Fara lissafinsu Kana Ta saki mganar suna gama wayar kuma ana Kiran Sallar Sai ta tashi Daman Tana da alwalanta ta tada Sallar Tana Idarwa Ta zauna nan kan Darduma Tana Addu"a Lokaci Daya kuma Tana Tunanin wani irin Zamane Mommy Take nufin Za"ayi a kansu..?Rashin samun amsa yasa ta Jawo wayarta Ta Kira Mansur ammh bai Daga ba sai ta kyaleshi gefen gadon ta Zauna ta Rafka Tagumi haka kurum Take ji Jikinta Duk ba Dadi da Faduwar gaba.

Tana nan Zaune Tayi Nisa a Tunaninta Taji mganar Daddynta ya Dawo chan kuma Taji Muryan Hajja suna gaisawa da Mommy Taji kuma mganar Aiya Data Mansur bata dai Taji ta Mastur din ba Bata Dauka ma ya Dawo ba,Zuruf ta Mike Jikinta na Rawa Daidai Lokacin da Wayarta Ta shiga kara Tana Dubawa Taga Mansur ne Gabanta sai ya Fadi ta kasa Daga Kiran Har ta katse Haka kurum Tunda Taji mganar Mommy Gabanta ke Fadi Ta na nan Tsaye Taji Shigowar Mommy Dakin Tana Fadin"Diza ki Fito Falo..Ana mgana.."

Zuru Diza Tayi mata da idi Ita kuma Mommy bata gane ba ta Dauka irin kunyar nan ne na Mata Mirmishi kawai Tayi Ta Fice Tana Fadin"Ja"irai Daga ke Har Mansur din.."Diza bata jita ba ita daj jikinta ne yayi sanyi Da Hijabin Sallar Dake Jikinta TaTaka ahankali ta Fita Zuwa Falon Tana jan kafa sai dai Tasha mamakin ganin Mastur Zaune Gefen Mansur,Sai Baba Habibu kan kujera kusa da Daddy sai Mommy agefe Chan Nesa Ita da Hajja Wacce ta saka Hijabi Sabanin Mommy Data saka Mayafi Aiya kuwa na Kujeran mai kallon su Daddy.
Kafafunta Taji sun fara rawa Tunda ta Fito Falon Mansur ya kafeta da ido yana Mirmishi Mastur kuwa da gabansa ke Faduwa bai iya Dago kansa ba Hailala kawai acikin Ransa Allah ya Rufamai asiri kada yayi acting din da za"a gane He is Love with Diza Shiyasa bai ji ma Sha"awar kallomta.

Aiya ce ta kirata tace tazo ta Zauna kusa da ita shi ya bata kwarin gwiwan karisawa ta Zauna Wajen kafafunta Lokaci Daya Tana gaida Baba Habibu da Hajja Mansur Dake kallonta ta Kallah sai taga yau yana mata wani irin kallo Mastur kuma bazata ce komai akansa Ba Domin kansa yana kasa ne ko Motsi ya kasa.

Daddy ne ya Bude Taron da addu"a kafin ya Kora da Jawabin Abunda ya Tarasu ya Karishe da Fadin"Kai Mastur kai ne Babba Ta kan ka Zan Fara Yaya muke ciki..? Ka samo Yarinyar da zaka aura..?
Dam gabansa ya Fadi Lokaci Daya Dana Diza Data Dago Tana kallonsa Lokaci Daya Tana Zare ido,Mastur kuwa kansa na kasa yakasa Dagowa Dakyar ya iya Muskutawa ganin Kowa Shi yake jira yace"A"a Daddy..Ban samu ba.."Daddy yace"Kaji Aikin ko Habibu..? Baba Habibu yace"Mastur ai Halinsa kenan komai Sai yace bai Duba ba..Bansan yaushe zai saki Jiki da Mutane haka ba.."

Yafada yana kallonsa Mastur kuwa kai ya kara Saddawa gabansa na Faduwa,Kai Daddy ya Jinjina yana Fadin"Bakomai Tunda kai baka Duba ba..Ni zana Duba maka na samo maka wacce ta Dace Dakai.."Mastur dai bai ce komai ba Aiya ce Tace"Da hakan ma akayi..Domin Dagani ai megidana baya kula kowa.."Diza kuwa ji Tayi kamar Ta Suma Saboda Zafin kishi Dana Zuciya Mastur din nata ne ake mganar an zabamai mata bata Dawo Cikin Hayyacinta ba Taji Daddy na cewa"Duk da Mansur ya Turo Yayansa Mastur ya gayamin Zabinsa.Ban yi Musu ba sai dai gashi gamu ya Sake maimaita abunda yace ma Dan"uwan nashi.."Sai kallo ya koma kan Mansur ita Diza ma Lokacin Ta Daina Fahimtar komai So take ta Mike tayi mgana ammuh kuma Jijiyon jikinta sun saki.
Mansur ya Zunguri Mastur Dake zaune kamar mutum Mutum Tunda ya sadda kai Kala bai ce ba Kansa na kasa yana Fama da Zuciyarsa wajen Raunin Datake so ta bayyana.

Cikin Rada Mansur ya Sunkuyo yana Fadin"Ya Mastur ka Fada musu.."Mastur ya kalleshi da Lumsassun Idanuwansa masu cike da Damuwa yace"Ka gaya musu da kanka..!.
Daddy ne yayi gyaran murya yana Fadin"Mansur kayi mgana mana..?duk da Sunsan mganar suna Bukatar kara jinta Daga bakinsa.
Kansa ya maida kasa Bayyan ya kalli Diza ita kuwa So take taji wayake so Wacce bata Taba saninta ba Alhalin basa Boye ma juna komai kamar a mafarki taji yace"Baba Daddy..Ni ba wacce na Dade ina son acikin Raina sai DIZA ita nake son Aura ta zama Matata.!
.
Diza Dataji mganar kamar saukan aradu akanta Ta Zabura Ta mike Dafe da kirji bayan Tayi Cilli da wayarta Mommy kuwa da Hajja da Su Daddy Sai Washe baki suke Mastur dake duke bai Dago ba yana kokarin Sarrafa kansa yaji muryan Diza da karfi Tana Fadin.

"A"a..Kada muyi haka Dakai Mansur..Wata Dizan ni..? A"a ni ba Soyayyah muke ba..A Dan"uwa Amini na Daukeka Mansur kar ka Hanani mallakan mafarkina..Tun Bayan Dana Mallaki Hankalin kaina Na Fahimci ba wanda nake so Sai YAYA MASTUR...!

_Topha yaya wannan Badakalan zata kare..? Ga dai Diza ta Fassala Sirrin zuciyarta Bayan kuma Mansur shima ya Fallasa nashi..? Shin kuna ganin Mastur zai yi amfani da wannan Damar ya Saba alkawarin Da yayi ma kansa na Binne soyayyar Diza a ransa ki zai bayyana..? Wace ce wacce Daddy yake so ya zaba ma Mastur..? Waye zai yi Sadaukarwar so kuma waye zai ci Riban Hakan..? duk wannan Tarin Tambayoyin suna Cigaban wannan Labarin Kamar yadda na Fada muku Daga wannan Shafin ne karshen Free page mai Bukatar jin ya zata kaya Zai iya Bin wannan Tsarin Domin mallakan nashi.._

_Albishirunku Masoyana wannan karan na bude muku wani Shashi na musamman Saboda ku..Ina masu Bukatan Atalla musu Hajarsu Ko wani iri ne Domin samun costumer ta ko"ina..? Ku garzayo kakarku ta kusa yanke saka Zan Tallata muku Hajarku a Duka Shafukana Domin inganta Sana"arku da kuma Samun Cinikaya mai Tsabta da kuma kara Hada hada wajen Masi siye da Siyarwa mai Bukatar A tallata mata Hajjarta Zata iya min mgana kai Tsaye ta wannan Lambar Tawa 09069067488 domin karin Bayani...Sai kunzo Kunsan dai mai kasuwa Shi ke da Riba.._
Chapter 35 · 0% Book details