Sashe 70
Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tsuru kawai Tayi ta kura ma Kofar Shigowa ido haka kurun tun Safe yau take jinta Cikin yanayi mara Dadi ta rasa gano Dalilin Haka Taji mganar Aisha a Sama Tana Fadin"Nifa yau naga Asibitin nan ta Cika da Mutane..Anya Lafiya..?
Rumana ta Dago Tana kallonta tace"Kinsan ai ita wannan asibitin kullim Cikin Jama"a take bata Rabo da mutane..!
Aisha bata kara mgana ta Mike Dauke da wayarta ta Fice Rumana ta Bita da kallo Tana Fita Batayi Nisa ba sai gashi ta Dawo ta iske Rumana Dauke da Jakarta Tana kokarin Fito da wayarta Cikin kulawa tace"Nifa nace..Yanzu na gamu da Dr.Yahaya shi yake Fadamin wani Dan Siyasa ne suka samu Hatsari a hanyar kaduna aka kawoshi nan asibitin kamar ma ya Rasu yace gawarsa ne ake kokarin Tafiya da ita..!
Sanda Aisha ta Fadi haka sai da gaban Rumana ya Fadi da Sauri taDago Tana kallonta Dauke da waya a Hannunta Cikin karfin gwiwa tace"Allah Sarki..Allah ya jikan Musulmi.."Ganin yadda Tayi ne yasa Aishan Tace mata"Ruma Meke damun ki..?
Ruma Data koma ta Zauna Tana Fadin"Meke kika gani Aisha Bala..?
Aisha tace"Na ganki so Cool..Kinyi wani Sukuku dake kamar ba Dr.Rumanan Dana sani ba mai Kazar kazar da Kuzari sosai..!
Wani Mirmishin Fatan baki Rumana ta saki kafin tace"Ni kaina haka na Tsinci kaina..Bansan meke Damuna ba..!ta fada kamar Zatayi kuka Aisha na Shirin mgana wayarta tayi kara sai ta Fice Domin ansa wayar Fitarta yasa Rumana ta maida Hankalinta kan wayarta Tana Dubawa sai abun ya bata mamaki ba Bata ga kiran Mastur ba Alhalin sunyi waya jiya da Daddare yace mata da Safe zai kirata ganin haka yasa ta Kirashi ammh wayarsa Tana kashe sai taji Zuciyarta ta tsinke Sanin Bashi da Dabi"an kashe waya duk Tsiya zaka Sameshi sai dai in bazai Daga bane.
Tana cikin kara kiran Wayar nashi ne Aisha ta Shigo a Razane Cikin Haki Kamar Zata Shide wanda ya Firgita Rumana ta Mike Cikin kaduwa Tana Fadin"Aisha Bala lafiya..?
Aisha ta karisa ga Rumana ta Riko Hannunta Tana Fadin"Taho Ruma inaga wannan kanin Mijin nakin ne ya rasu..Yanzu nabi ta Wajen Emergency naga Baban Mijinki Daya Taba kwanciya anan asibitin da kuma Matar gidan nan naku suna ta kuk.."
Ai Rumana bata gama jin mganar Aisha ba Ta Fincike Hannunta Daga na Aisha Wayarta Dake hannunta Ta Subuce Allah yasa Aishan Tayi Saurin Tare wayar Rumana ta Fita Tana Haki da gudu Tana Salati Lokaci Daya tana Fadin"Lahaula walakuwatu Illah Billahi..!
Haka take ta Fada tana Kuka Lokaci Daya kowa ya ganta yasan Bata Cikin Natsuwarta Rumana ganin Sauri bazai mata ba yasa ta Fara Hadawa da gudu Cikin Lokaci sai gashi ta iso Emergency din Daidai Lokacin da aka Fito da gawan Mansur Zanin da aka Rufeahi Dashi Zanin Hajja ne wanda tayi mayafi dashi ta bada Har ya Jike saboda Jini,Nurses ne maza suka Daukosa akan gadon da aka Daukan Matattu dashi.
Mommy na gefe Tana kuka Diza na Jikinta tana Zubar kwallah masu Zafi Hajja ma na gefe Tana kuka ita da Aiya Baba Habibu ne da Daddy sai Kawu Usman ke Biye da gawan zuwa Wajen Motar Ambulance din da asibitin ta bada zasu Kaishi gida,Sauran Tawagan Marigayi mansur suka Rufa musu baya Cikin wani yanayi.
Rumana Dataji tamkar gangar Jikinta bazai Dauketa ba ta kasa ma karisawa ga su Hajja,Tana Tsaye kamar an Dasata Tana jin kamar kanta na Juyawa da ita Bayanta Aisha ce data Biyo bayanta da Jakarta da wayarta Cikin wani yanayi Baba Habibu ne ya Dawo bayan an gama Saka Mansur a mota yazo yace su Hajja su Fito su tafi gida yaci karo da Rumana Cikin yanayin kuka na Fitar Hayyaci.
Ganinsa Yasa Rumana ta samu kwarin gwiwan yin mgana Cikin Muryan Kuka da Sarewa tace"Ba.Ba..Me samu Mansur..?
Baba Habibu Daya ke nuna Dakiya da Jarumta yace"Rumana ashe kina cikin asibitin..? Rudanin da muke ciki ya mantarmu Dake..Sai Hakuri Allah ya Dauki Ran Mansur..!
Da wani irin karfi Rumana ta Dora Hannu aka ta saki wani Razanannen Kuka Lokaci Daya Tana Zubewa akasa Domin kafafunta sun gaza Daukanta.
Baba Habibu Dayake jin shima kamar ya saka kukan yace cikin Lallashi"Ash..Tashi Rumana..Tashi..Mansur ba kukan ku yake Bukata ba addu"a kadai ce Zamu yi mai mu nunamai Soyayyarmu.."Yake fada cikin Dauriya kafin ya karisa wajen su Mommy yana Fadin"Hajiya kuyi hakuri ku Fito muje..ni zan bi Motar gawan Ku kuma Alhaji ya kiran Drebansa yana waje yana jiranku zai Tuka ku shi Alhaji Zai Taho atashi Motar,Usman kuma zai Taho da Babur dina sauran jama"a kuma zasu bi bayanmu da Motocinsu.."Fadin haka Da yayi yasa kukan Hajja ya karu Kallonta kawai yayi yana Fadin"Hajara Ba kuka Mansur ke Bukata ba yanzu..Ahalin Dayake Ciki addu"anmu itace Soyayyarmu garesa Don Allah ku Daina mai kuka Allah ne fa ya bamu Shi kuma shi ya Dauke abun Shi Domin yafi mu sonshi..Hu hanzarta ku Fito mu Tafi..Saboda asallaceshi da wuri a kaishi Gidansa na gaskiya.."Yana mgana ya Kama Hajja Data kusa Fadi ya kuma Riko Hannun Aiya Mommy ta Tallafo Diza Dake Zubar kwallah ta Zama kamar Mutum mutum kawai Rumana Data ga Ta yunkura ta mike Aisha ta Taimaka mata Suka Rufa musu Baya Cikin Alhini da Rauni.
Kamar yadda aka Tsara hakan ce ta Faru Baba Habibu Shi ya Bi Motar Gawan Su kuma Matan Direban Daddy ya Tukasu Rumana kuma Aisha ta karbi Key din ta tukasu Sauran Jama"ar Mansur suka Rufa musu Baya Irin su Sagir Cikin Tashin Hankali.
Zuwa Lokacin da suka isa anguwan Tuni Rasuwan ta isa kunnen Mutane Tunda Gidajen Radio sun Watsa Labarin,Daddy kuma Tun yana asibitin sukayi mgana da Baba Habibu kan Lokacin Jana"iza karfe 4:00pm na yammah Tunda Hatsarin ya Faru ne wajen karfe 9:30am na Safe da kawo su asibiti da karban gawan da komai 11am na Safe ma ya wuce suka Dawo saboda Sauran Mutane da kuma Uwa Uba Mastur Da ake ta kira akashe Za"a Jingirta Domin yazo ya Sallaci gawan Dan"uwansa kafin kace kwabo anguwa ta Cika da al"umma kama Daga Abokan Siyasan Mansur matasa yan makaratansu Yan maruka ma sun iso Cikin Raunin Zukata Sai aka Hade Falon Hajja ana ta kuka Kamar me,Ba iya Cikin Gida ba Har waje magidanta kuka suke na Rashin Mansur haka Matasa,Inna karime ma ta iso Ita da Mijinta Tana kuka,Sai ga Maryama itama ita da mijinta da Kishiyarta ajaran majaran Ita bata ma ji Ba Mijin nata ne yaga Labarin na yawo A social media yazo ya gayamata Tunda yasan Yayanta ne, Shine fa Hankula suka Tashi Ajaran majaran suka Taho.
Tana Shigowa sai kuka kuma ya Karu Gawan Mansur Tana Uwar Dakin Hajja ne,chan aka kaisa Hajja na gefe sanye da Hijabi da Carbi Tana ja kuka ya Dauke mata Mommy na gefenta itama Cikin Hijabi da Qur"ani a Hannunta Tana karatu sai Daga Chan Gefen Diza ce Zaune tana Jingine da Bango Tana Sanye da katon Hijabin Hajja sai Carbi Dake hannunta ta kura ma gawan Mansur ido Dake Lullube da Zani tana Zubar kwallah Shaa!!! Kamar famfo Gefenta kuma Rumana ce itama Cikin Hijabi Itama kuksn take sai Kawarta Aisha itama sai Sharan kwallah take sai mardiya,Sakina dasu Mariya suna Falon Hajja suna ta kuka dasu Balaraba da Sauran matan Baffanin Baba Sule,da sauran Makota da suka Shigo,Ana cikin hakane sai ga Umma ta iso ita da Anty Saratu itama Tana shiga taga gawan Mansur sai ta Fadi Tana Kuka Hawaye na Zubar mata take Fadin"Allahu akbar..Allah jikan ka Mansur Allah ya maka Rahma..Allah ya sadaka da Mala"ikun Rahma..Allah Sarki Rayuwa kenan..'Take Fada Tana kuka Anty Saratu na Riketa itama Tana Sharan kwallah Dagata tayi suka koma Gefen Hajja suka Zauna Cikin kuka take Fadin"Hajja ya muka ji da Hakurin wannan Babbar Rashin..?
Hajja ta Bude baki Cikin Shakkiyar Muryan Dataji kuka tace"Hakuri..Namu ne Duka Hajiya sannunku da zuwa. mansur ya tafi ya barmu..Shima yazo ya tafi kamar yadda Mahaifiyarsa Maryama Tatafi ta barmu.."
Umma na kuka take Fadin"Allah ya musu Rahma..Allah ya sadashi da mala"ikun Rahma..An gayama Shi Dan"uwan nashi..? Har muka iso Abban Ruma nata kiransa Wayarsa Tana kashe..!
Wannan karon Mommy ce Tayi mgana cikin Zubar kwallah Tace"Duka an kira wayoyinsa a kashe..Ba'a samesa ba..Su Alhaji sunce baza"a jira sa ba..Gwara ayi a Sallacesa Zuwa Gidansa na gaskiya..Tun dazu ma da suka Shogi nan har sun kira Chan dambom makabarta an Fara Hakan kabari nan kuma Usman Mijin balaraba ya tafi Hado likafani da kayan wanka..!
Tana Fade tana Sharan kwallah Umma ta gyada kai tana Fadin"Allahu akbar..Rai bakon Duniya.!.
Rumana ta mike tsam ta Fice Daga Dakin Bata kuka sai dai idanuwanta sun yi Jajir Saboda kuka kitchen ta Shiga ta Zaro wayarta Cikin Haban Sikat din ta Kara Nenan Layin Mastur bata shiga Kawai sai ta yanke Shawaran Turamai sako.
*Ya Mastur kana ina ne..? Ko a ina kake kazo gida ba lafiya..*
Daga haka ta Turamai kana ta Fito Daga kitchen Dakin Aiya ta Shiga Aiya tana Falo kamar ma ta Rude sai mganganu take,Dake da Tiolet ta Shiga ta Dauro alwala tazo ta Dauki Aqur"ani Ta koma Dakin ta koma inda tatashi Ta Bude Qur"ani ta Fara karatu Cikin Sanyi da Rauni Duk Sai Dakin ya Dau Shuru kowa yana ji Bugawar Zuciya da Rauni mai Tsanani.
*****
Shigowarsa Office dinsa kenan yau tun safe bai zauna ba wani Operation suka Tafi kuma Abun Farincikin Operation din is Sessufull,Sai da ya zauna kan kujeransa ya Tuna daya kashe wayoyinsa tun Safe bai ma Tafi dasu ba nan Cikin Office din ya watsar dasu Tun Shigowarsa da Safe.
Rumana ta Dago Tana kallonta tace"Kinsan ai ita wannan asibitin kullim Cikin Jama"a take bata Rabo da mutane..!
Aisha bata kara mgana ta Mike Dauke da wayarta ta Fice Rumana ta Bita da kallo Tana Fita Batayi Nisa ba sai gashi ta Dawo ta iske Rumana Dauke da Jakarta Tana kokarin Fito da wayarta Cikin kulawa tace"Nifa nace..Yanzu na gamu da Dr.Yahaya shi yake Fadamin wani Dan Siyasa ne suka samu Hatsari a hanyar kaduna aka kawoshi nan asibitin kamar ma ya Rasu yace gawarsa ne ake kokarin Tafiya da ita..!
Sanda Aisha ta Fadi haka sai da gaban Rumana ya Fadi da Sauri taDago Tana kallonta Dauke da waya a Hannunta Cikin karfin gwiwa tace"Allah Sarki..Allah ya jikan Musulmi.."Ganin yadda Tayi ne yasa Aishan Tace mata"Ruma Meke damun ki..?
Ruma Data koma ta Zauna Tana Fadin"Meke kika gani Aisha Bala..?
Aisha tace"Na ganki so Cool..Kinyi wani Sukuku dake kamar ba Dr.Rumanan Dana sani ba mai Kazar kazar da Kuzari sosai..!
Wani Mirmishin Fatan baki Rumana ta saki kafin tace"Ni kaina haka na Tsinci kaina..Bansan meke Damuna ba..!ta fada kamar Zatayi kuka Aisha na Shirin mgana wayarta tayi kara sai ta Fice Domin ansa wayar Fitarta yasa Rumana ta maida Hankalinta kan wayarta Tana Dubawa sai abun ya bata mamaki ba Bata ga kiran Mastur ba Alhalin sunyi waya jiya da Daddare yace mata da Safe zai kirata ganin haka yasa ta Kirashi ammh wayarsa Tana kashe sai taji Zuciyarta ta tsinke Sanin Bashi da Dabi"an kashe waya duk Tsiya zaka Sameshi sai dai in bazai Daga bane.
Tana cikin kara kiran Wayar nashi ne Aisha ta Shigo a Razane Cikin Haki Kamar Zata Shide wanda ya Firgita Rumana ta Mike Cikin kaduwa Tana Fadin"Aisha Bala lafiya..?
Aisha ta karisa ga Rumana ta Riko Hannunta Tana Fadin"Taho Ruma inaga wannan kanin Mijin nakin ne ya rasu..Yanzu nabi ta Wajen Emergency naga Baban Mijinki Daya Taba kwanciya anan asibitin da kuma Matar gidan nan naku suna ta kuk.."
Ai Rumana bata gama jin mganar Aisha ba Ta Fincike Hannunta Daga na Aisha Wayarta Dake hannunta Ta Subuce Allah yasa Aishan Tayi Saurin Tare wayar Rumana ta Fita Tana Haki da gudu Tana Salati Lokaci Daya tana Fadin"Lahaula walakuwatu Illah Billahi..!
Haka take ta Fada tana Kuka Lokaci Daya kowa ya ganta yasan Bata Cikin Natsuwarta Rumana ganin Sauri bazai mata ba yasa ta Fara Hadawa da gudu Cikin Lokaci sai gashi ta iso Emergency din Daidai Lokacin da aka Fito da gawan Mansur Zanin da aka Rufeahi Dashi Zanin Hajja ne wanda tayi mayafi dashi ta bada Har ya Jike saboda Jini,Nurses ne maza suka Daukosa akan gadon da aka Daukan Matattu dashi.
Mommy na gefe Tana kuka Diza na Jikinta tana Zubar kwallah masu Zafi Hajja ma na gefe Tana kuka ita da Aiya Baba Habibu ne da Daddy sai Kawu Usman ke Biye da gawan zuwa Wajen Motar Ambulance din da asibitin ta bada zasu Kaishi gida,Sauran Tawagan Marigayi mansur suka Rufa musu baya Cikin wani yanayi.
Rumana Dataji tamkar gangar Jikinta bazai Dauketa ba ta kasa ma karisawa ga su Hajja,Tana Tsaye kamar an Dasata Tana jin kamar kanta na Juyawa da ita Bayanta Aisha ce data Biyo bayanta da Jakarta da wayarta Cikin wani yanayi Baba Habibu ne ya Dawo bayan an gama Saka Mansur a mota yazo yace su Hajja su Fito su tafi gida yaci karo da Rumana Cikin yanayin kuka na Fitar Hayyaci.
Ganinsa Yasa Rumana ta samu kwarin gwiwan yin mgana Cikin Muryan Kuka da Sarewa tace"Ba.Ba..Me samu Mansur..?
Baba Habibu Daya ke nuna Dakiya da Jarumta yace"Rumana ashe kina cikin asibitin..? Rudanin da muke ciki ya mantarmu Dake..Sai Hakuri Allah ya Dauki Ran Mansur..!
Da wani irin karfi Rumana ta Dora Hannu aka ta saki wani Razanannen Kuka Lokaci Daya Tana Zubewa akasa Domin kafafunta sun gaza Daukanta.
Baba Habibu Dayake jin shima kamar ya saka kukan yace cikin Lallashi"Ash..Tashi Rumana..Tashi..Mansur ba kukan ku yake Bukata ba addu"a kadai ce Zamu yi mai mu nunamai Soyayyarmu.."Yake fada cikin Dauriya kafin ya karisa wajen su Mommy yana Fadin"Hajiya kuyi hakuri ku Fito muje..ni zan bi Motar gawan Ku kuma Alhaji ya kiran Drebansa yana waje yana jiranku zai Tuka ku shi Alhaji Zai Taho atashi Motar,Usman kuma zai Taho da Babur dina sauran jama"a kuma zasu bi bayanmu da Motocinsu.."Fadin haka Da yayi yasa kukan Hajja ya karu Kallonta kawai yayi yana Fadin"Hajara Ba kuka Mansur ke Bukata ba yanzu..Ahalin Dayake Ciki addu"anmu itace Soyayyarmu garesa Don Allah ku Daina mai kuka Allah ne fa ya bamu Shi kuma shi ya Dauke abun Shi Domin yafi mu sonshi..Hu hanzarta ku Fito mu Tafi..Saboda asallaceshi da wuri a kaishi Gidansa na gaskiya.."Yana mgana ya Kama Hajja Data kusa Fadi ya kuma Riko Hannun Aiya Mommy ta Tallafo Diza Dake Zubar kwallah ta Zama kamar Mutum mutum kawai Rumana Data ga Ta yunkura ta mike Aisha ta Taimaka mata Suka Rufa musu Baya Cikin Alhini da Rauni.
Kamar yadda aka Tsara hakan ce ta Faru Baba Habibu Shi ya Bi Motar Gawan Su kuma Matan Direban Daddy ya Tukasu Rumana kuma Aisha ta karbi Key din ta tukasu Sauran Jama"ar Mansur suka Rufa musu Baya Irin su Sagir Cikin Tashin Hankali.
Zuwa Lokacin da suka isa anguwan Tuni Rasuwan ta isa kunnen Mutane Tunda Gidajen Radio sun Watsa Labarin,Daddy kuma Tun yana asibitin sukayi mgana da Baba Habibu kan Lokacin Jana"iza karfe 4:00pm na yammah Tunda Hatsarin ya Faru ne wajen karfe 9:30am na Safe da kawo su asibiti da karban gawan da komai 11am na Safe ma ya wuce suka Dawo saboda Sauran Mutane da kuma Uwa Uba Mastur Da ake ta kira akashe Za"a Jingirta Domin yazo ya Sallaci gawan Dan"uwansa kafin kace kwabo anguwa ta Cika da al"umma kama Daga Abokan Siyasan Mansur matasa yan makaratansu Yan maruka ma sun iso Cikin Raunin Zukata Sai aka Hade Falon Hajja ana ta kuka Kamar me,Ba iya Cikin Gida ba Har waje magidanta kuka suke na Rashin Mansur haka Matasa,Inna karime ma ta iso Ita da Mijinta Tana kuka,Sai ga Maryama itama ita da mijinta da Kishiyarta ajaran majaran Ita bata ma ji Ba Mijin nata ne yaga Labarin na yawo A social media yazo ya gayamata Tunda yasan Yayanta ne, Shine fa Hankula suka Tashi Ajaran majaran suka Taho.
Tana Shigowa sai kuka kuma ya Karu Gawan Mansur Tana Uwar Dakin Hajja ne,chan aka kaisa Hajja na gefe sanye da Hijabi da Carbi Tana ja kuka ya Dauke mata Mommy na gefenta itama Cikin Hijabi da Qur"ani a Hannunta Tana karatu sai Daga Chan Gefen Diza ce Zaune tana Jingine da Bango Tana Sanye da katon Hijabin Hajja sai Carbi Dake hannunta ta kura ma gawan Mansur ido Dake Lullube da Zani tana Zubar kwallah Shaa!!! Kamar famfo Gefenta kuma Rumana ce itama Cikin Hijabi Itama kuksn take sai Kawarta Aisha itama sai Sharan kwallah take sai mardiya,Sakina dasu Mariya suna Falon Hajja suna ta kuka dasu Balaraba da Sauran matan Baffanin Baba Sule,da sauran Makota da suka Shigo,Ana cikin hakane sai ga Umma ta iso ita da Anty Saratu itama Tana shiga taga gawan Mansur sai ta Fadi Tana Kuka Hawaye na Zubar mata take Fadin"Allahu akbar..Allah jikan ka Mansur Allah ya maka Rahma..Allah ya sadaka da Mala"ikun Rahma..Allah Sarki Rayuwa kenan..'Take Fada Tana kuka Anty Saratu na Riketa itama Tana Sharan kwallah Dagata tayi suka koma Gefen Hajja suka Zauna Cikin kuka take Fadin"Hajja ya muka ji da Hakurin wannan Babbar Rashin..?
Hajja ta Bude baki Cikin Shakkiyar Muryan Dataji kuka tace"Hakuri..Namu ne Duka Hajiya sannunku da zuwa. mansur ya tafi ya barmu..Shima yazo ya tafi kamar yadda Mahaifiyarsa Maryama Tatafi ta barmu.."
Umma na kuka take Fadin"Allah ya musu Rahma..Allah ya sadashi da mala"ikun Rahma..An gayama Shi Dan"uwan nashi..? Har muka iso Abban Ruma nata kiransa Wayarsa Tana kashe..!
Wannan karon Mommy ce Tayi mgana cikin Zubar kwallah Tace"Duka an kira wayoyinsa a kashe..Ba'a samesa ba..Su Alhaji sunce baza"a jira sa ba..Gwara ayi a Sallacesa Zuwa Gidansa na gaskiya..Tun dazu ma da suka Shogi nan har sun kira Chan dambom makabarta an Fara Hakan kabari nan kuma Usman Mijin balaraba ya tafi Hado likafani da kayan wanka..!
Tana Fade tana Sharan kwallah Umma ta gyada kai tana Fadin"Allahu akbar..Rai bakon Duniya.!.
Rumana ta mike tsam ta Fice Daga Dakin Bata kuka sai dai idanuwanta sun yi Jajir Saboda kuka kitchen ta Shiga ta Zaro wayarta Cikin Haban Sikat din ta Kara Nenan Layin Mastur bata shiga Kawai sai ta yanke Shawaran Turamai sako.
*Ya Mastur kana ina ne..? Ko a ina kake kazo gida ba lafiya..*
Daga haka ta Turamai kana ta Fito Daga kitchen Dakin Aiya ta Shiga Aiya tana Falo kamar ma ta Rude sai mganganu take,Dake da Tiolet ta Shiga ta Dauro alwala tazo ta Dauki Aqur"ani Ta koma Dakin ta koma inda tatashi Ta Bude Qur"ani ta Fara karatu Cikin Sanyi da Rauni Duk Sai Dakin ya Dau Shuru kowa yana ji Bugawar Zuciya da Rauni mai Tsanani.
*****
Shigowarsa Office dinsa kenan yau tun safe bai zauna ba wani Operation suka Tafi kuma Abun Farincikin Operation din is Sessufull,Sai da ya zauna kan kujeransa ya Tuna daya kashe wayoyinsa tun Safe bai ma Tafi dasu ba nan Cikin Office din ya watsar dasu Tun Shigowarsa da Safe.