Sashe 83
Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 9 min read
Afalon Mommy Ta zaunar da ita ita kuma ta Shiga Cikin Bedroom din da Sauri Ta taso Daddy jin Rumana tazo tana kuka yasa Jallabiya kadai ya Zura ya Fito Cikin Tashin Hankali Rumana na ganinsa ta Mike Tana kuka Shar Hawaye suna ta Zubo mata kamar an Bude Famfo Daddy ya kalli Mommy itama ta kalleshi Cikin wani yanayi wajenta ya karisa Cikin Wani Hali yace"Subhanallah Rumana Lafiya kike kuka..?
Jin haka yasa ta kara saka kukanta Lokaci Daya ta Zube gabam Daddy Tana Fadin"Don Allah Daddy..Ka Rufamana asiri..Ka Aura ma YA MASTUR Diza in ba so kake mu rasashi kamar yadda muka rasa Mansur Ba Daddy..!
Tafada Cikin gunjin kuka da wani Kishi Hade da Soyayyar Mijinta,Ba Daddy da Mommy sukaji Mganar kamar Daga sama ba Hatta Diza dake bakin kofar Shigowa Sai ta Taji wani Dum! Dum! Sau Biyu kanta ya wani Sara mata Sai ta kasa Shiga Dakin ta Dakata tana jin wani Bakon Lamari yana Ratsa gangan Jikinta me Rumana take so ta Fada?
Metake Nufi ne..? Wata mgana ce take so ta Furta...?
Bata gama mamaki ba Taji Daddy na Fadin"Rumana wata irin mgana kike Fadi haka Rumana..?
Yafada Lokaci Daya yana Dagota Daga Durkushen ya Zaunar da ita kan kujera Mommy ma ta ksa Mgana Saboda yadda Taji mganar.
Rumana ta gyada kai Tana Fadin"Eh Daddy..Im kukayi kuskuran barin Diza ta auri Sagir ina mai Tabbatar muku Zamu rasa Ya Mastur Shima zai barmu har Abada Kamar yadda Mansur ya barmu..!
Daddy ya kura mata ido Cikin wana yanayi Gefenta ya Zauna yana Dafa kafadarta lokaci Daya yana Fadin"Naji duk mganarki Rumana ammh meyasa kika ce haka..?kuma shi Mastur din ne ya aiko ki..?
Rumana na Sharan Hanci Tace"Bashi ya aiko ni ba Daddy ni na aiko kaina..Asali ma baisan na san Halin Dayake Ciki ba!
Mommy ta kalli Daddy shima ya kalleta kafin ta maida kallonta kan Rumana tace"Wani Hali yake Ciki.?
Rumana ta gyara zama Cikin Zubar kwallah da Shasshekan kuka ta Fara Fadin"Nasan Abunda ke Damun ya Mastur da ba wanda ya sani Daga shi sai Allah suka sani..Nima ba gayamin yayi ba Sanda mukaje wajensa baida Lafiya ne na Samu ganin Diary dinsa na karanta anan nasan Komai..!
Nan ta Fara Basu Labarin Abunda Tagani Rubuce a Diary din Mastur wanda ya Rubutu Tu daga Farkon Fara son Diza da Bullowar mganar Mansur da yadda ya Sadaukar da soyayyarsa ga Dan"uwansa uwa uba kuma da yadda ya Nuna ma Diza bai taba sonta ba ya Roketa ta so Marigayi mansur Saboda Soyayyar datake yimai da Auransa da Rumana da abubuwan da suka Faru Rumana tana mgana tana kuka ta Karishe da Fadin"Hatta da Hawan jinin Daya samu da Ciwon Zuciyarsa Dalilin Diza ne Daddy..Ya mastur ya wahala saboda Soyayyar Diza,saboda Mansur yasa ya Boye abun a ransa bai Taba Fadama kowa ba, Kada wannan karon ya rasata in ya kara rasata zamu rasa gabadaya ne kamar yadda muka rasa Mansur kuma Faruwar haka tamkar bayyanar wani wawaken Rauni ne wanda har Abada bamai iya Cikeshi Daddy..!
Ta fada cikin kuka sosai kamar Zata Shide ba ita datasan Labarin ba Mommy da Daddy da yau suka taba ji haka suke Sharan kwallar Tsausayin Mastur da Dattakonsa,Ballatana Diza da kafafunta suka kasa Daukanta ta Sulale nan kofar Falon Mommy Tana Kuka Lokaci Daya tana Toshe bakinta da Hannayenta kada kukanta ya Bayyana ammh Labarin da Rumana ta bada yasakata cikin wani yanayin da bazata iya Fassarashi nan take ba.
Bata sani ba na Tsausayin Mastur ne ko matsananancin Soyayyarsa.?kawai ita dai taji Zuciyarta na Bugawa da Sauri da Sauri kanta na wani Sarawa.
Achan falon kuwa Daddy ne ya Mike da Sauri yana Share kwallar Tsausayin Mastur yace"Lalle ya cika sunan da iyayensa ke kiransa BABBAN MUTUM..Ku taso..Maza mu je gidan Habibu kowa yaji wannan al"amarin..Al"amarin da ko a mafarki bamu Taba Tsammani ba Asiya sako mayafinki ki kubiyo keda Rumana ki ma Diza mgana ta taho itama..! Yake fada yana kama Hanyar Ficewa saboda Halin Dayake ciki Diza tayi kokarin Mikewa Dakyar suka Kusan cin karo da Daddy ganinta Tana kuka yasa ya gane taji komai kai ya gyada mata yana Fadin"Ki kibiyo su ku taho Tare..!
Daga haka ya sauka kasa a Sarssaafa kamar zai tashi Sama Diza Dakyar ta Rufamai Baya zuwa Daki ta iske Mansur karami bai tashi Daga barci ba ammh bata Cikin Hayyacinta haka ta Daukesa yana barcin ta saba shi a Bayanta ta Goya tana ta Sharan kwallah sai ga Mommy ta Shigo Ganinta Tana ta Faman Sharan kwallah sai ya bata mamaki kafin Tayi mgana Diza ta gyada mata kai Tana Fadim"Naji komai Mommy..Naji komai..!
Take Fada Tana Hawaye,Mommy ta Riko Hannunta Dake Dauke da mayafinta tace"Ki daina kuka Diza..Taho mu tafi Rumana na jiranmu da Daddy..!
Ita ta jawo hannuwanta Har Falon inda suka Tadda Rumana Tsaye Tana jiransu kallon kallon sukayi Tsakaninta da Diza alokacin Kowa yaji kishin kowa Musamman Diza da Rayuwarta Daman Rumana abokiyar kishinta tace,Ita kuma Rumana wani iri taji acikin Ranta na Diza Mastur yake so ba ita ba Akwai wannam Kishin acikin Idanuwanta.
Haka suka karisa gidansu Hajja Jiki a sanyaye koda suka je har Baba Habibu ya Fito yayi ma Daddy Jagora zuwa Cikin Falon,Hajja na gefe zaune Ayya ma Haka su kadai ake jira suna Shigowa zama kawai Sukayi Daddy ya kalli Rumana yana Fadin"Rumana maimaita Abunda kike zomin dashi yanzun nan..!
Rumana bata yi kasa a gwiwa ba ta Shiga maimaita komai Daki Daki,kafim ta gama Hajja ta Fashe da kuka Tana Fadin"Biri yayi kama da Mutum..Baban Mansur ka Tuna Bayan Bikin yaranan nayi maka Zencen Babban Mutum..?
Baba Habibu da gabadaya Jikinsa yagama yin sanyi yace"Tabbas..Kin min Zencen gabadaya ya sauya ya Rame.
yanzu ya kara zama mara som mgana da Hayaniya kikacemin kina ganim kamar wani abu na Damunsa nace miki kada ki Damu kanki Lafiyansa lau..Wlh nima alokacin nace miki Hakane kawai ammh ni kaina nasan ya Chanza ammh Tunda har ni da kaina na Tambayeshi meke Damunsa yace bakomai sai kawai acikin Raina na Cigaba da Tayasa addu"a Allahu Akbar Allah ya jikam Mansur da Rahma..Tabbas Mastur yayi Rashi..da sun Rayu da juna da An samu Nagargartattun yan"uwa masu Sadaukar da komai nasu Domin junansu na Tabbata da Mansur yasan Mastur na son Hadiza Wlh Tallahi shima bazai aureta ba zai ce ne ya bar ma Dan"uwansa sai dai shi Lamarin Ubangiji muna namu Allah na nashi ne..Tabbas Rabon samun Mansur karami yasa akayi wannan Auran Rasuwar mansur kuma wata aya ce nacewa Akwai Rabon Zama Tsakanin Mastur da Hadiza Tabbas bazamu ja da Hukuncin Allah ba..,!
Ya karishe fada yana Saurin Dauke Hawayen Daya kawo masa Ayya ma da Jikin Tsufanta Tana Sharan kwallah tana Fadin"Allah yayi maka Rahma Mansur..Habibu Alhaji ku aura ma Megidana Hadiza ko bai ce yana Sonta ba Duk Duniya shi kadai zai riketa ita da mansur karami Cikin aminci kuma na Tabbata Mansur zai samu salama Cikin kabarinsa sanin Hadiza da Mansur karami bazasu Tagayyara ba!
Kowa sai da kalaman Ayya ya sakashi kuka barin ma Diza da Tunda aka Zauna take kuka,Mansur karami ya tashi ganin Mamansa na kuka shima sai ya Fara Saukoshi Tayi ta Rumgume Tana kuka,Rumana kuwa kanta na kasa Cikin Dashewar murya tace"Ayanzu haka yana nan gida na barsa Ba yadda yake..Tun jiya Daya ga Diza da Sagir..Yau da safe har Aman jini sai da yayi..!
Gabadaya Falom aka Dauki Salati Daddy ya Mike da Hanzari yana Fadin"Habibu ku tashi muje Chan gidan nasu Kada shima mu Rasashi indai Hadiza ce na bashi ita Halak malak..Ku tashi mu Tafi Gabadaya muje mu Hada hannunshi da na Hadiza Domin ya Tabbatr da ita din kaddara ta Riga ta Hadasu waje Daya..!da sauri kowa ya mike Hajja batama Tsaya Daukan Hijabi ba Zanin atamfanta ta yafa ta kama Ayya datake kokarin mikewa ta saka mata Hijabi suka Bi bayansu Daddy da suka Fita Tuni.
Rumana ita ta Tuka matan Shi kuma Daddy da Baba Habibu da Mansur karami Dake hannunsa suna Motar Daddy.
Basu ci burki ko"ina ba sai Haraban Gidan Su Rumana Dake Lowsoct,Suka paka Motocinsu Cikin Hanzari suka Firfito Rumana ne kan gaba ta Jagorancesu zuwa Shashensu ba wanda yayi Tunanin Tsayama a Falo Gabadayansu Cikin Bedroom din suka Nausa Rumanace ke gaba suna Binta Sahu sahu a baya bamai mgana ammh kowa kagani Kirjinsa na Bugawa.
Suna Shiga suka iskeshi kwance ya Lumshe idanuwansa ba barci yake ba Yaji Sallaman Rumana sauran Sallaman ne bai ji ba saboda ba suyi sallama ba Hankalinsu baya jikinsu gabadaya su Gaban gadon suka Tsaya Banda Diza Dake Chan gefe Tana kallon Mastur yadda rame dare Daya ya koma haka.
Rumana ce ta Durkusa ta Dafa Hannayensa Tana Fadin"Ka Bude idonka..Naje na samo maka mganin Mtsalarka tare nake dasu Daddy har da ita kanta Dizan Daka ke kwance saboda ita..!
Kamar a mafarki yaji kalaman Rumana cikin mamaki ya Shiga Bude idanuwansa Karaf ya fara saukewa kan Daddy da Baba Habibu,sai Mommy da Hajja, da Ayya Dake gefe Tana Sharan kwallah sai Daga gefe kuma Diza ce Take ta kuka ya kasa Sauke idanuwansa Daga kanta yana jinsa kamar Zuciyarsa Zatayi Tsalle ta Fito waje gefe Daya kuma yana Jin mganar Rumana kamar a mafarki.
Daddy ne ya zauna gefen Mansur din ya saka Hannu ya Dagosa yana Fadin"Tashi Tashi..Ba a son Namiji kamar ka da Ragwanci..Abokan aikin ka zasu yi maka Dariya in sukaji Labarin Saboda mace kake kwance Zaka Mutu.Maza ka Mike indai Hadiza ce na baka ita Halak malak..Zan Daura muku aure yau bayan Sallar azahar da yardan Allah..!
Shidai gashi nan zaume ne yana bin kowa da kallo mganganun Daddy da Rumana kamar bai Fahimci ina suka Dosa ba sai dai kawai yayi shuru bakinsa yayi Nauyi Mansur karami ne yake ta mikamai hannu yana kiran Baba sai Baba Habibu ya mikamai shi ya karbeshi,kana Baba Habibu ya Dafa kan Mastur din yana Fadin"A gaishe da Babban Mutum..Banda abunka ai Hadiza Takace meyasa bakayi mgana ba Tun Fari..? Tunda Kaddara ta Dauke Dan"uwanka kai ya Dace ka aureta Daman ka zama Bangonta Mastur.!
Mastur da sai yanzu ya samu Damar mgana Cikin wani Nauyin baki yace"Baba..Waya fada muku wannan mganar..?
Kafin yayi mgana Rumana tace"Nice..Na karanta komai acikin Diary dinka Daka Rubuta Lokacin Danaje Porthercourt na Zauna Dakai..Tun lokacin nayi alkawarin wa kaina Zan samo Sillan da zaka samu Abunda kake so..So yayyata dakai bazatayi Sillar da zan kasa Taimaka ka samu Abunda kake so ba..!
Kura mata ido kawai yana kallonta Lokaci Daya Zuciyarsa na Budewa da Kofofi kofofin yarda da Aminci da Soyayyar Rumana wanda bai san Daga ina hakan yake Faruwa ba Hawayenta ta Share tana Fadin"Insha Allahu yau Zaka Zama angon Diza...Daga barayina nayi maka alkawarin bazaka Taba Samun wata mtsala ba sai dai Kuskure na Dan Adam..!
Gabadaya sai ta bama kowa Tsausayi a wajen Mommy ta Rumgumota Jikinta Tana Fadin"Allah yayi miki albarka Rumana..!
Acikin Zuciyar Mastur kuma yace"Ameen..Allah ya Biyaki Rumana..Allah kada ya kamani da Hakkin Sabamiki koda da Rana Daya..!
Yake fada Cikin Ransa Lokaci Daya yana kallonta itama shi take kallo Tana Dariya sai Lokacin ta waiga taga ba Diza Mastur yaga Lokacin Data Fita su Hajja Falo suka Fita suka bar Shi da Baba Habibu da Daddy suna ta mai Nasiha da nuna yadda Al"amarin Allah yake.
Diza kuma suna Falo tare dasu Mommy,Kuka kawai take yi kowa ya kasa gane inda ta dosa Su Daddy Basu dade ba suka Fito sai ga Mastur Kan kafafunsa ya Rakosu yana Rike da Mansur Karami har bakin mota suka Rakasu shi da Rumana inda Daddy ya kara Jadadda Bayan Sallar Azahar za"a Daura auran Diza ta Fara shiga Mota Mastur bai tsaya Fahimtar yanayinta ba Rumana kawaiyake kallo yana aika mata Godiyarsa da ido Mansur karami yaki Bin su Mommy sai Rumana tace abarshi in zasu zo zasu zo dashi.
Jin haka yasa ta kara saka kukanta Lokaci Daya ta Zube gabam Daddy Tana Fadin"Don Allah Daddy..Ka Rufamana asiri..Ka Aura ma YA MASTUR Diza in ba so kake mu rasashi kamar yadda muka rasa Mansur Ba Daddy..!
Tafada Cikin gunjin kuka da wani Kishi Hade da Soyayyar Mijinta,Ba Daddy da Mommy sukaji Mganar kamar Daga sama ba Hatta Diza dake bakin kofar Shigowa Sai ta Taji wani Dum! Dum! Sau Biyu kanta ya wani Sara mata Sai ta kasa Shiga Dakin ta Dakata tana jin wani Bakon Lamari yana Ratsa gangan Jikinta me Rumana take so ta Fada?
Metake Nufi ne..? Wata mgana ce take so ta Furta...?
Bata gama mamaki ba Taji Daddy na Fadin"Rumana wata irin mgana kike Fadi haka Rumana..?
Yafada Lokaci Daya yana Dagota Daga Durkushen ya Zaunar da ita kan kujera Mommy ma ta ksa Mgana Saboda yadda Taji mganar.
Rumana ta gyada kai Tana Fadin"Eh Daddy..Im kukayi kuskuran barin Diza ta auri Sagir ina mai Tabbatar muku Zamu rasa Ya Mastur Shima zai barmu har Abada Kamar yadda Mansur ya barmu..!
Daddy ya kura mata ido Cikin wana yanayi Gefenta ya Zauna yana Dafa kafadarta lokaci Daya yana Fadin"Naji duk mganarki Rumana ammh meyasa kika ce haka..?kuma shi Mastur din ne ya aiko ki..?
Rumana na Sharan Hanci Tace"Bashi ya aiko ni ba Daddy ni na aiko kaina..Asali ma baisan na san Halin Dayake Ciki ba!
Mommy ta kalli Daddy shima ya kalleta kafin ta maida kallonta kan Rumana tace"Wani Hali yake Ciki.?
Rumana ta gyara zama Cikin Zubar kwallah da Shasshekan kuka ta Fara Fadin"Nasan Abunda ke Damun ya Mastur da ba wanda ya sani Daga shi sai Allah suka sani..Nima ba gayamin yayi ba Sanda mukaje wajensa baida Lafiya ne na Samu ganin Diary dinsa na karanta anan nasan Komai..!
Nan ta Fara Basu Labarin Abunda Tagani Rubuce a Diary din Mastur wanda ya Rubutu Tu daga Farkon Fara son Diza da Bullowar mganar Mansur da yadda ya Sadaukar da soyayyarsa ga Dan"uwansa uwa uba kuma da yadda ya Nuna ma Diza bai taba sonta ba ya Roketa ta so Marigayi mansur Saboda Soyayyar datake yimai da Auransa da Rumana da abubuwan da suka Faru Rumana tana mgana tana kuka ta Karishe da Fadin"Hatta da Hawan jinin Daya samu da Ciwon Zuciyarsa Dalilin Diza ne Daddy..Ya mastur ya wahala saboda Soyayyar Diza,saboda Mansur yasa ya Boye abun a ransa bai Taba Fadama kowa ba, Kada wannan karon ya rasata in ya kara rasata zamu rasa gabadaya ne kamar yadda muka rasa Mansur kuma Faruwar haka tamkar bayyanar wani wawaken Rauni ne wanda har Abada bamai iya Cikeshi Daddy..!
Ta fada cikin kuka sosai kamar Zata Shide ba ita datasan Labarin ba Mommy da Daddy da yau suka taba ji haka suke Sharan kwallar Tsausayin Mastur da Dattakonsa,Ballatana Diza da kafafunta suka kasa Daukanta ta Sulale nan kofar Falon Mommy Tana Kuka Lokaci Daya tana Toshe bakinta da Hannayenta kada kukanta ya Bayyana ammh Labarin da Rumana ta bada yasakata cikin wani yanayin da bazata iya Fassarashi nan take ba.
Bata sani ba na Tsausayin Mastur ne ko matsananancin Soyayyarsa.?kawai ita dai taji Zuciyarta na Bugawa da Sauri da Sauri kanta na wani Sarawa.
Achan falon kuwa Daddy ne ya Mike da Sauri yana Share kwallar Tsausayin Mastur yace"Lalle ya cika sunan da iyayensa ke kiransa BABBAN MUTUM..Ku taso..Maza mu je gidan Habibu kowa yaji wannan al"amarin..Al"amarin da ko a mafarki bamu Taba Tsammani ba Asiya sako mayafinki ki kubiyo keda Rumana ki ma Diza mgana ta taho itama..! Yake fada yana kama Hanyar Ficewa saboda Halin Dayake ciki Diza tayi kokarin Mikewa Dakyar suka Kusan cin karo da Daddy ganinta Tana kuka yasa ya gane taji komai kai ya gyada mata yana Fadin"Ki kibiyo su ku taho Tare..!
Daga haka ya sauka kasa a Sarssaafa kamar zai tashi Sama Diza Dakyar ta Rufamai Baya zuwa Daki ta iske Mansur karami bai tashi Daga barci ba ammh bata Cikin Hayyacinta haka ta Daukesa yana barcin ta saba shi a Bayanta ta Goya tana ta Sharan kwallah sai ga Mommy ta Shigo Ganinta Tana ta Faman Sharan kwallah sai ya bata mamaki kafin Tayi mgana Diza ta gyada mata kai Tana Fadim"Naji komai Mommy..Naji komai..!
Take Fada Tana Hawaye,Mommy ta Riko Hannunta Dake Dauke da mayafinta tace"Ki daina kuka Diza..Taho mu tafi Rumana na jiranmu da Daddy..!
Ita ta jawo hannuwanta Har Falon inda suka Tadda Rumana Tsaye Tana jiransu kallon kallon sukayi Tsakaninta da Diza alokacin Kowa yaji kishin kowa Musamman Diza da Rayuwarta Daman Rumana abokiyar kishinta tace,Ita kuma Rumana wani iri taji acikin Ranta na Diza Mastur yake so ba ita ba Akwai wannam Kishin acikin Idanuwanta.
Haka suka karisa gidansu Hajja Jiki a sanyaye koda suka je har Baba Habibu ya Fito yayi ma Daddy Jagora zuwa Cikin Falon,Hajja na gefe zaune Ayya ma Haka su kadai ake jira suna Shigowa zama kawai Sukayi Daddy ya kalli Rumana yana Fadin"Rumana maimaita Abunda kike zomin dashi yanzun nan..!
Rumana bata yi kasa a gwiwa ba ta Shiga maimaita komai Daki Daki,kafim ta gama Hajja ta Fashe da kuka Tana Fadin"Biri yayi kama da Mutum..Baban Mansur ka Tuna Bayan Bikin yaranan nayi maka Zencen Babban Mutum..?
Baba Habibu da gabadaya Jikinsa yagama yin sanyi yace"Tabbas..Kin min Zencen gabadaya ya sauya ya Rame.
yanzu ya kara zama mara som mgana da Hayaniya kikacemin kina ganim kamar wani abu na Damunsa nace miki kada ki Damu kanki Lafiyansa lau..Wlh nima alokacin nace miki Hakane kawai ammh ni kaina nasan ya Chanza ammh Tunda har ni da kaina na Tambayeshi meke Damunsa yace bakomai sai kawai acikin Raina na Cigaba da Tayasa addu"a Allahu Akbar Allah ya jikam Mansur da Rahma..Tabbas Mastur yayi Rashi..da sun Rayu da juna da An samu Nagargartattun yan"uwa masu Sadaukar da komai nasu Domin junansu na Tabbata da Mansur yasan Mastur na son Hadiza Wlh Tallahi shima bazai aureta ba zai ce ne ya bar ma Dan"uwansa sai dai shi Lamarin Ubangiji muna namu Allah na nashi ne..Tabbas Rabon samun Mansur karami yasa akayi wannan Auran Rasuwar mansur kuma wata aya ce nacewa Akwai Rabon Zama Tsakanin Mastur da Hadiza Tabbas bazamu ja da Hukuncin Allah ba..,!
Ya karishe fada yana Saurin Dauke Hawayen Daya kawo masa Ayya ma da Jikin Tsufanta Tana Sharan kwallah tana Fadin"Allah yayi maka Rahma Mansur..Habibu Alhaji ku aura ma Megidana Hadiza ko bai ce yana Sonta ba Duk Duniya shi kadai zai riketa ita da mansur karami Cikin aminci kuma na Tabbata Mansur zai samu salama Cikin kabarinsa sanin Hadiza da Mansur karami bazasu Tagayyara ba!
Kowa sai da kalaman Ayya ya sakashi kuka barin ma Diza da Tunda aka Zauna take kuka,Mansur karami ya tashi ganin Mamansa na kuka shima sai ya Fara Saukoshi Tayi ta Rumgume Tana kuka,Rumana kuwa kanta na kasa Cikin Dashewar murya tace"Ayanzu haka yana nan gida na barsa Ba yadda yake..Tun jiya Daya ga Diza da Sagir..Yau da safe har Aman jini sai da yayi..!
Gabadaya Falom aka Dauki Salati Daddy ya Mike da Hanzari yana Fadin"Habibu ku tashi muje Chan gidan nasu Kada shima mu Rasashi indai Hadiza ce na bashi ita Halak malak..Ku tashi mu Tafi Gabadaya muje mu Hada hannunshi da na Hadiza Domin ya Tabbatr da ita din kaddara ta Riga ta Hadasu waje Daya..!da sauri kowa ya mike Hajja batama Tsaya Daukan Hijabi ba Zanin atamfanta ta yafa ta kama Ayya datake kokarin mikewa ta saka mata Hijabi suka Bi bayansu Daddy da suka Fita Tuni.
Rumana ita ta Tuka matan Shi kuma Daddy da Baba Habibu da Mansur karami Dake hannunsa suna Motar Daddy.
Basu ci burki ko"ina ba sai Haraban Gidan Su Rumana Dake Lowsoct,Suka paka Motocinsu Cikin Hanzari suka Firfito Rumana ne kan gaba ta Jagorancesu zuwa Shashensu ba wanda yayi Tunanin Tsayama a Falo Gabadayansu Cikin Bedroom din suka Nausa Rumanace ke gaba suna Binta Sahu sahu a baya bamai mgana ammh kowa kagani Kirjinsa na Bugawa.
Suna Shiga suka iskeshi kwance ya Lumshe idanuwansa ba barci yake ba Yaji Sallaman Rumana sauran Sallaman ne bai ji ba saboda ba suyi sallama ba Hankalinsu baya jikinsu gabadaya su Gaban gadon suka Tsaya Banda Diza Dake Chan gefe Tana kallon Mastur yadda rame dare Daya ya koma haka.
Rumana ce ta Durkusa ta Dafa Hannayensa Tana Fadin"Ka Bude idonka..Naje na samo maka mganin Mtsalarka tare nake dasu Daddy har da ita kanta Dizan Daka ke kwance saboda ita..!
Kamar a mafarki yaji kalaman Rumana cikin mamaki ya Shiga Bude idanuwansa Karaf ya fara saukewa kan Daddy da Baba Habibu,sai Mommy da Hajja, da Ayya Dake gefe Tana Sharan kwallah sai Daga gefe kuma Diza ce Take ta kuka ya kasa Sauke idanuwansa Daga kanta yana jinsa kamar Zuciyarsa Zatayi Tsalle ta Fito waje gefe Daya kuma yana Jin mganar Rumana kamar a mafarki.
Daddy ne ya zauna gefen Mansur din ya saka Hannu ya Dagosa yana Fadin"Tashi Tashi..Ba a son Namiji kamar ka da Ragwanci..Abokan aikin ka zasu yi maka Dariya in sukaji Labarin Saboda mace kake kwance Zaka Mutu.Maza ka Mike indai Hadiza ce na baka ita Halak malak..Zan Daura muku aure yau bayan Sallar azahar da yardan Allah..!
Shidai gashi nan zaume ne yana bin kowa da kallo mganganun Daddy da Rumana kamar bai Fahimci ina suka Dosa ba sai dai kawai yayi shuru bakinsa yayi Nauyi Mansur karami ne yake ta mikamai hannu yana kiran Baba sai Baba Habibu ya mikamai shi ya karbeshi,kana Baba Habibu ya Dafa kan Mastur din yana Fadin"A gaishe da Babban Mutum..Banda abunka ai Hadiza Takace meyasa bakayi mgana ba Tun Fari..? Tunda Kaddara ta Dauke Dan"uwanka kai ya Dace ka aureta Daman ka zama Bangonta Mastur.!
Mastur da sai yanzu ya samu Damar mgana Cikin wani Nauyin baki yace"Baba..Waya fada muku wannan mganar..?
Kafin yayi mgana Rumana tace"Nice..Na karanta komai acikin Diary dinka Daka Rubuta Lokacin Danaje Porthercourt na Zauna Dakai..Tun lokacin nayi alkawarin wa kaina Zan samo Sillan da zaka samu Abunda kake so..So yayyata dakai bazatayi Sillar da zan kasa Taimaka ka samu Abunda kake so ba..!
Kura mata ido kawai yana kallonta Lokaci Daya Zuciyarsa na Budewa da Kofofi kofofin yarda da Aminci da Soyayyar Rumana wanda bai san Daga ina hakan yake Faruwa ba Hawayenta ta Share tana Fadin"Insha Allahu yau Zaka Zama angon Diza...Daga barayina nayi maka alkawarin bazaka Taba Samun wata mtsala ba sai dai Kuskure na Dan Adam..!
Gabadaya sai ta bama kowa Tsausayi a wajen Mommy ta Rumgumota Jikinta Tana Fadin"Allah yayi miki albarka Rumana..!
Acikin Zuciyar Mastur kuma yace"Ameen..Allah ya Biyaki Rumana..Allah kada ya kamani da Hakkin Sabamiki koda da Rana Daya..!
Yake fada Cikin Ransa Lokaci Daya yana kallonta itama shi take kallo Tana Dariya sai Lokacin ta waiga taga ba Diza Mastur yaga Lokacin Data Fita su Hajja Falo suka Fita suka bar Shi da Baba Habibu da Daddy suna ta mai Nasiha da nuna yadda Al"amarin Allah yake.
Diza kuma suna Falo tare dasu Mommy,Kuka kawai take yi kowa ya kasa gane inda ta dosa Su Daddy Basu dade ba suka Fito sai ga Mastur Kan kafafunsa ya Rakosu yana Rike da Mansur Karami har bakin mota suka Rakasu shi da Rumana inda Daddy ya kara Jadadda Bayan Sallar Azahar za"a Daura auran Diza ta Fara shiga Mota Mastur bai tsaya Fahimtar yanayinta ba Rumana kawaiyake kallo yana aika mata Godiyarsa da ido Mansur karami yaki Bin su Mommy sai Rumana tace abarshi in zasu zo zasu zo dashi.