← Book details Sadaukarwa So Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 18 OF 94

Sashe 18

Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 8 min read

Abu Dayane Bata samu ba Har yau Abunda Take kwana Dashi Aranta Tana Tashi..Shima Din ta Dangantanshi da Lokaci ne bai yi ba ammh Tabbss In Lokaci yayi Zata mallaki Abunda Take so,Duk yadda suka Shaku Da Mansur Bata Taba gayamai wannan Sirrin Zuciyar nata ba Bata san Dalili ba Gashi Dai baimai yawan Fara"a bane gareta bamai yawan Dariya bane gareta ba,bamai yawan Mata Wasa bane Bata ganin Sakin fuskarsa bane Ballatana Sakin Jiki Da Mutane Haka Allah yayi sa Kuma ahakan Take jin sonsa Aranta Kamar tama fi sonsa akan karan kanta Wanda Gashi dai ba wata Shakuwa sai Tsakanin Girmamawa Ta yaya da kanwa Ammh kuma Batasan ya akayi ba Itadai ta wayi Gari da Soyayarsa wacce kullum Take Huda Duka Gabobinta Tana kara Ninkaya acikin Zuciyarta.

Sai da Ta gama Duba Duka Sakon nin Dake Cikin wayarta,Hauwa ta Kira sukayi mgana kan Wadanda sukayi Buking din kwalliya sun Rabu kan Zata Shigo Zuwa anjuma Merry ta kira sukayi mgana kan Gidan Sarki suna Bukatar oder Cake,Wajen Spicess 3000,Daman ta Sanar dasu Ta kara kira ne Taji komai na Tafiya Daidai Merry Ta Tabbatar mata da nan da Zuwa 1pm komai zai kamallah Sai da suka gama wayar ne ta kalli agogon wayarta pass 10,Cikinta ta Shafa Domin Tana jin Yunwa Tashi Tayi Tana wani naka naka da Fuska Tana kallon Upstairs Baki Ta Tura gaba Ta Nufi Hanyar Kitchen bayan ta Cillar da wayarta kan kujera kamar ta Wurgan da wani abun banza.

Da Sallama ta Shiga Kitchen din Ganin Fadime Datake kira Mama wacce ta Manyanta yanzu Kimamin Shekaru 54 aduniiya Fadime Ta Dago Tana Washe baki tace"A"a Uwar Dakina Har kin tashi..?

Diza Ta Daka Tsalle ta Dane kan Kitchen Cabinet Tana Fadin"Na tashi Mama..Na Fito Ma ko"ina is To Booring Daddy da Mommy basu Sauko ba.."Ta Fada Tana Tura Baki irin na Shagwabbun yaranan da suka samu gata.
Fadime na Soya kwai Daya Cika Kamshin Kitchen din Tace"Zasu Sauko yanzu ai Uwar Dakina.."

Diza TaRausayar dakai Tana Fadin"Ina kwana Mama Fadime.. ? Tana Saka kwan Cikin wani Filet take Fadin"Lafiya lau UwarDakina ya gajiya..? Saukowa Tayi Daga kan Cabinet din Tana Fadin"Ba wata gajiya fa Mama..Ni yau bana jin cin irin wannan Breakafsat din naku Mama bari na Leka wajen Hajja Allah sa Kunu da Kosai Tayi Mana.."

Mama Fadime na Dariya Tace"Hanzarta Domin Kisan Bata Kiyuwan yin kosai Hajja.."Diza ta Fice tana Dariya Fita Tayi Ta koma katayyacen Dakinta kamar Dakin Wata Matar Aure Saboda yadda yaji kayan alatun Rayuwa Babban Wardrope dinta ta Bude ta Dauki Wata Abayarta ta Zura bayan ta Cire kayan Barcin Jikinta Sai ta Dauki Bakin gyalen Abayan ta Yane kanta Dashi,Ta Fito Falo Bayan ta Sauya takalmin kafarta Direct Fita Tayi zuwa Falo ta Dauki Wayarta kana ta fita zuwa Haraban Gidan inda Tsala Tsalan Motoci guda uku suke Fake a Wajen Daya nata ne Daya kuma na Hajiya Asiya ne Dayan ce Ta Alhaji Sunusi.

Gaisawa Sukayi da Baba megadi kana ya bude mata karamar kofa ta Fice Tana Fita Taga matasa Da yawa akofar gidansu Hajja Mirmishin Saman Lebe Tayi Domin tasan mai girma Honourable suke jira Dama Jiya ya gayama ta yau zasu yi Taro da Shugaban Jamiya anan Zaria Bata kula kowa ba duk da wasu sun santa aido Suna ta mata barka da Fitowa Bata tankasu ba Ta Tura Get din Gidan Baba Habibu daya Dawo na Zamani mai Dauke da Sashe Biyu.

Shashen Farkon na Su Hajja ne Shashen Ciki kuma na Mansur da Mastur wanda ke Dauke da Babban Falo sai Kitchen sai Bedroom guda Biyu Daya na Mansur Daya na Mastur ne Gabadaya Gidan kamar bashi ba Bambamacinsa Dana su Diza kawai Bene,Ammh Shima gidan sun kashemai kudi wajen Tsarashi Filin Dake kusa dasu suka Siye sukaHadeshi da Gidansu Shiyasa Filin ya wadata Har aka samu ma"adanar Motoci da Dan Haraban Gidan da suka Fitar ma Get.

Tana Shigowa Haraban gidan da bai Cika Girma ba sosai Taga Mashin din Baba Habiba Domin Yaki yarda Mastur ya siya masa Mota yace su dai su hau shi Mashin dinsa itace Daidai Dashi,Dole suka kyalesa ammh Sun Sauyamai da Roba Roba mai kyau ta Zamani,Sai Motar Mansur kirar Matric Baka,Tana gani ta gane dukkansu basu Fita ba kenan kai Tsaye kofar da sadata da Babban Falon Gidan ta Nufa ta Tura da Sallama Cikin Siririyar Muryanta ta Shiga.

Aiya ce ke Zaune kan Daya Daga Cikin kujerun katon Falon Tana kallo Duk da Tsufa ya kara kamata ammh Jin dadi sun sauka Har yanzu da karfinta sai dai Ciwociwo na Tsoffafi wadanda ba"a rabasu Dashi Tana jin muryan Diza Ta Dago Cikin Fara"a Tana Fadin"Muryan wa nake kamar ta Hadizatu..?

Tafada Cikin muryan Tsufa Wanda Daman kanta Duk ya Cika da Furfura,Diza data kariso ta zauna agefenta Tace cikin Tura baki  "Ni fa Aiya ba sunana Hadizatu ba suna Khadija ko kice min Diza.."Tabe baki Aiya Tayi Tana Fadin"Kwaji Dashi dai..Ku yaran zamanin nan akwai Sanabe..Sunanki suna ne mai Daraja sunan matar ma"aki Sallallahu alaihi wasallam Kuma itace mace ta Farko Data Fara Karban kalmar Shahada a mata kuma ta bada Rabin Dukiyanta wajen yima addinin Allah Hidima ammh Shine kike wasa da sunanki kina maidashi wani wai Dizza.."Ta fada Cikin bayanna Takaichinta Dariya ta kama Diza ta Fara kyakyatawa Sai ga Hajja ta Fito Daga Cikin kitchen din Dake Falon Ta kara zama Babban Mace,Ta kara kyau Domin yazu Rayuwa tayi musu Daidai Tana Fadin"Aiya ke da wa kuma..?

Sai kuma Taga Diza Baki ta Washe Tana Fadin"Diza ashe kece..?ni danaji mgar Aiya ma na Zata Dan albarkan nanne yazo yana Tsokarnata Mansur.."Diza ta Sauko Daga kan kujera ta Duka tana gaida Hajja ta amsa Cikin Fara"a Tana Tambayanta iyayaanta tace suna Lafiya,Kafin tatashi ta koma ta zauna Tana Fadin"Hajja ina Baba..?baifito bane..?

Hajja Tace"Yanzu zai Fito..Na barsa yana wanka ne Dazu.."Diza tace"Ok..Allah sa Koko da kosai kikayi mana Hajja Shi nazo sha nagaji da cin Kwai da Tea wlh.."Hajja na Dariya tace"Kamar kin sani..Yau Daga Baban Mansur Har Mansur din Shi sukace suna son su karya Dashi..Sha kurumakin yanzu zan karisa Toyan kosan.."Tsalle Diza taBuga Tana Fadin"Yauwa..Hajjanmu Har naji Dadi wlh..Muje na Tayaki Soyan Kosan.."

Hajja Tayi Saurin Fadin"a"a barshi..Kwaskon Karshe ya Ragemin Zan karisa aikina Kinji Diza.."Diza ta bata rai Zatayi mgana Hajja tace"kar ki damu Maza Tashi ki leka Abokin naki Yanzu ya bar nan Naji yana Fadin suna da Taro kilama yana chan yana yana Shiriritarsa na Fama.."Mirmishi Diza Tayi ta Mike Tana Fadin"Shikeman Hajja Tunda kin Hanani Tayaki aikin..Bari na lekasa na Dawo.."

Hajja Tace"Yauwa kafin ku Dawo na Gama komai Diyata.."Dariya Diza Tayi Aiya Dake Zaune Tatabe baki Tana Fadin"Katon Saurayi ammh Har yau bai bar Shiririta ba ni bansa ma ya akayi aka Zabe wannan Talasurin ba wlh..Allah sarki Megidana Mastur Namijin Duniya Dan Sanda mai ma kasar sa Hidima.."Daga Hajja Har Diza Dariya suka saka Diza na Ficewa Take Fadin"Zaki maimaita agabansa.."Tana Fada ta Fice ta Fita Zuwa Shashen su Mansur din.

Knooking Ta Farayi Daga Kofar Falon Mansur Daya Ke cikin Dakinsa yana Kokarin Saka Links dinsa na rigar Blue din Shaddan Dake Jikinsa yayi Tsai da Rai sai kuma ya kara,jin Knooking din Cikin Tunanin ko waye ya Fito Daga Bedroom dinsa yana Kokarin saka Links Din Kofar Falon ya isa ya Zare Key din Jiki Bayan ya Bude sai ga Diza ta Bayyana Tana Tsaye Tana kallonsa Shima Idon ya kafeta Dashi kamar zai Cinyeta.
Aduniya in akwai Hallitan Da Baya gajiya da kallo Diza ce..Ita ce wacce ke jan Ragamar Rayuwarsa Gabadaya,Ko Bata gabansa ya Riga ya gama Zana Duka Hotonta acikin Zuciyarsa ko Bata Tare Dashi Da Zarar ya kadaice ita yake gani kuma yaji Har ya samu Sukuni Duk Duniya Bayan Iyayansa da Yayansa Mastur bai Taba son Abu kamar Ransa Kamar yadda yake son Diza ba zai iya Mutuwa Duk Ranar Daya Rasata,
Wani kallon kauna da Muradi mai Girma yake Jifanta Dashi  cikin Matsakaitan Idanuwansa Mansur ya Sauya ya Kara Girma Da Cikar mazantaka,Kallo Daya zakamai kaga kamar Hoton Maryama ce saboda Tsabar yadda kamminsu ya Bayyana Mansur Dogo ne,Sai dai ba Sosai ba Bai kama Kafar Tsawon Mastur ba A kafadan Mastur yake in suka Jera da juna,Mansur yana da Haske sosai Har yafi ma Mastur sai dai Shi Fuskarsa Mai Yalwar Fara"a ce da Barkwanci mai wasa da Dariya da Dadin Zama,Mansur ya zama Cikakken Mutum da Cikar Zati da kamala a Shekarunsa Daya Taka Matakin Rayuwa mai Cike da Nasara da Sa"a Mutane Dadama suna mamakin ganinsa yaro Matashi Ya samu Sa"ar Rayuwa har yake amsa sunan Honourable Mansur Sulaiman Doguwa.

Diza ce Taga ya Shagala da kallonta sai ta Saka Gefen Mayafinta Ta Daki Fuskarsa Tana Fadin"Wannan kallon fa My Honourable,ko baka Taba ganina bane..? Daman haka take Kiransa Shi kuma sai yace mata My Firstlady

Sai Lokacin Mansur ya Dawo Daga Cikin Hayyacinsa Ya saki ajiyar rai bai ce mata komai ba ya Bata Hanya yana Fadin"Bismillah My First lady.."Tayi Dariya kawai Ta Shige Shikuma yamaida kofar ya Rufe yaBiyo bayanta yana Fadin"Kamar kin sani yanzu nake Shirin Kiranki..'"

Tana Zama kan Daya Daga Cikin kujerun Falon Take Fadin"Gani nazo..Ai kasan ko baka nemeni ba Duk inda aka ga gwamna sai anga Firstlady dinsa.."Ta karishe Tana Dagamai Gira Dariya yayi yana Karisa Saka Links Dinsa yace"Nagode My Firstlady.."

Tana Mirmishi ta Kalleshi Sama da kasa Tana Dariya Shima sai yabi kansa da kallo yana Fadin"Ya akayi ne..? Ko Kayan basu yi bane na Sauya su..?

Kai ta Girgiza Tana Fadin"A"a..Kayi kyau My Honourable na..kayan sun maka kyau sosai..Ammh pass 8 fa kada ka makara wajen Taron.."Tafada Tana kallonsa agogon Azurfan Dake Hannunsa ya kai Duba kafin ya dan Yamutsa Fuska yana Fadin"Sai10am za"a Fara Taron..Bari na je na Dauko Hulata da wayata da key din Motata muje Shashen Hajja mu karya kafin na wuce ko..? Zaki fita yau ne ko zakimin Rakiya ne..?

Diza Tace"Eh zan je Office Anjuma akwai wadanda sukayi Bukking din kwalliya..kuma Hauwa Zataje House Service ni kadai ce.."
Chapter 18 · 0% Book details