← Book details Sadaukarwa So Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 24 OF 94

Sashe 24

Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 8 min read

*Domin zama Daya Daga cikin wadanda zasu karanta Labarin SADAUKARWAR SO..! Zaku Biya kudin karatunku kamar haka Masu amfani da Banki Zasu Tura â‚?300 ta wannan asusun banki 0552179550 Jamila umar gtb,Masu Katin waya kuma zasu Turo â‚?400, ta wannan lambar wayar 09069067488 Adauki Hoton katin sai aturo kai Tsaye mutanenmu na Niger kuma zasu Tuntubi wannan lambar kamar haka +22794775574 domin karin bayani,Insha Allahu mutum zai tsinci kansa a paid group ina maraba da ku masoyana Nagode*

*Janafty...*
1/1/22, 18:53 - Maryam Badmsi: *SADAUKARWAR SO..!!*
_(Labarin Yan"uwantaka,Soyayyah Tare da Sadaukarwa)_

*Wattpad:@Jamilaumar315*
*Mallakar:Jamilaumar(Janafty)*

*Page1️⃣2️⃣*

""Kwata kwata yaki Daukan Wayan Mansur Ballatana ya Sauraresa Duk kuwa da nacin Kiran da yake mai da Turamai Sakonnin ban Hakuri yayi mai Biris Abunda ke bashi Mamaki da kanin nashi Har zuwa yanzu bai iya zama ya natsu ba Ballatana ya gano Laifinsa Sai Shirmensa kawai yake in ya Tuna Haka sai yaji Dacin wani abu Ba haka yaso kanin nashi ya zama ba ammh bashi da yarda Zai yi Kullum Mansur ya Girma ne baisan ya Girma ba in yayi wani abun kamar wani yaro karami.

Ya gama gayamawa Kowa yayan nashi na Fushi Dashi..Harda Daddy Da Mommy Sai da suka Kirashi Suna Tambayan Dalili yace musu bakomai Zai kira Mansur aiki ne yamai yawa kowa ya yarda da kalaman Mastur sanin Halinsa kaifi Dayane sai ake Tausan Mansur din yayi ma yayan nashi Uzuri yanayin aikinsu ne Nan kuwa Mansur yasan waye Mastur Irin Horansa kenan kuma yana da Tabbacin Koma wani Laifi ya aikata mai Girma ya bata ran Yayan nashi da bai da kamarsa Duk Duniya Yayan Da baya son ganinsa Cikin Damuwa yayan Dayake Samin abu ya Hanawa kansa Saboda shi..Ya Tabbata Koma Miye ya Faru ya batama Mastur rai matuka Dalilin Dake Hanashi Kwanciyar Hankali kenan Ko Itama Diza tun bata Damuwa Har tazo ta Fara Damuwa ganin yadda Mansur din ya Hana kanshi Sukuni.

Daran Jumma"a ya baro Parthercourt da yammah ya iso Zaria da Safe Misalin Karfe 10:30am nasafe,Ba wanda yasan da zuwansa ko Habibu Bai gayama Ga Ranar da zai Taho ba,Kuma Shi kadai yazo Dan Rakiya Ko Daya bai Taho Dashi ba,Sai dai su Hajja suka gansa kwatsam Lokacin Tuni Baba Habibu ya Tsufa akasuwa Gogan kuwa Yana Ciki yana Barci bai ma Tashi ba Diza ma Tana Gida Bata da masaniya Ita Fita Zatayi Domin Tana da aiki Sosai Yanzu Suna samun yawan Costumer sosai arana gashi Daga ita sai Hauwa,an kawo mata Wasu mata wadanda suka samu kwarewa akan Makeup din ammh Duk basu yi mata ba Bata Daukesu ba Tana dai Cigaba da Dubawa Tun Safe tayi wanka Tashirya Bayan Tayi Taking Breakfast Daddy ya Fita kamfani sunyi baki Abokan Cinikanyasu ne,Mommy kuma Tana Sama bata Sauko Falo ba Ta Fito ta zauna Tana latsan waya Tana Jiran 11am ta cika sai ta Fita.

Shi da kansa ya Bude ma kansa get Daman basu da megadi Bayan nan kuma ya Shigo da Motarsa Cikin Haraban Gidan,Motar Mansur Daya gani yasa yaji Dadi Allah ya Taimakeshi yau ba"a Fita Gantalin Siyansa ba Sai da ya kashe Motar yaDauko Duka Wayoyinsa bai zo da kaya ba Saboda aiki zasu zame mai yana da kaya anan gidan System dinsa kawai yazo Dashi Saboda aiki ita ya Dauko Ya Taka zuwa kofar da Zata sadashi da Falon Hajja Yana Sanye da Riga da wando na Kamfanin Dkny,Black and White sai P.Cap din Dake kansa da Takalmi Booth Daya Rufe kafarsa Dashi.

Sallama yayi da Muryansa mai Cike da Zati Aiya dake zaune ta Fara Jinsa Domin Aiya Gashi dai ta Tsufa ammh akwai son kallo Haka zata gwafe a falo Tana Dale ido,Hajja ma kallon bai Dameta ba,Bata cika Zama ba ko Tana Daki ko Tana Kitchen,Kamar a mafarki Taji Muryansa Cikin Sauri Aiya Ta Dago kai Tana Fadin"ah..ah..Muryan wa nakeji Kamar ta megidana..Lah..Wlh Shine Hajara ke fito ga yaronki Da Safe haka Maraba Maraba da Zuwa..!

Take Fada Cikin Fara"a Kamar bakinta Zai yage Saboda Murna Mirmishi ya saki Har Hakoransa Farare suka Bayyana Dukawa Yayi ya cire Takalmin Kafarsa kana ya kariso Cikin Falon kasa ya Zauna Daidai kafafun Aiya ya ijiye abunda ke Hannunsa yace"Aiya na same ku lafiya..?

Ya Fada yana kallonta Kansa ta Shafa tana Fadin"Lafiya Megidana Dan albarka..Zuwa Haka ba Sanarwa.."Kansa na kasa yace"Saboda yanayin aiki ne Aiya..Kada nace gani zuwa kuma ban samu zuwa ba..! Ina Hajja da Baba..?

Yafada Yana Kara gyara Zama Cikim Fara"a Tace"Eh hakane kam..Hajja tana ciki Habibu kuma ya fita kasuwa Ke Hajara..Ki Fito ga Mastur ya Dawo.."Tafada da dan karfi Hajja Dake Cikin Dakimta Tana Gyaran kayanta Taji kamar Muryan Aiya Dayake ta Kunna Radio ga kuma karan Tibi baisa Taji ba Fitowa Tayi Tana Fadin"Aiya naji..."Mganarta Ta makale ne ganin Mastur zaune yana kallonta Baki ta Washe Tana Fadin"A"a Babban Mutum ne..? saukar yaushe..?

Tafada Cikin Farinciki Tana karisawa Kusa Dashi kansa Ya maida kasa ya Danrankwafa yana Fadin"Ina kwana Hajja..? Yanzu na iso.."Cikin Fara"a ganin Dan nata take amsa mai Lokaci Daya Tana Tambayansa Wajen aikinsa yace Alhamdulillah Mikewa Tayi bayan Aiya tace"Ke Hajara Kawo mai abun kari mana..Kin barsa Zaune kuma kinsan Tafiyar Safe yayi.."Shi dai kawai Mirmishi yayi bai yi mgana ba Hajja Ta Shiga Kitchen Ta Zubomai Soyayyan Dankalin Da Suka karya Dashi Dama na Mansur ne ta Diban mai da kwai sai Fulas din Ruwan Zafi da kayan Tea ta Fito Dauke da Faranti Da Sauri ya Mike ya karba yana Fadin"Sannu Hajja..Da baki Dauki ba da kin Kirani na Dauka Dakaina.."

Yafada yana Ijiyewa nan Saman Cafet Din Daya Malale a tsakar Falon,Hajja Tayi Mirmishi Tana kallon yaron nata Daya kara Sauyawa Tace"ai ka girma da wannan aikin Babban Mutum.."Yana Zama gaban kayan Karyawan yace"A"a Hajja Kin Taba gani ko Jin inda D'a ya girma da yima iyayansa aiki..?

Dariya Tayi Tana kara Godema Allah Daya bata D'a kamar Mastur in yayi mgana ko Baba Habibu albarka,Tea ya fara Hadawa ya Fara kurba Aiya na Gefe Tace"Hala Habibu bai son da Zuwanka bane..? Hajara ko Zaki Kirashi ne ki gayamai..?

Da Sauri ya Girgiza kai yana Fadin"A"a Aiya a kyaleshi ai ina nan ba yau zan koma ba sai Gobe in Allah ya kaimu.."Hajja Tace"Gobe goben nan Babban Mutum..? Kallonta yayi yana Fadin"Eh Hajja..Monday akwai aiki fa..Zuwan Daman Domin na ganku ne..Na kuma Bata ma Mansur rai."Aiya tace"Aifa Koda naji yana ta Sambatun nan nasan wani abu yayi.? mansur sai Shirin Allah ni Habibu ma yayi mai aure ko Zai yi Hankali.."

Hajja na Dariya Tace"Ai ya isa Auran Aiya.."Aiya ta Tabe baki Tace"Ahakan..? Ammh Irinsa Mashiririciya irin yarinyar nan Hadiza ko..? Daman sun Dace da juna a aura musu juna suje Chan su karata bamai ma wani Fada.."Yana kurban Tea ne Aiya ta Fadi haka Sai da yaji Ruwan Zafi ya kasa Shiga Cikinsa ya Tsaya Cak Makogwaronsa Sai kuma Numfashinsa ya Fara sama Sama nan da nan ya Kware ya Fara Tari Hajja da Aiya suka Rude suna mai Sannu nan da nan sai ga Tea din na Biyo Hancinsa Ruwa Hajja ta Ruga Kitchen ta Debomai na sama wanda Take Tarawa a kofi Ta Bashi ya karba ya kafa kai yasha Sosai kana ya Dire Kofin ya Koma yana Jingina da kujera yana Maida Numfashi Su kuma suna aukin Jeramai Sannu.

Ya Dade yana kai da kawo Tsakaninsa da Zuciyarsa da kalaman Aiya kafin ya Iya Daidatuwa Dakyar ya iya Bude Idanuwansa da sukayi Jajir Dasu Kamar Garwashi,ya Muskuta yana Kallon Hajja da Aiya da suka Kwabe Fuska kamar Suyi kuka Mirmishi ya saki kafin yace"Kada ku damu..Bakomai Hajja.."Yafada Lokaci Daya yana Mikewa Domin Gabadaya Cikinsa ya Cushe ne Duk da rabonsa da wani abu Tun Daya Bar Porthercourt ya taho yana mararin abincin Hajja ammh Kalaman Aiya sun saka komai ya Fita kansa.

Ganin ya Mike yasa Aiya Tace"Ah ya haka..?baka karisa karyawan ba Ka tashi..?
P.cap dinsa yadan Ja baya ya Shafa Goshinsa yana Fadin"Sai anjuma Aiya.."Yana Fadin haka ya Duka ya Kwashi Wayoyinsa da System dinsa ya dago yana Kallon Hajja Datayi wani iri kafin yayi mgana Ta Rigasa da Cewa"Kana dai Lafiya ko..,?

Mirmishi yayi mata kafin ya gyada kai yana Fadin"Eh..Hajja bari naje nayi wanka.."Da Sauri tace"Dan"uwanka na nan bai Tashi ba.."jinjina kai yayi bai yi mgana ba ya Fara Takawa zai Fita Tace"Me zan Dafa maka da Rana..?

Yana jin Haka ya waiwayo yana kallonta kafin yayi Mirmishi yace"Nayi kewar Tuwonnki Hajjanmu.."Farinciki ya kamata da Sauri tace"Angama Babban Mutum..Yau zakaci Tuwon Hajja Har ka Koshi.."Kai ya gyada kafin ya Duka ya Zura Takalminsa Ya Dago Hajja Ta Juya Zata Shiga Kitchen da Tiren kayan karyawan Data kawomai yace"Hajja Inna Karime ta Kirani...!

Waigowa Tayi Tace"Yaya karime.? Lafiya..? Cikin Sigan Tambaya Juyawa yayi yana Fadin"Sai na Fito Zamu Tattauna.."Ajiyar rai ta Sauke Tadanyi Mirmishi kafin Tace"Afito Lafiya..'Ranta ba Dadi Domin tasan mganar kenan Yaya karime bata bar mganar Hada Auran Babban Mutum da Yar wajenta Bushira ba,ta Ina Rayuwar Bushara da mastur ta Dace in da ace Zai yi Na"am Datafi kowa Murnan ammh kuma hakan akwai karuwa ga wanda yayi Karatun Boko mai Zurfi ya Rayu a Wayewan waje a Hadashi da wacce ko Hanyar makaranta Bata sani ba Ta Tabbata Mansur bazai karbi Bushara ba Ballatana Babban Mutum.

Bayan Fitansa ne Zata Shige Kitchen Din Dake Falon Taji mganar Aiya Tana Fadin"Uhm..aini Laifin Habibu nagani da bai Takama Karime Burgi ba..Ina Bushara Ina Megidana..! Ai ko Mansur dai Da ba wani Hankali ya Cika ba bana so ya aureta ba Tsakani ga Allah da akwai Cutuwa.."Mirmishi kawai Hajja TayiSanin Halin Aiya Tunda karimen Ta Tako da kanta Tazo Da mganar Aiya ta Kushe Tace bazata Sabu ba Baba Habibu kuma Daman bamai mgana bane yace mgana tana Hannun Mastur Inya amince Shi bai da Ta cewa Mansur kuwa ba wanda ya gayamai mganar ansan Bakinsa Kamar Sikat kada ya gayama Mastur sai gashi Ta Kirashi Da kanta kuma Tunda yace Ta Kirashi Aranta Tasan mganar ne.
Chapter 24 · 0% Book details