← Book details Sadaukarwa So Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 94

Sashe 9

Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tuni an saka Mansur makaranta Inda yake da Shekara 9 a duniya Mastur kuma yana da Shekara 13 aduniya ne yaana aji Shida a primary ayayin da Mansur na primary 3 alokacin Suna zuwa Islamiya da yammah asabar da Lahadi kuma suna zuwa Hadda Na Safe Basu da kowa sai su Balaraba wacce suke kira da Inna Balaraba Hajara kuma Mansur ke kiranta da Hajja Tun yana yaro sai sunan ya Bita Harta da Mastur shima Hajja yake Kiranta Habibu kuma Daya Zama Magidanci yanzu Baba suke Kiransa Zuwa Lokacin Sule na yawan zuwa yana Duba Mansur ganin haka yasa Habibu ya gayamai Shine Mahaifinsa Saboda ya Girma Koda watarana Bashi da Rai yace bai san wannan ba Hatta da Suna a makaranta ma Mansur Sulaiman Doguwa yake amfani Dashi Sabanin Mastur Dayake amfani da Mastur Habib Doguwa Tun alokacin Akwai yarinta atare da Mansur so bai wani Damu ba ya Shiga Sabgarsa.

Tun alokacin Hallayarsu Ta Fara Bambamta Tun suna da kankanin Shekaru Mastur Miskilin Mutun ne wanda mgana bata Damunsa Shi dai barsa da karatu ina zaka Karatu ina ka Fito karatu bashi da yalwar Fara"a Ballatana Sakin Jiki da wanda bai sani ba yana da wuyar sabo da kuma Wuyar Mu"amala,Sabanin Mansur Dayake Tun yana karaminsa mai Fara"A mai Surutu mai yawan waasa da Sakin Jiki da Mutame Shiyasa Mastur yake mai Fada in kaga Mansur na Tura baki Mastur ne ya Tasa shi gaba sai yayi Karatu Shi yafi maida Hankalinsa kan wasa Fiye da Karatu,Ko a makaranta Haka yake da wasa kamar me baya maida Hankali In Mastur yayi mgana Hajja tace yarinta ke Damun Mansur zai bari saboda bata son ana Takuramai Habibu kuwa kullum sai yayi ma Mansur Fadan ya Tsaya yayi karatu ya natsu Tamkar yayansa ammh Ina akace Hallita wani abu ne Wasa da Rashin maida hankali ga Abu ajinin Mansur yake sabanin Mastur da sai ya wuni bai yi mgana ba Shi dai karatu Domin yana da Burin Yayi ilimi mai Zurfi Domin Cika Burinsa na ganinsa Sanye da Kakin D'AN SANDA..!

*Wannan kenan..*

_Albishirunku Masoyana wannan karan na bude muku wani Shashi na musamman Saboda ku..Ina masu Bukatan Atalla musu Hajarsu Ko wani iri ne Domin samun costumer ta ko"ina..? Ku garzayo kakarku ta kusa yanke saka Zan Tallata muku Hajarku a Duka Shafukana Domin inganta Sana"arku da kuma Samun Cinikaya mai Tsabta da kuma kara Hada hada wajen Masi siye da Siyarwa mai Bukatar A tallata mata Hajjarta Zata iya min mgana kai Tsaye ta wannan Lambar Tawa 09069067488 domin karin Bayani...Sai kunzo Kunsan dai mai kasuwa Shi ke da Riba.._

*Domin zama Daya Daga cikin wadanda zasu karanta Labarin SADAUKARWAR SO..! Zaku Biya kudin karatunku kamar haka Masu amfani da Banki Zasu Tura â‚?300 ta wannan asusun banki 0552179550 Jamila umar gtb,Masu Katin waya kuma zasu Turo â‚?400, ta wannan lambar wayar 09069067488 Adauki Hoton katin sai aturo kai Tsaye mutanenmu na Niger kuma zasu Tuntubi wannan lambar kamar haka +22794775574 domin karin bayani,Insha Allahu mutum zai tsinci kansa a paid group ina maraba da ku masoyana Nagode*

*Janafty...
1/1/22, 18:51 - Maryam Badmsi: *SADAUKARWAR SO..!!*
_(Labarin Yan"uwantaka,Soyayyah Tare da Sadaukarwa)_

*Wattpad:@Jamilaumar315*
*Mallakar:Jamilaumar(Janafty)*

*Page5️⃣*

*MAFARI..*
*Kaduna State..Zaria*
_Area:Hanwanfulani_

"Dare ne Domin Duhu ya Shiga Misalin 8:30pm na Dare ne Tunda har anyi Sallar Isha"i kafa ya fara Daukewa Daga anguwa sai dai akwai Wutan lantarki Duhun bai yi yawa ba Tunda Haske kwaya kwayan Gidajen Jama"a ya Haske anguwan.

Suna Zaune a Tsakar gidan kan Katuwar Tabarman da Hajja take Shimfida musu bayan sun yi sallar Isha"i in sun gama cin Abinci sai Mastur ya Tasa Mansur gaba yana Karamai karatu inda bai gane ba Daga na Bokon har na Arabiyan.

Yau ma Hakan ce ta kasance Dukkansu suna kan Tabarman Bayan sun gama cin tuwo Miyar Kukan da Hajja tayi musu,Hajja ta kwashe kwanukan zuwa karamin Kitchen din da aka Gina mata a nan Tsakar gidan Tunda Dakin karshe Habibu ya gyarama su Mansur Na Tsakiyan kuma nan Ayya ke ciki  Dayake Duka Ciki Daya Daya ne Na Hajja ne kadai mai Dauke da Ciki Biyu.

Ayya da Hajja na gefe suna Hira Sama sama Mansur kuma na Zaune Daga gefe yana Dukufa yana Karatu Mastur na zaune gefensa yana kallonsa Shima Wani Littafin ne a Hannunsa na Koyin Turanci yana Dubawa ammh Rabin Hankalinsa na kan kanin nashi ganin Lokaci Bayan Lokaci yana Karatu ne yana wasa Saboda Akwai Hasken kwan Latarki a Tsakar Gida Shiyasa Mansur ya Shiga Taitayinsa Domin yasan In yayan nashi ya kamashi yana Wasa Ransa sai ya baci.

Tundaga waje sukaji Karar Mashin din Baban nasu Mansur Dake karatu ya Dago kansa da Sauri Lokaci Daya yana Mikewa Yana Fadin"Baba..Oyoyo Baba.."Mastur Dake Zaune ya Daga kai yana kallonsa kafin ma ya samu Zarafin mgana Mansur din yayi wuf ya Fita waje da Gudu Da kallo ya Bisa kafin ya Kada kai kawai ya maida Hankalinsa kan Littafin Dake Hannunsa na Teach ur Self.

Ayya ce ta Tabe baki Tana Fadin"Bansan yaushe yaron nan zai Daina wasa ba.."Hajja na kokarim Tashi Tsaye Tace"Ayya zai Daina yarinta ne.."Ayya tace"Ko yaushe haka kike Fadi Hajara ammh Mansur ai wasa yana cikin kansa ne..Shi ko Koyi baya yi da Dan"uwansa Megidana Mastur.."Hajja tana Dariya tace"Ai ba Hallitansu Daya ba Ayyah..Shi wannan Mijin naki ai Miskiline kafi mahaukaci ban Haushi.."

Ayya Tace"Yafi...Da wannan yaron naku mai son wasan Tsiya.."Hajja dai Dariya take yi Daidai Lokacin da Habibu Daya zama Mallam Habibu Uba ga Mansur da Mastur ya Shigo yana Gunguro mashin Dinsa karfe Karfe Mansur na Biye Dashi a baya Dauke da wata Bakar Leda Sai Washe baki yake kamar Gonar auduga Dayake Likafa Taci gaba Habibu ya bar ma Mastur kekensa yana Goya Mansur suna zuwa makaranta ya Siya Mashin.

Sallama yayi su Ayya suka amsa suna mai sannu da Zuwa ya amsa Cikin Fara"arsa Kusa da Madafin ya jingina Mashin Din Kafin ya Kariso kan Tabarma Lokaci Daya yana Cire Takalmin kafarsa Mansur na Biye Dashi kamar Jela ya zauna Bayan ya Kira Sunan Allah Ayya ya kara gaidawa yana mata sannu da gida Ita kuma tana Tambayansa ya kasuwa Hajja Data Fito Daga Daki da kwanukan abinci ta Ijiye gabansa Tana mai Sannu da Zuwa ya amsa yana Tambayanta ya Gidan sai Lokacin Mastur ya Dago kansa Daga Karatun Dayake ya kalli Baban nasu yana Fadin"Sannu da Zuwa Baba.."

Ya Kallesa yana Sakin Mirmishi kafin yace"Yauwa..Babban Mutum ana ta Karatu ne..? Kai kawai ya gyadamai Batare da yayi mgana ba Bai damu ba sanin Halinsa sai kawai yace"Masha Allah..Abada Himma Allah ya Taimaka ya baku Ilimi mai albarka.."Gabadayansu suka amsa da Ameen banda Mansur Dake ta kokarin Fito da Abunda ke Cikin Ledan da Baba ya shigo Dashi Mastur ne ya Lura Dashi Nan da nan ya Dakamai Tsawa Cikin Muryansa kamar ta Babba yace"Bana ce maka ka Daina Taba abunda ba"a baka ba Mansur..? Kai aka kawo mawa..? Bazaka ba Hajja ba Shine zaka zauna kana Budewa kabar Karatunka ka tafi kana wasan ka ko..?

Turo Baki Mansur yayi ya Ijiye Ledan yana Fadin"kayi hakuri ya Mastur bazan kara ba.."Jin yace haka yasa yace"Taso kazo nan..Ka cigaba da Karatun ka.."Ba Musu Mansur ya Mike ya koma gaban Mastur ya Dauki Littafinsa ammh fa Duk Fara"an Dake Fuskar Mansur ta Goshe Saboda ance yazo yayi Karatu Ayya ta kada kai tana Dariya tace"Dakyau..an Hada Mansur da makiyinsa Karatu Dole ya bata rai.."Waigowa yayi yana Bata rai yace"Hajja kinga Ayya ko..?

Hajja Tana Zubama Baba Ruwa yana wanke Hannu Take Fadin"Kyaleta Yi Karatunka Dan albarka na Insha Allahu sai ka Zama gwamna.."Ba Ayya ba Hatta Mastur sai da ya Murmusa bai ce komai ba Baba Daya Ke Dage Hannun Rigansa Zai Fara Cin Abinci yake Fadin"To Ameen Maman Mansur.."Yafada yana yar Dariya Ayya na Tayasa Mansur kuwa Sai Dariya Jin ance zai zama gwamna Mastur na kallonsa bai ce mai komai ba Sai Da ya Dago suka Hada ido kana Yayi Saurin Daukan Littafin Kada kai Mastur yayi yana Fadin"Ba"a zama gwamna ba Ilimi Mansur..Kayi karatu Sosai ka Daina wasa kanina Watarana sai Labari.."Yafada Cikin Sanyin Murya Mansur ya gyada kai yana Fadin"Zan yi Ya Mastur..Zanyi karatu na zama kamar kai Har na zama gwamna.."Ayya Dake jinsu Tace"Dakyau Kaga Daga ranar sai na koma ina Auran Dakai na Zama matar gwamna.."

Baki ya Tura yana Fadin"Lalle wazai aureki..? Sai dai kiyi ma gwamna aiki.."Zuwa yanzu Har Baba Dariya yake Mastur ne ya Murdemai kunni yana Fadin"Kada na kara Jin bakin ka anan wajen.."Da Sauri yace'Angama Yaya.."

Baba Dake cin Tuwonsa Farinciki Duk ya Cikasa yana kallon ya"yansa abun alfaharinsa Har ya gama cin Abincin ya Dauki Butan Dake gefensa ya wanke Hannu yana Fadin"Hajara Dauki Ledan nan Tsire ne aciki ki Raba muku.."Tunda ya ambaci Tsire Mansur ya washe baki Yana Ji kamar ya tashi ya gansa gaban ledan Ammh Sanin Halin Mastur yasa ya maida Zalamarsa Ammh dai Hankalinsa Rabi na kan karatun Rabi na kan Su Hajja Data Kwashe kwanukan zuwa Madafi kana ta Dawo ta Dauki Ledan ta Fito da Tsiren sai Taga Ledan Biskit guda Biyu Ta Dago Tana Fadim"Baban Mansur wannan Biskit din fa Dake Ciki..?

Yana Shan Ruwa ne Take mganar bai bata amsa ba sai da yagama kana yace mata"Daya na Mansur ne Daya na Babban Mutum Yaron Maryama."Daman hakan yake Kiran Mastur wani Lokacin ai Tunkafin Tayi mgana Mansur yace"Hajja bani nawa.."Dariya Tayi ta Mikamai Tana Fadin"Gashi Yaron Hajja..Mastur ga naka.."Kai ya Girgiza mata yana Fadin"ki ijiye ma Mansur Da safe in Zamu Tafi makaranta yaje Dashi.."Baki Mansur ya washe ya Mike yana Tsalle ya Rumgume Mastur yana Fadin"Nagode Yaya.."Ayya da Hajja sai Dariya suke mai Mirmishi kadai yayi mai ya Mike Dauke da littafinsa yana Fadin"Nasan ba karatun zaka karisa ba..Ka shigo ciki mu kwanta da Wuri saboda makaranta Gobe.."Mansur Dake Murnan Biskit dinsa kai kawai ya Dagamai Mastur bai bi ta kansa ba yayi ma su Baba Sai da Safe suka Rakashi da Allah ya Tashemu Lafiya ya Shiga ciki ya Cigaba da Karatunsa Domin Hayaniya ce Baya so Gashi Mansur kuma Hayaniya da Mgana Tamkar ajininsa suke shiyasa ya Gudo Ciki ,nan ma ba wai ya Daina Ji ba sai dai ba kamar yana Tsakar Gidan ba.
Chapter 9 · 0% Book details