← Book details Sadaukarwa So Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 80 OF 94

Sashe 80

Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 5 min read

Diza da kanta ta Nemi Izinin Daddy Akan tana so ta koma Wajenta aikinta Hakan zai Rage mata Zaman kadaici,Daddy bai yi Gaddama ba ya yarda Daman Abunda suke nema ne gashi ya Tabbata su ga Diza ta saki Jikinta ta Dawo kamar Baya,Data gayama Mastur bai ce komai ba Illah Jadadda mata ta kula da Mansur karami,Ta Fara Zuwa Catering dinta Ranar awajensu Hauwa kamar Salla,haka aka Dinga Daukan Mansur karami kamar Za"a Lashesa Saboda ya Saba da Mutane bashi da kiyuwa Sosai Ammh Saboda Daukansa da Bashi Ruwa yasa Diza tayi ma Mommy mgana kan Tana so ta Dauki nanny wacce Zata rika Taimaka mata in sun Fita Mommy Balaraban Usman Tayi ma Mgana ita ta samo musu yar nan kusa dasu Wata yarinya Hanne yar Shekara Sha uku,Diza ta Dauke Zata rika Biyanta Duk Wata akan Lokaci Daman iyayan nata ba wani Hali sai sukaji Dadin hakan.
Da hanne take Tafiya wajen aiki Tana Tayata kula da Mansur in kuma suka Dawo gida shikenan yana wajen Mommy ko kuma yana Gidansu Hajja wajen mardiya ko Ita Hajjan da kansa,Sai ko abunda ba"a rasa ba Daman da sun dawo Diza ke Sallaman Hanne ta koma Gida sai kuma Gobe in zasu Fita in kuma bazata Fita ba sai dai tazo Gida Tazauna Haka ta Daukeshi Zuwa Chan kuma Diza sai ta Sallameta ta koma gida.
Haka suka Cigaba da Tafiyar da Rayuwarsa aduka Bangarorin Rumana Tana Cigaba da zuwa wajen aikinta kuma Lokaci Bayan Lokaci Tana Biyo nan ta gaida su Hajja ta Biya taga Mansur karami da Diza,wacce Manema suka Fara mata ja,Kamar ana jiranta Ciki harda P.A din Marigayi Mansur Sagir,mastur yana chan bai ji Labari ba kuma bawanda ya sanar dashi Diza ma basa gabanta Domin ta Tabbatar musu baxatayi aure ba sai Mansur karami ya Girma.
Sagir dai shine ya Rike wuta da Cewarsa Zaman Amanan da sukayi da marigayi Shi ya Dace ya aureta ya Rike Mansur Karami Tamkar shine ya Haifesa Diza bata amince dashi ba ammh kamar su Daddy sun karbeshi Domin Taga sunyi Na"am Dashi Duk da itama bama wannan ba awannan karon in ba Burin Ranta bazata yarda ta Kara wani Aure ba sai dai ta Hakura.

Rumana bata da Labarin Abubuwan da suka Faru saboda Kwana Biyu bata leko ba aiki yayi mata yawa a asibiti Sai Ranar Lahadi Data Leka Mommy ke mata Zencen Tana Umartatan Data Bama Diza shawaran Sagir Ya Dace da ita Duk da Saurayi ne bai da mata ammh Iyayensa kansu sunyi Na"am da Batun na Diza Rumana Mamaki ya Hanata mgana data samu Diza da mganar ta Fasa mata kuka Dole ta Rabu da ita ammh Taje gida ta kwana tana Tunani ta rasa mafita.
Diza tayi kokarin ta Kaucema Mganar Sagir ammh hakan ya gagara Domin har su Hajja sun yi Na"am dashi yana zuwa Lokaci Bayan Lokaci Hidima kuwa Yana yinta da Jikinsa da Aljihunsa Mansur karami Dan gatane ta ko"ina Har Mastur yazo ganin gida ya koma ba wanda yamai Tadin Sagir,Shima Sagir din baya gari alokacin sai da ya koma yazo
Daddy daya Lura Diza na Karar Sagir da kansa ya kirata ya bata Shawara Akan bazai Tursasata ta auri Sagir ba ammh kuma in ta Zabesa zai ji mata Dadi da karin Shawarwari sosai wadanda suka karya Lagon Diza sosai su Mommy sun Wahala da ita tayarda ta kara rasa Burin ranta akaro na Biyu Tunda shi bai sonta kuma bai Furta mata ba Dadai ta Tsaida wannan Alhazan masu katon Tumbi gwara Tayi Maneji da Sagir din..
Da kanta take Sanar da Rumana Abunda ta yanke game da Sagir ita kuma Tace mata Tayi mgana da Mastur Diza tace A"a sai Abun yazo ba yanzu bane sai ta yaye Mansur karami.

*******

Bayan Shudewar wani Lokaci.
Tuni Mansur karami yana Tafiyarsa ko"ina Lokacin yana watansa na goma da Haihuwa,yana gudunsa ko"ina,yana kara yawo kamaninsa da Marigayi Mansur na kara Bayyana Tare da kwaramiyansa,ya Fara mgana irin nsu na yara ya iya kiran sunan Hajj,da Baba Habibu,da Aiya sai Daddy Dayake kira Baba Diza kuma Mama,Rumana ma Mamace ,Mardiya kuma Anty,Mastur kuma Baba Daman a kansane ya iya kiran sunan Baban
Mansur karami yana ganin gata kowa nan nan yake dashi yan maruka Musamman suke zuwa ganinsa kan Uban kowa su Sakina Lokaci Bayan Lokaci suna zuwa da abun arzikinsu ga Dansu Mansur da suke ganin Tanmkar Dan"uwansu.
Baba Sule kuwa saboda yanayin Tsufa,Diza ke kaimasa Shi ya gansa in ta samu Lokaci Zuwan Datayi na karshe Yana ta mata Nasihan da Lallashin ta Cire komai aranta Tayi auranta Dagajin haka tasan Daddy ne ko Baba Habibu wani yayi Zencen dashi.
To me zata ce..,? Bata da abun cewa Domin wanda takejira bazata samesa ba,kuma ayanzu bata da wani Zabi tunda ta rasa Mansur Taa Cire wani Buri acikin Ranta Tasan bata auri Mansur Domin Tana sonsa ba ammh kuma akwai Shakuwa mai karfi a Tsakaninsu,Ya rasu ya barta da Ciki alokacin Data Fara sonshi Take jin Dadin Zama dashi Har Abada bazata manta wannan Rasuwar ba,mutuwar mansur gareta Tamkar wani gyambo ne acikin Zuciyarta wanda bazai goge ba.
Ashe Sagir ne yazo har nan maruka ya samu Baba Sule da mganar Diza Akan ya Rokar mai ita ta bashi Daman ya Turo mgabatansa Tunda su Daddy sunce bazasu Tursasama Diza Duk Abunda ta yanke Daidai ne,Yazo musu da Kayan abinci kuma ya Zube ma Baba Sule kudade masu yawa ba wannan ne Zuwansa na Farko ba yana zuwa Lokaci bayan Lokaci yace Alherin da Marigayi yayi mai bazai Taba Biyansa ba Dalilinsa gashi Shima yayi Nisa a Siyasa Dashi kuma yake Tsaye da Kafafunsa.

Har wannan Lokacin Mastur bai san Sagir na Neman Auran Diza ba yasan dai Zawara sun mata Chaa,Tunda sun Taba mganar da Daddy bai maida kai ba Tunda Daddy da kanshi ya sanar dashi Diza bata bama kowa Fuska kuma Shi bazai Takura mata ba,Dayake yanzu yakan Dade bai zo gida ba,Saboda yanayin aiki Daya musu yawa in kuma yazo kwana Daya yake yi,ko Biyu ya juya kuma koda yazon Wani Lokacin in yaje ya Dauko Mansur karami Gida yake Dawowa Dashi shi da Rumana suyita Hidima Dashi,Sai yamma ko Dare suke maidashi gida wajen Diza Shiyasa Lokacin da Sagir yake zuwa bai sani ba itakuma Rumana ta sani ammh kuma bata yarda Tayi mganar da Mastur Domin batasan me Zata gayamai ba.
Chapter 80 · 0% Book details