Sashe 10
Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bayan Shigarsa Mansur Cin Biskit Dinsa ya hau yi yana Wasansa da Tsirensa da Hajja ta Raba Ta bashi nashi Ta Diban ma Aiya nata Sai na Mastur Data ijiye mai Da safe,Baba Damsn bazai ci ba nasu ne ya siyo musu,Sai ita Hajja Data Diba nata Tana ci su kuma su Baba suna ta Hira da Ayyai itama Tana cin nata Tsiran suna Hiran yadda anguwan ta Cika Sosai ba kamar Dawowarsu ba,Baba yace"Ai anguwan ta cika Fiye da Zaton ki ayya..Kinga Duk Yawancin Gina ginan da muka samu anayi duk an tare..Bayan Chan gabanmu ma ana ta Saida Filaye ana gini.."Hajja tace"Sosai Nima na gani Dazu da muka je Barka Gidan Maman Anas nida Balaraba Naga ma wannan Katon Gidan Dake Jikin namu Ana ta kawo kaya acikin Kwalaye ma"aikata nata Shiga Dasu Ciki.."
Baba yace"Eh Nima yanzu da muka Fito Masallaci da Usmanu yake Fadamin Megidan zasu Tare Cikin Satinan Dayake anan Anguwan mukayi sallar Isha"i Bayan mun taso Daga kasuwa.."Ayya tace"Dankari wai ni wannan katon Gidan Benen nan na waye ne Habibu..?
Tafada Tana Daga kai tana kare ma Gidan kallo Domin yana kusa Dasu suna ganinsa Dayake Ginin Harda Bene Kerarran Gida ne kamar a kasar Turai san da suka Dawo garin ake Gina Gidan sai kwananan aka gamashi kai Dagaji kasan an kashe Dukiya.
Baba yace"Wlh Aiya ban sani ba Naji dai Usman na Fadin Gidan Mai Kamfanin Saida Motocin nan ne na Bakin Titi..TURETA AND SONS MOTORS LIMITED.."
Aiya ta Zaro ido Tana Fadin"Badai Dankakaren wajen Saida Motocin nan Dake Bakin Titi ba wanda ke Hajara kika Nuna min kwanaki da Zamu asibiti gaida Balaraba sanda tayi Barin din nan.."Hajja Tace"Ina ga nan ne Aiya.."Baba yace"Nan fa To shine megidan Ance Dan Sokoto ne a karamar Hukumar Tureta Dake Sokoto,Yana da kudi sosai yana Saida Motoci ne ance ya Fara zama asokoto ya Dawo kaduna Shi da Iyalansa toh bayan ya Gina wannan wajen saida Motocin ne yanzu yayi gina kusa da wajen yana so su Dawo nan gabadaya da Zama shi da Iyalansa..kuma abun Farincikin ma Masallacin nan Dake Jikin Gidansa da aka Ginashi muna cewa ko Gwannati ne an ce Duka nashi ne.."Aiya Ta gyada kai Tana Fadin"Allah sarki..Abun Duniya baya Boyuwa Duk a ina ka samu wannan Labarin Habibu.."Bashi kadai ba Hatta Hajja sai da tayi Dariya kai ya Girgiza sanin Halin Aiya da Tambayan Kaka uwarka ta kawo ka Duniya yace"Nima Dazu nake ji Da muka Fito masallacin Usman da Baban Anas makocinsa naji suna Hirar kinji inda naji Labarin.."
Aiya Tace"Au..Koda naji..Allah yasa to makotan arziki ne..Kuma Allah yasa kada bayan sun Tare acikin Gidanan Benen nan In yaji Mutane ya Fado mana acikin Agidan ba.."Baba na Dariya Hajja na Tayashi Kafin su Tsaigata Aiya Taji Haushi tace"Ai toh..Gani nayi abun asama haka.."Baba yace"Bazai Taba Fadowa ba Aiya ki kwantar da Hankalinki.."Mikewa Tayi Tana Fadin"Ai Shikenan..Kunga sai da Safenku..Ke Hajara ga Da'nki nan Shi bai yi Karatun ba ya gama cin Biskit yayi barci.."Daga haka ta Shiga Dakinta Baba ya Bita da addu"an Allah ya Tashe su lafiya.
Suma nan Hiran ya Tashi Hajja ta Dauki Mansur ta kai shi Dakinsu ta samu Har Mastur ya gama Karatunsa yayi Barci ta kwantar da Mansur nan gefensa ta Tofa musu addu"an barci kana ta gyara musu Labule bayan Ta kashe musu Hasken Dakin Ba Sauro Dayake tun Gabatowar mangariba ta saka Mastur ya yayyafa Fiya Fiya acikin Duka Dakunan.
Baba ya Shiga Daki Hajja ta Nannade Tabarman ta Shiga Dashi Dakin da Aiya ke kwanciya ta ijiye ta Sameta Tana Shirin kwamciya ta mata sai da Safe ta Fito Daman Kofar Gidan Tun Shigowarsa ya saka ma Gidan Sakata bata Shiga Ciki ba sai da ta gama Duka kaye kayenta a tsakar gida kana tayi alwala ta Shiga.
Baba har ya kwanta Saboda gajiya itama sai ta Shimfida sallaya ta tada salla Shafa"i da Wututri Tayi kana tazo Tayi Shirin kwanciya Sai alokacin Nepa suka Dauke Wuta sai ta kunna Fitila kadan Saboda bata son Duhu sosai itama Tazo ta kwanta bayan tayi addu"an Barci Tana kallon Habibu Dake jan Minshari Mirmishi Tayi Domin tasan ya gaji Zaninta ta yafamai Daga kafa Zuwa Cikinsa kafin ta kwanta abayansa Tana Sauke Numfaahi Itama nan da nam Barci ya kwasheta.
Washegari kuma ta kama Talata ne Tun Safe tatashi Tayi abunda ya kamata na abunda karyawansu Mastur shi ke Sharan Tsakar gidansu ya kuma Cika mata Botikanta da Ruwa kana yaje yayi wanka yazo ya Tada Mansur yamai wanka Suyi Shirin makarata Tare suke karyawan kana Mastur ya Fito Da Kekensa ya Goya Mansur Zuwa makaranta Iyayansu na Binsu da Allah ya Kiyaye sai sun Fita kana Habibu keyin wanka Shima ya Fita Bakin Sana"Arsa abar Hajja da Aiya acikin Gida suna Debema Juna kewa Duk da Hajja bata barin Aiya Tayi aiki ammh ita bata san Zaman hakanan tana kama mata wasu ayyukan da bazu Gagareta ba.
Bayan Sati da yin wannan mganar Tsakanin Baba da Aiya Da yammah wasu manyan Motoci Tsala Tsala wajen Biyar ta Shiga Gidan Dake kusa dasu,Daga alamun dai masu gidanan ne suka Tare Tunda Sai shiga ake ana Fita,Baba ya Shigo da goro da Minti Bayan ya Dawo yace a Masallaci aka Raba Alhajin Da kansa yazo Salla masallacin ya kuma bada Kwalayen Sweet din aka Raba musu yana gayyatan Kowa da kowa zuwa wajen Walimar Tarewarsa da kuma Taya Yarsa Kwara Daya Da ta cika Shekara 5 aduniya uwa uba da kuma Addu"an Bude Sabon masallacin Daya Gina.
Baba na basu Hajja Labari yana Fadin"Aiya baki ga Alhajin ba wlh..Mai Mutumci da Fara"a sai gaisawa yake da Mutane har dani nan mun gaisa Dashi.."Aiya ta kada kai Tana Fadin"Masha Allah..Allah yasa Makota na gari ne.."Baba yace"Ameen..Ai Usman ke Fadamai Nine ke Zaune Kusa Da Gidansa yace Allah Sarki muka kara gaisawa yana Tambayana Iyalai.."
Hajja Tace"Ilkon Allah..Dama wasu masu kudin ance ba Ruwansu.."Baba ya kada kai yana Fadin"Ai Kowa da irin Tasa Zuciyar Hajara Kudi wawayen Abu ne suna Jefa Mutum ga Halaka.."Aiya tace"Allah ya karemu.."Daganan suka Cigaba Da Hiransu.
Washegari kamar yadda Aka Raba Sweet aka tashi Da Shagalin Walima Abinci kala da kala da ababen Sha Mutane Dadama yan anguwa sun Shiga Mata da Maza ammh Hajja bata Leka ba Ballatana Aiya Domin Har Baba ya Fita bai ce mata komai ba Shiyasa da Balaraba ta Biyo su Tafi tace taje kawai itace ma Tazo da abinci a Takeway da Lemuka Da Naman Kaza,Tana basu Labarin Irin Daular Dake Gidan Tana Fadin abinci gayinan Sai wanda ka Zaba Lemuka da Naman kaji kuwa kamar Banza ita bata ma gane Matar gidan ba Taga dai Manyan Mata da yawa sai dai Taga yarinyar da akayi ma Murna Cika Shekara Biyar Karamar yarinya ce Fara wacce Taci gayu da kayan Alfarma Balaraba na Labari Tana Jin Dadi Da Zata tafi tace Hajja ta Dibi Naman kaza Tace A"a sai tace ta Diban ma su Mansur jin haka yasa ta Diba ganin da yawa Cikin wata Roba mai Murfi Ta Diba Harda Aiya Saboda Tana ciki Tana Barci ne Su kuma su Mansur sun Tafi Islamiya.
Sai da Habibu ya Dawo Hajja ke Fadamai Balaraba ta Biyo mata Su Tafi Wajen Waliman Sai ya dafe kai yana Fadin ya manta bai ce ta Shiga ba ammh Ko Daga Baya su Shiga ita da Aiya su Musu Murna.
Wajen kwana Biyu kafin kafa ta Dauke Baki Duk suka koma Inda Suka Fito a kwana na uku ne da Tarewar ALHAJI SUNUSI TURETA..Ya nemi alfarman Limamin masallacin da su Baba ke salla ya sama mai Amintattun da Zasu kula da masallacin Daya Gina Wanda zai Zama an Fara salla da Ibadu aciki Alhaji Sunusin Tunda suka Dawo anguwan Sallah bata Wucesa in dai yana nan baya Fita bane,Nan da nan kuwa liman din yaji Dadi Karramawan Da Alhaji Sunusi yayi mai yace kada ya Damu Da kansa ya Nada Dalibansa masu Neman Ilimi Domin kula da masallacin Cikin kwana Daya aka Fara Gudanar da Salla Cikin kayattacen Masallacin Dake jikin Gidan Alhaji Sunusin.
Sai Wadanda ke kusa da Masallacin suka koma suna Sallan su anan ciki Harda Baba Habibu da Usman nan suka koma suna Sallah Tunda nan yafi kusa Dasu Shima Alhaji sai ya koma yana Salla masallacin Dake jikin Gidansa wanda ya kuma ya kasance mallakinsa ne.
Mutanen anguwan sun ji Dadin Masallacin ko bakomai ya"yansu ba zasu rika jin Nisan zuwa masallaci ba cikin masu Murnan Harda Baba Habibu ganin Mansur da Mastur suna Kokarin Zuwa masallaci Da sun ji Kiran Sallah Abun yana Burgeshi Dadin masallaci a kusa Dakai kenan Shi Da Rana baya Salla anan Tunda yana kasuwa ammh Isha"i da Asuba nan yake yinta,kowa na yabon Kirki da Dattako na Alhaji Sunusi Domin Bayan Sallar asuba Kafin a watse sai ya gaisa da Duka Mazan Dake masallacin Cikin Fara"a Son Mutane Cikin Lokaci kalilan Mutane suka saba Dashi suke kuma Yabon kyawawan Hallayansa.
Sati Biyu da Fara Amfani da masallacin Alhaji Sunusin ya Roki arziki Don Allah abude wani majalisun karatun Bayan Sallar asuba Asaka Littafi Domin atunartae da Juna Kowa yayi Na"am da wannan Shawaran ana Shawaran wazai Jagoranci majalisin Usman Mijin Balaraba ya Nuna Habibu yana Fadin Tabbas yana da Tarin Ilimin Addini Zai iya Jagorantan Majalisin Baba Habibu bai samu Bakin mgana ba Alhaji Sunusi ya Fara mai Godiya Tare da Rokonsa Don Allah kada yace A"a Bashi da yarda Zai yi ya amince bayan an yi Shawara an Tsaida Littafin da Za"a Fara mafi Rinjiye akace a Fara da Karatun Ahalari Yau in ayinshi Gobe sai atabo Tauhidi da Qur"ani Da wannan Shawaran aka Tsaya Baba ya koma Gida yana gaya ma su Aiya suka Bisa da Fatan Alheri.
Baba yace"Eh Nima yanzu da muka Fito Masallaci da Usmanu yake Fadamin Megidan zasu Tare Cikin Satinan Dayake anan Anguwan mukayi sallar Isha"i Bayan mun taso Daga kasuwa.."Ayya tace"Dankari wai ni wannan katon Gidan Benen nan na waye ne Habibu..?
Tafada Tana Daga kai tana kare ma Gidan kallo Domin yana kusa Dasu suna ganinsa Dayake Ginin Harda Bene Kerarran Gida ne kamar a kasar Turai san da suka Dawo garin ake Gina Gidan sai kwananan aka gamashi kai Dagaji kasan an kashe Dukiya.
Baba yace"Wlh Aiya ban sani ba Naji dai Usman na Fadin Gidan Mai Kamfanin Saida Motocin nan ne na Bakin Titi..TURETA AND SONS MOTORS LIMITED.."
Aiya ta Zaro ido Tana Fadin"Badai Dankakaren wajen Saida Motocin nan Dake Bakin Titi ba wanda ke Hajara kika Nuna min kwanaki da Zamu asibiti gaida Balaraba sanda tayi Barin din nan.."Hajja Tace"Ina ga nan ne Aiya.."Baba yace"Nan fa To shine megidan Ance Dan Sokoto ne a karamar Hukumar Tureta Dake Sokoto,Yana da kudi sosai yana Saida Motoci ne ance ya Fara zama asokoto ya Dawo kaduna Shi da Iyalansa toh bayan ya Gina wannan wajen saida Motocin ne yanzu yayi gina kusa da wajen yana so su Dawo nan gabadaya da Zama shi da Iyalansa..kuma abun Farincikin ma Masallacin nan Dake Jikin Gidansa da aka Ginashi muna cewa ko Gwannati ne an ce Duka nashi ne.."Aiya Ta gyada kai Tana Fadin"Allah sarki..Abun Duniya baya Boyuwa Duk a ina ka samu wannan Labarin Habibu.."Bashi kadai ba Hatta Hajja sai da tayi Dariya kai ya Girgiza sanin Halin Aiya da Tambayan Kaka uwarka ta kawo ka Duniya yace"Nima Dazu nake ji Da muka Fito masallacin Usman da Baban Anas makocinsa naji suna Hirar kinji inda naji Labarin.."
Aiya Tace"Au..Koda naji..Allah yasa to makotan arziki ne..Kuma Allah yasa kada bayan sun Tare acikin Gidanan Benen nan In yaji Mutane ya Fado mana acikin Agidan ba.."Baba na Dariya Hajja na Tayashi Kafin su Tsaigata Aiya Taji Haushi tace"Ai toh..Gani nayi abun asama haka.."Baba yace"Bazai Taba Fadowa ba Aiya ki kwantar da Hankalinki.."Mikewa Tayi Tana Fadin"Ai Shikenan..Kunga sai da Safenku..Ke Hajara ga Da'nki nan Shi bai yi Karatun ba ya gama cin Biskit yayi barci.."Daga haka ta Shiga Dakinta Baba ya Bita da addu"an Allah ya Tashe su lafiya.
Suma nan Hiran ya Tashi Hajja ta Dauki Mansur ta kai shi Dakinsu ta samu Har Mastur ya gama Karatunsa yayi Barci ta kwantar da Mansur nan gefensa ta Tofa musu addu"an barci kana ta gyara musu Labule bayan Ta kashe musu Hasken Dakin Ba Sauro Dayake tun Gabatowar mangariba ta saka Mastur ya yayyafa Fiya Fiya acikin Duka Dakunan.
Baba ya Shiga Daki Hajja ta Nannade Tabarman ta Shiga Dashi Dakin da Aiya ke kwanciya ta ijiye ta Sameta Tana Shirin kwamciya ta mata sai da Safe ta Fito Daman Kofar Gidan Tun Shigowarsa ya saka ma Gidan Sakata bata Shiga Ciki ba sai da ta gama Duka kaye kayenta a tsakar gida kana tayi alwala ta Shiga.
Baba har ya kwanta Saboda gajiya itama sai ta Shimfida sallaya ta tada salla Shafa"i da Wututri Tayi kana tazo Tayi Shirin kwanciya Sai alokacin Nepa suka Dauke Wuta sai ta kunna Fitila kadan Saboda bata son Duhu sosai itama Tazo ta kwanta bayan tayi addu"an Barci Tana kallon Habibu Dake jan Minshari Mirmishi Tayi Domin tasan ya gaji Zaninta ta yafamai Daga kafa Zuwa Cikinsa kafin ta kwanta abayansa Tana Sauke Numfaahi Itama nan da nam Barci ya kwasheta.
Washegari kuma ta kama Talata ne Tun Safe tatashi Tayi abunda ya kamata na abunda karyawansu Mastur shi ke Sharan Tsakar gidansu ya kuma Cika mata Botikanta da Ruwa kana yaje yayi wanka yazo ya Tada Mansur yamai wanka Suyi Shirin makarata Tare suke karyawan kana Mastur ya Fito Da Kekensa ya Goya Mansur Zuwa makaranta Iyayansu na Binsu da Allah ya Kiyaye sai sun Fita kana Habibu keyin wanka Shima ya Fita Bakin Sana"Arsa abar Hajja da Aiya acikin Gida suna Debema Juna kewa Duk da Hajja bata barin Aiya Tayi aiki ammh ita bata san Zaman hakanan tana kama mata wasu ayyukan da bazu Gagareta ba.
Bayan Sati da yin wannan mganar Tsakanin Baba da Aiya Da yammah wasu manyan Motoci Tsala Tsala wajen Biyar ta Shiga Gidan Dake kusa dasu,Daga alamun dai masu gidanan ne suka Tare Tunda Sai shiga ake ana Fita,Baba ya Shigo da goro da Minti Bayan ya Dawo yace a Masallaci aka Raba Alhajin Da kansa yazo Salla masallacin ya kuma bada Kwalayen Sweet din aka Raba musu yana gayyatan Kowa da kowa zuwa wajen Walimar Tarewarsa da kuma Taya Yarsa Kwara Daya Da ta cika Shekara 5 aduniya uwa uba da kuma Addu"an Bude Sabon masallacin Daya Gina.
Baba na basu Hajja Labari yana Fadin"Aiya baki ga Alhajin ba wlh..Mai Mutumci da Fara"a sai gaisawa yake da Mutane har dani nan mun gaisa Dashi.."Aiya ta kada kai Tana Fadin"Masha Allah..Allah yasa Makota na gari ne.."Baba yace"Ameen..Ai Usman ke Fadamai Nine ke Zaune Kusa Da Gidansa yace Allah Sarki muka kara gaisawa yana Tambayana Iyalai.."
Hajja Tace"Ilkon Allah..Dama wasu masu kudin ance ba Ruwansu.."Baba ya kada kai yana Fadin"Ai Kowa da irin Tasa Zuciyar Hajara Kudi wawayen Abu ne suna Jefa Mutum ga Halaka.."Aiya tace"Allah ya karemu.."Daganan suka Cigaba Da Hiransu.
Washegari kamar yadda Aka Raba Sweet aka tashi Da Shagalin Walima Abinci kala da kala da ababen Sha Mutane Dadama yan anguwa sun Shiga Mata da Maza ammh Hajja bata Leka ba Ballatana Aiya Domin Har Baba ya Fita bai ce mata komai ba Shiyasa da Balaraba ta Biyo su Tafi tace taje kawai itace ma Tazo da abinci a Takeway da Lemuka Da Naman Kaza,Tana basu Labarin Irin Daular Dake Gidan Tana Fadin abinci gayinan Sai wanda ka Zaba Lemuka da Naman kaji kuwa kamar Banza ita bata ma gane Matar gidan ba Taga dai Manyan Mata da yawa sai dai Taga yarinyar da akayi ma Murna Cika Shekara Biyar Karamar yarinya ce Fara wacce Taci gayu da kayan Alfarma Balaraba na Labari Tana Jin Dadi Da Zata tafi tace Hajja ta Dibi Naman kaza Tace A"a sai tace ta Diban ma su Mansur jin haka yasa ta Diba ganin da yawa Cikin wata Roba mai Murfi Ta Diba Harda Aiya Saboda Tana ciki Tana Barci ne Su kuma su Mansur sun Tafi Islamiya.
Sai da Habibu ya Dawo Hajja ke Fadamai Balaraba ta Biyo mata Su Tafi Wajen Waliman Sai ya dafe kai yana Fadin ya manta bai ce ta Shiga ba ammh Ko Daga Baya su Shiga ita da Aiya su Musu Murna.
Wajen kwana Biyu kafin kafa ta Dauke Baki Duk suka koma Inda Suka Fito a kwana na uku ne da Tarewar ALHAJI SUNUSI TURETA..Ya nemi alfarman Limamin masallacin da su Baba ke salla ya sama mai Amintattun da Zasu kula da masallacin Daya Gina Wanda zai Zama an Fara salla da Ibadu aciki Alhaji Sunusin Tunda suka Dawo anguwan Sallah bata Wucesa in dai yana nan baya Fita bane,Nan da nan kuwa liman din yaji Dadi Karramawan Da Alhaji Sunusi yayi mai yace kada ya Damu Da kansa ya Nada Dalibansa masu Neman Ilimi Domin kula da masallacin Cikin kwana Daya aka Fara Gudanar da Salla Cikin kayattacen Masallacin Dake jikin Gidan Alhaji Sunusin.
Sai Wadanda ke kusa da Masallacin suka koma suna Sallan su anan ciki Harda Baba Habibu da Usman nan suka koma suna Sallah Tunda nan yafi kusa Dasu Shima Alhaji sai ya koma yana Salla masallacin Dake jikin Gidansa wanda ya kuma ya kasance mallakinsa ne.
Mutanen anguwan sun ji Dadin Masallacin ko bakomai ya"yansu ba zasu rika jin Nisan zuwa masallaci ba cikin masu Murnan Harda Baba Habibu ganin Mansur da Mastur suna Kokarin Zuwa masallaci Da sun ji Kiran Sallah Abun yana Burgeshi Dadin masallaci a kusa Dakai kenan Shi Da Rana baya Salla anan Tunda yana kasuwa ammh Isha"i da Asuba nan yake yinta,kowa na yabon Kirki da Dattako na Alhaji Sunusi Domin Bayan Sallar asuba Kafin a watse sai ya gaisa da Duka Mazan Dake masallacin Cikin Fara"a Son Mutane Cikin Lokaci kalilan Mutane suka saba Dashi suke kuma Yabon kyawawan Hallayansa.
Sati Biyu da Fara Amfani da masallacin Alhaji Sunusin ya Roki arziki Don Allah abude wani majalisun karatun Bayan Sallar asuba Asaka Littafi Domin atunartae da Juna Kowa yayi Na"am da wannan Shawaran ana Shawaran wazai Jagoranci majalisin Usman Mijin Balaraba ya Nuna Habibu yana Fadin Tabbas yana da Tarin Ilimin Addini Zai iya Jagorantan Majalisin Baba Habibu bai samu Bakin mgana ba Alhaji Sunusi ya Fara mai Godiya Tare da Rokonsa Don Allah kada yace A"a Bashi da yarda Zai yi ya amince bayan an yi Shawara an Tsaida Littafin da Za"a Fara mafi Rinjiye akace a Fara da Karatun Ahalari Yau in ayinshi Gobe sai atabo Tauhidi da Qur"ani Da wannan Shawaran aka Tsaya Baba ya koma Gida yana gaya ma su Aiya suka Bisa da Fatan Alheri.