Sashe 27
Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai da ta Tsaya akofar Dakin Tayi Sallama Cikin Siririyar Muryanta Lokaci Daya Taji Kafafunta na Rawa Lokacin Dataji Muryansa yana Fadin Ashigo Cikin Karfin Hali da Jarumta Ta saka Hannu Ta Tura Kofar ta Shiga Cikin Dakin tana karayin Wata Sallaman.
Kansa na Kasa yana ta aiki Bisa System dinsa atsakiyar gadonsa Tun Datayi sallaman Farko Yaji Muryantq ya Shaidata Ko Mutuwa yayi ya Dawo zai iya Shaida Muryan Dizan Daya gama Tantaceta Tun Shekarun Baya,lokacon Data Shigo Cikin Dakin Bai yi Saurin Dagoewa ba Duk da Yadda Zuciyarsa Tayi Tsalle Waje Daya Saboda Murna ganinta sai ya basar ya Dago kansa a Hankali yayi mata kallo Daya ya kauda kai Bayan ya amsa Sallamanta.
Lokacin Daya kalleta kamar TaKafafunta Zasu kadata Saboda wani irin yam Dataji ya Tsirgamata Tundaga Kafarta Har saman kanta Dakyar ta iya Zare Takalmin Kafarta Ta Fara Taku Har Cikin Dakin Gefen Gadon Ta samu matsunguuni Ta Dofana Duwawunta Tana Gaisheshi ya amsa batare daya Dago ba,Sai da Tagama gaishesa ya Dago yana kallonta Kasa kasa ganin Ta wani Zauna kamar Ana Koranta kuma ta wani Sunkuyar Dakai yana mamakin Yadda yarinyar take mai Girman kai ko don Yana mata Fada ne in tayi ba Dadai ba Ko kuma Saboda Baya musu wasa Tun Baya Daga ita Har Mansur din.
Cikin Dakakkiyar Muryansa yace"Ki zauna Dakyau mana.."Jin Abunda yace ne yasa ta Dan gyara Zamanta Taa Dan Muskuta Tana Fadin"Mommy Tace tana gaisheka..Kuma wai Tana nan Tana Jiranka batayi Fushi ba.."Kamar bazai Tankata ba Sai da ta Saci kallonsa Taga yana Dan Mirmishin nan nashi mai Tsada Chan Taji muryansa Cikin Kasaita yace"Zan shiga anjuma in Daddy ya Dawo.."Daga haka bai kara mgana ba itama Sai ta Dauke kanta Kamar bata kallonsa Tana ta wasa da wayarta Dake Hannunta.
Shuru na wani Lokaci ita Tana Zaune kanta a kasa Bata kara mgana ba ammh Zamansu a waje Daya yana kara Sakata Cikin Natsuwa bataki su Dauwama ahaka ba Har Abada ba,Shi kuma yana auna Yadda Dizan ta koma ne yanzu yana mamakin Inya gansu Tare da Mansur Wani bayama wani Fada ammh In suka Hadu kamar Salaha take komamai Sai yake Danganta Haka da Girman kai takemai ko kuma wani Shariyace bai sani ba..
Wayarta ake ta Kira Tana kin Dagawa yana jinta karan Wayarce ta Dameshi Da wani Zafin Zuciya yana Tunanin kada ace wani Namiji ke kiranta Cikin Muryansa Ta Dakiya yace"Ki Daga wannan wayar taki..Kararta na Damuna..".
Da sauri tace"Hauwa ce ke kirana..Wacce ke taimakamin Bangaran Office dina na Makeup.."Bai kara mgana ba ya Dai kalleta ta gefen ido Ganin Ta Daga Kiran Tana Fadin"Ya akayi ne Hauwa..?
Baisan me ake ce mata ba Daga Karshe dai tace"Hauwa kiyi ma wadanda sukayi Bukking na Gobe..Kuma ina Gayamiki bana sin zari..Kada ki Cikamana Mutane Mutane Goma sun isa in kuma kika Cika Wlh ke zan bari da aiki Am Telling u.."Dagachan Bangaran Hauwa na Dariya tace"Bakomai Madam.."Daga haka ta yanke Kiran Duk yana Jinta ita kuma Sai Ta gama wayar ta gano Laifinta da Sauri Tace"Kayi Hakuri..Zan yi waya ban Fita ba Allah sa Hayaniyata bai Dameka ba..'
Bai tankata ba Har ta Cire rai Sai Taji yace"Kin fi jin Dadin wannan Sana"ar taki da Cigaban Karatunki Khadija..?
Yafada yana Kafeta da Idanuwansa masu Firgitata da Sauri ta Sadda kai ta kasa Mgana Ba Tun yau ba yasha mata mganar Cigaban Karatunta Dama Dama ace Zata iya Karatun Datayi Saboda Cikama Mastur Burinsa Sai Dai kuma Bazata iya Juran Wahalhaun Karatun ba kuma Ba Ra"ayinta bane yin Karatu bai Zurfi Hakan tafi jin Dadin Rayuwarta So Simple.
Ganin ta kasa Mgana yasa ya kada kai yana Fadin"Is ok..Tashi kije..Tunda haka kika zaban ma kanki..Ammh ki Sani akwai Watarana da Zatazo kina son Kiyi Karatun..Ammh kuma Lokaci ya Riga ya Kure Miki.."Yafada yana Jin wani Takaichi acikin Ransa Kamar akan kaya take ta Mike da Sauri Ta Juya ta Fara taku Zata Fita yayi Galala yana Binta da kallon Soyayyah Muradi Sha"awa da Kauna Ta Har abada Sai gaahi ta waigo Sun Hada ido Irin kallon Dataga yana mata yasa ta Saka takalminta da Sauri ta Fice Ta Rufomai Kofan tana Sauke Numfashi Dakyar ta iya Jan Kafa ta Fice Daga Shashen Saboda Halin Datake Ciki Ko Shashen su Hajja bata koma ba ta Fice Daga Gidan Zuwa Gida Gabadaya Soyayyar Mastur Data Binneta acikin Ranta Taji Tana ta Fitowa Daya Bayan Daya,Har ta Shiga Cikin gida Jikinta bai bar Rawa ba Dakinta Ta Fada ta Rufo Kofa Ta Dire kan gado Tana Haki kafim Lokaci Daya kuma wasu Hawaye suka Fara Zubomata kanta Ta Dafe Tana Fadin"Ya zan yi ya gane ina Matukar Sonsa..?me zan yi Nima ya Soni Kamar yadda Nake sonsa..?
Haka take ta Fada kafin ta Sulale kan gadon ta Fashe da wani marayan kuka wanda yake Fitowa Daga Karkashin Zuciyarta.
Shikuwa abagaran Mastur yayi kokarin Zama Namijin Duniya Bayan Fitan Diza bakinsa ya Cija yana Kada kai Har sai yaushe ne zai iya gayamata Yana Sonta..? Watarana ne zai gayamata Ya Fara sonta ne Tun bata mallaki Hankalin kanta ba..? WaniDare zai Tabbata Dare mai Albarka da Tarihi a garesu..?shima bai sani ba ammh Tabbas in ya Cigaba da Zama ahaka yarinyar Zata kasheshi Lokacinsa bai yi ba.
Sai dakyar ya iya yakice Tunaninta ya Cigaba da aikinsa Har Mansur ya Dawo Dole ya Ijiye aikin ya Cigaba da yima Mansur din Fada da lallashi yana kara Nunamai Muhimmancin Iyaye da kuma yan'uwa Har Mansur din ya gamsu yace mai insha Allahu Hakan bazata kara Faruwa ba,Da haka suka Cigaba da Hiransu Rabin Hiran Duk Mansur ne yana Bashi Labarin Siyarsu da Halin da ake Ciki Sjidai yana jinsu wani wajen yayi Mirmishi wani wajen kuma Dayaga yana da ta cewa sai ya Tofa albaarkacin Bakinsa Har aka Kira Sallar mangariba suka Fita Zuwa masallaci Mastur bai bari sun Dawo ba sai da suka Tsaya akayi Sallar Isha"i wanda Tare da Daddy da Baba Habibu akayi ta Sai Bayan an Idar da Sallan ne suka ga Mastur wanda ya Duka yana Gaishesu Daddy ya amsa Cikin Farinciki ya Dagosa yana Shafa kansa Basu Tsaya wata mgana ba Su Mansur da Baba Habibu suka Nufi Gida Bayan Mastur din yace Zai Shigo kafin ya kwanta.
Suna komawa suka Hadu anan Falon Hajja,Baba Habibu nata Tambayan Mastur wajen aikinsa yana amasa mai,shi kuma Mansur yana Kitchen Wajen Hajja sai gasu sun kawo Abinci Shinkafa da Miya da Salat,Sai Tuwon da Mastur yace a Dumamai Shi zai ce,Baba Habibu na gani yacr Hajja Tayi Sonkai Shima Tuwon yake so Mastur yace Bari ya wanko Hannu sai suji Tare Mansur na jin Haka yace Shima Dashi Za"aci,Haka kuwa akayi su uku suka Taru suna ci Tuwon Cikin Farinciki Bayan sun gama ne Mansur da Baba Habibu suka Kara da Shinkafa Shi kuma Mastur yana gefe yace ya Koshi Yaje Kitchen ya wanko Hannu yazo ya zauna yana Kallon Baba Habibu ganin haka yasa ya gyara Zama yana Fadin"Babban Mutum ya akayi ne..?
Mastur yace"Baba kan mganar Zuwa Maruka Duba Baba Sule..Gobe zamu Tafi da Mansur in Zaka samu zuwa sai mu Tafi Tare ."Baba Habibu yace"Ba Mtsala Allah ya kaimu..Kayi Tunani kwarai kuma ina Fatan kayi mai Fadan Sakacin da yake yi da Iyayansa da yan"uwansa."Mastur ya gyada kai yana Fadin"Namai Fada Baba.."Mansur ya Tura Baki yana Fadin"Ni wai Baba sai kayi ta cewa amin Fada.."Aiya Dake gefe tace"Kana jin mgana ne..? Tun kana yaronka kake Laifi.."Hararanta Yayi yana Fadin"Kefa Daman yar saka Ido ne Aiyan nan.."Yafada yana wani Mele mata baki Ta Jefeshi da Murfin kula Tana Fadin"Kada kamin Rashin kunya..Ga megidana akusa in saka ya sakayamin kai.."Dariya ta kama su Baba Habibu Mastur ma sai da ya Murmusa.
Hajja ce ta kalli Baba Habibu Tana Fadin"Kaji ashe ya karime ta Kira Babban Mutum..? Baba Habibu Dake sakacen Hakori ya Kalleta yana Fadin"Topha..Me tace mai..?kardai kan mganar Busharan ne..?
Hajja na kallon Mastur tace"Bansani bai gayamin komai ba ammh ina Zaton akanta ne.."Baba Habibu zai yi mgana Mansur yace"Wata Busharan kuma Hajja..?Kafin suyi mgana Aiya tayi karaf Tace"Busharan Karime mana..Wai Saboda Shirmenta Taga Megidana ya zama Ubansu Take so ta Hadashi da Bushara yarta.."Mansur ya waro ido Yana Fadin"Wai ya tafi da ita Porthercourt tayi mai aiki..?
Dariya Ta kama Mastur Sai da ya Murmusa Allah ya Shiryi Mansur Baba Habibu ne yamai Dakuwa yana Fadin"Kaga naka nan Mansur..Ko Zai dauki yar aiki mai Zai Hadasa da Daukan mace Kuma ma yar"uwansa.."Mansur yace"Ah Baba in ba yar aiki ba Bushara fa..!wlh a yar aikin ma xai Taimaka mata ne.."Aiya Tace"Kai Sakarai waye yace maka yar aiki ce..? Wai fa ya Aureta..?
Mansur ya Zaro Ido Kamar yaji Mugun Abu yace"Au...? Na shiga Uku ni Mansur Sulaiman Doguwa..Ammh Inna karime Ta Gama da Ya Mastur wannan Bakauyan yarinya Kazama da wani katon Bakinta kamar Dankalin Kasa ne Zata Auri Yayana Son kowa kin Yarinyar Data Rasa..? chab wlh da Sake wannan ma Allah Yaya in ya kalleta ayyada yake zai iya yin amai.."Hajja ce Dake kusa Dashi Ta Sakarmai Dundu Tana Fadin"Zan ci Mutumcinka fa Mansur.."Yana Dariya ya Tashi Da Gudu Zuwa Bayan Mastur yana Fadin"Wlh Yaya kada ka yarda..Uhm.Wlh ka yarda ka Aurta achan Wajen aiki Sai an Daina ganin Girmanka.."Hajja ta Sake Dakamai Tsawa Aiya tace"Ke Hajara ki kyaleshi mana..Karya ya Fada..? Kamar yadda Karime take yaya gareki Ni Uwa nake gareta ammh fa Bana Goyon bayan Karya da Cuta Kin gani nan."
Mansur ya Daga mata Hannu yana Fadin"Yauwa Aiya..Ko kefa..Zan yi meneji Dake in na zama gwamna ko Shugaban Tsoffin mata na baki.."Baki ta Washe Tana Fadin"Haba Honorobul ko dai Mukamin Fisladi din.."Gabadaya Su Baba Habibu suka saka Dariya Mansur Har yana Tuntsirawa Ya Dago yana Fadin"Aiya bafa Honorobul ba Honourble akace..Ba kuma Fisladi ba Firstlady akace mtsalan ba Turanci.."Mastur ne ya Murdemai kunni yana Fadin"Baakajin mgana ko..? Ihu ya Fara yana Fadin"Na bari Yaya kunnina..Srry.."sakinsa yayi yana Mirmishi Aiya kuma Rai Ta Bata Tana Fadin"Koma miye..dai nadai Fada Daidai ehe..Dakace cewa ba Turanci kafi ni iya Fada ne..?
Mastur ne yace"Bai fi ki ba Aiyata..'Baki ta Washe Tana Fadin"Yauwa Megidana na kaina.."Baba Habibu ne yayi gyaran Murya yana Fadin"Babban Mutum me kace game da mganar Kariman..? Abunda ka yanke Shine Daidai Tunda Kaine keda Wuka Da Nama..?
Kansa na Kasa yana ta aiki Bisa System dinsa atsakiyar gadonsa Tun Datayi sallaman Farko Yaji Muryantq ya Shaidata Ko Mutuwa yayi ya Dawo zai iya Shaida Muryan Dizan Daya gama Tantaceta Tun Shekarun Baya,lokacon Data Shigo Cikin Dakin Bai yi Saurin Dagoewa ba Duk da Yadda Zuciyarsa Tayi Tsalle Waje Daya Saboda Murna ganinta sai ya basar ya Dago kansa a Hankali yayi mata kallo Daya ya kauda kai Bayan ya amsa Sallamanta.
Lokacin Daya kalleta kamar TaKafafunta Zasu kadata Saboda wani irin yam Dataji ya Tsirgamata Tundaga Kafarta Har saman kanta Dakyar ta iya Zare Takalmin Kafarta Ta Fara Taku Har Cikin Dakin Gefen Gadon Ta samu matsunguuni Ta Dofana Duwawunta Tana Gaisheshi ya amsa batare daya Dago ba,Sai da Tagama gaishesa ya Dago yana kallonta Kasa kasa ganin Ta wani Zauna kamar Ana Koranta kuma ta wani Sunkuyar Dakai yana mamakin Yadda yarinyar take mai Girman kai ko don Yana mata Fada ne in tayi ba Dadai ba Ko kuma Saboda Baya musu wasa Tun Baya Daga ita Har Mansur din.
Cikin Dakakkiyar Muryansa yace"Ki zauna Dakyau mana.."Jin Abunda yace ne yasa ta Dan gyara Zamanta Taa Dan Muskuta Tana Fadin"Mommy Tace tana gaisheka..Kuma wai Tana nan Tana Jiranka batayi Fushi ba.."Kamar bazai Tankata ba Sai da ta Saci kallonsa Taga yana Dan Mirmishin nan nashi mai Tsada Chan Taji muryansa Cikin Kasaita yace"Zan shiga anjuma in Daddy ya Dawo.."Daga haka bai kara mgana ba itama Sai ta Dauke kanta Kamar bata kallonsa Tana ta wasa da wayarta Dake Hannunta.
Shuru na wani Lokaci ita Tana Zaune kanta a kasa Bata kara mgana ba ammh Zamansu a waje Daya yana kara Sakata Cikin Natsuwa bataki su Dauwama ahaka ba Har Abada ba,Shi kuma yana auna Yadda Dizan ta koma ne yanzu yana mamakin Inya gansu Tare da Mansur Wani bayama wani Fada ammh In suka Hadu kamar Salaha take komamai Sai yake Danganta Haka da Girman kai takemai ko kuma wani Shariyace bai sani ba..
Wayarta ake ta Kira Tana kin Dagawa yana jinta karan Wayarce ta Dameshi Da wani Zafin Zuciya yana Tunanin kada ace wani Namiji ke kiranta Cikin Muryansa Ta Dakiya yace"Ki Daga wannan wayar taki..Kararta na Damuna..".
Da sauri tace"Hauwa ce ke kirana..Wacce ke taimakamin Bangaran Office dina na Makeup.."Bai kara mgana ba ya Dai kalleta ta gefen ido Ganin Ta Daga Kiran Tana Fadin"Ya akayi ne Hauwa..?
Baisan me ake ce mata ba Daga Karshe dai tace"Hauwa kiyi ma wadanda sukayi Bukking na Gobe..Kuma ina Gayamiki bana sin zari..Kada ki Cikamana Mutane Mutane Goma sun isa in kuma kika Cika Wlh ke zan bari da aiki Am Telling u.."Dagachan Bangaran Hauwa na Dariya tace"Bakomai Madam.."Daga haka ta yanke Kiran Duk yana Jinta ita kuma Sai Ta gama wayar ta gano Laifinta da Sauri Tace"Kayi Hakuri..Zan yi waya ban Fita ba Allah sa Hayaniyata bai Dameka ba..'
Bai tankata ba Har ta Cire rai Sai Taji yace"Kin fi jin Dadin wannan Sana"ar taki da Cigaban Karatunki Khadija..?
Yafada yana Kafeta da Idanuwansa masu Firgitata da Sauri ta Sadda kai ta kasa Mgana Ba Tun yau ba yasha mata mganar Cigaban Karatunta Dama Dama ace Zata iya Karatun Datayi Saboda Cikama Mastur Burinsa Sai Dai kuma Bazata iya Juran Wahalhaun Karatun ba kuma Ba Ra"ayinta bane yin Karatu bai Zurfi Hakan tafi jin Dadin Rayuwarta So Simple.
Ganin ta kasa Mgana yasa ya kada kai yana Fadin"Is ok..Tashi kije..Tunda haka kika zaban ma kanki..Ammh ki Sani akwai Watarana da Zatazo kina son Kiyi Karatun..Ammh kuma Lokaci ya Riga ya Kure Miki.."Yafada yana Jin wani Takaichi acikin Ransa Kamar akan kaya take ta Mike da Sauri Ta Juya ta Fara taku Zata Fita yayi Galala yana Binta da kallon Soyayyah Muradi Sha"awa da Kauna Ta Har abada Sai gaahi ta waigo Sun Hada ido Irin kallon Dataga yana mata yasa ta Saka takalminta da Sauri ta Fice Ta Rufomai Kofan tana Sauke Numfashi Dakyar ta iya Jan Kafa ta Fice Daga Shashen Saboda Halin Datake Ciki Ko Shashen su Hajja bata koma ba ta Fice Daga Gidan Zuwa Gida Gabadaya Soyayyar Mastur Data Binneta acikin Ranta Taji Tana ta Fitowa Daya Bayan Daya,Har ta Shiga Cikin gida Jikinta bai bar Rawa ba Dakinta Ta Fada ta Rufo Kofa Ta Dire kan gado Tana Haki kafim Lokaci Daya kuma wasu Hawaye suka Fara Zubomata kanta Ta Dafe Tana Fadin"Ya zan yi ya gane ina Matukar Sonsa..?me zan yi Nima ya Soni Kamar yadda Nake sonsa..?
Haka take ta Fada kafin ta Sulale kan gadon ta Fashe da wani marayan kuka wanda yake Fitowa Daga Karkashin Zuciyarta.
Shikuwa abagaran Mastur yayi kokarin Zama Namijin Duniya Bayan Fitan Diza bakinsa ya Cija yana Kada kai Har sai yaushe ne zai iya gayamata Yana Sonta..? Watarana ne zai gayamata Ya Fara sonta ne Tun bata mallaki Hankalin kanta ba..? WaniDare zai Tabbata Dare mai Albarka da Tarihi a garesu..?shima bai sani ba ammh Tabbas in ya Cigaba da Zama ahaka yarinyar Zata kasheshi Lokacinsa bai yi ba.
Sai dakyar ya iya yakice Tunaninta ya Cigaba da aikinsa Har Mansur ya Dawo Dole ya Ijiye aikin ya Cigaba da yima Mansur din Fada da lallashi yana kara Nunamai Muhimmancin Iyaye da kuma yan'uwa Har Mansur din ya gamsu yace mai insha Allahu Hakan bazata kara Faruwa ba,Da haka suka Cigaba da Hiransu Rabin Hiran Duk Mansur ne yana Bashi Labarin Siyarsu da Halin da ake Ciki Sjidai yana jinsu wani wajen yayi Mirmishi wani wajen kuma Dayaga yana da ta cewa sai ya Tofa albaarkacin Bakinsa Har aka Kira Sallar mangariba suka Fita Zuwa masallaci Mastur bai bari sun Dawo ba sai da suka Tsaya akayi Sallar Isha"i wanda Tare da Daddy da Baba Habibu akayi ta Sai Bayan an Idar da Sallan ne suka ga Mastur wanda ya Duka yana Gaishesu Daddy ya amsa Cikin Farinciki ya Dagosa yana Shafa kansa Basu Tsaya wata mgana ba Su Mansur da Baba Habibu suka Nufi Gida Bayan Mastur din yace Zai Shigo kafin ya kwanta.
Suna komawa suka Hadu anan Falon Hajja,Baba Habibu nata Tambayan Mastur wajen aikinsa yana amasa mai,shi kuma Mansur yana Kitchen Wajen Hajja sai gasu sun kawo Abinci Shinkafa da Miya da Salat,Sai Tuwon da Mastur yace a Dumamai Shi zai ce,Baba Habibu na gani yacr Hajja Tayi Sonkai Shima Tuwon yake so Mastur yace Bari ya wanko Hannu sai suji Tare Mansur na jin Haka yace Shima Dashi Za"aci,Haka kuwa akayi su uku suka Taru suna ci Tuwon Cikin Farinciki Bayan sun gama ne Mansur da Baba Habibu suka Kara da Shinkafa Shi kuma Mastur yana gefe yace ya Koshi Yaje Kitchen ya wanko Hannu yazo ya zauna yana Kallon Baba Habibu ganin haka yasa ya gyara Zama yana Fadin"Babban Mutum ya akayi ne..?
Mastur yace"Baba kan mganar Zuwa Maruka Duba Baba Sule..Gobe zamu Tafi da Mansur in Zaka samu zuwa sai mu Tafi Tare ."Baba Habibu yace"Ba Mtsala Allah ya kaimu..Kayi Tunani kwarai kuma ina Fatan kayi mai Fadan Sakacin da yake yi da Iyayansa da yan"uwansa."Mastur ya gyada kai yana Fadin"Namai Fada Baba.."Mansur ya Tura Baki yana Fadin"Ni wai Baba sai kayi ta cewa amin Fada.."Aiya Dake gefe tace"Kana jin mgana ne..? Tun kana yaronka kake Laifi.."Hararanta Yayi yana Fadin"Kefa Daman yar saka Ido ne Aiyan nan.."Yafada yana wani Mele mata baki Ta Jefeshi da Murfin kula Tana Fadin"Kada kamin Rashin kunya..Ga megidana akusa in saka ya sakayamin kai.."Dariya ta kama su Baba Habibu Mastur ma sai da ya Murmusa.
Hajja ce ta kalli Baba Habibu Tana Fadin"Kaji ashe ya karime ta Kira Babban Mutum..? Baba Habibu Dake sakacen Hakori ya Kalleta yana Fadin"Topha..Me tace mai..?kardai kan mganar Busharan ne..?
Hajja na kallon Mastur tace"Bansani bai gayamin komai ba ammh ina Zaton akanta ne.."Baba Habibu zai yi mgana Mansur yace"Wata Busharan kuma Hajja..?Kafin suyi mgana Aiya tayi karaf Tace"Busharan Karime mana..Wai Saboda Shirmenta Taga Megidana ya zama Ubansu Take so ta Hadashi da Bushara yarta.."Mansur ya waro ido Yana Fadin"Wai ya tafi da ita Porthercourt tayi mai aiki..?
Dariya Ta kama Mastur Sai da ya Murmusa Allah ya Shiryi Mansur Baba Habibu ne yamai Dakuwa yana Fadin"Kaga naka nan Mansur..Ko Zai dauki yar aiki mai Zai Hadasa da Daukan mace Kuma ma yar"uwansa.."Mansur yace"Ah Baba in ba yar aiki ba Bushara fa..!wlh a yar aikin ma xai Taimaka mata ne.."Aiya Tace"Kai Sakarai waye yace maka yar aiki ce..? Wai fa ya Aureta..?
Mansur ya Zaro Ido Kamar yaji Mugun Abu yace"Au...? Na shiga Uku ni Mansur Sulaiman Doguwa..Ammh Inna karime Ta Gama da Ya Mastur wannan Bakauyan yarinya Kazama da wani katon Bakinta kamar Dankalin Kasa ne Zata Auri Yayana Son kowa kin Yarinyar Data Rasa..? chab wlh da Sake wannan ma Allah Yaya in ya kalleta ayyada yake zai iya yin amai.."Hajja ce Dake kusa Dashi Ta Sakarmai Dundu Tana Fadin"Zan ci Mutumcinka fa Mansur.."Yana Dariya ya Tashi Da Gudu Zuwa Bayan Mastur yana Fadin"Wlh Yaya kada ka yarda..Uhm.Wlh ka yarda ka Aurta achan Wajen aiki Sai an Daina ganin Girmanka.."Hajja ta Sake Dakamai Tsawa Aiya tace"Ke Hajara ki kyaleshi mana..Karya ya Fada..? Kamar yadda Karime take yaya gareki Ni Uwa nake gareta ammh fa Bana Goyon bayan Karya da Cuta Kin gani nan."
Mansur ya Daga mata Hannu yana Fadin"Yauwa Aiya..Ko kefa..Zan yi meneji Dake in na zama gwamna ko Shugaban Tsoffin mata na baki.."Baki ta Washe Tana Fadin"Haba Honorobul ko dai Mukamin Fisladi din.."Gabadaya Su Baba Habibu suka saka Dariya Mansur Har yana Tuntsirawa Ya Dago yana Fadin"Aiya bafa Honorobul ba Honourble akace..Ba kuma Fisladi ba Firstlady akace mtsalan ba Turanci.."Mastur ne ya Murdemai kunni yana Fadin"Baakajin mgana ko..? Ihu ya Fara yana Fadin"Na bari Yaya kunnina..Srry.."sakinsa yayi yana Mirmishi Aiya kuma Rai Ta Bata Tana Fadin"Koma miye..dai nadai Fada Daidai ehe..Dakace cewa ba Turanci kafi ni iya Fada ne..?
Mastur ne yace"Bai fi ki ba Aiyata..'Baki ta Washe Tana Fadin"Yauwa Megidana na kaina.."Baba Habibu ne yayi gyaran Murya yana Fadin"Babban Mutum me kace game da mganar Kariman..? Abunda ka yanke Shine Daidai Tunda Kaine keda Wuka Da Nama..?