← Book details Sadaukarwa So Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 68 OF 94

Sashe 68

Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hulansa ta Daukomai kalan Sararin Samaniya wacce ta Dace da kalan Shaddan Jikinsa Dake maiko da yarari ta aza mai Bisa kansa Bayan tayi Dage da Turtstsen Cikinta Daya Fito Sosai Turare ta Dauko ta Shiga Fesamai Tana kauda kai Lokaci Daya bata so Su Hada ido Dashi.
Kugunta ya Riko Lokaci Daya da Hannunwanta Yana so su Hada ya Kalli Fuskarta ammh sai ta kawar da kanta ganin Haka yasa ya Rumgumota gabadaya acikin Jikinsa yana Fadin"Haba Firstlady dita Duk Fushin ne na Kada na tafi na barki yasa kika kasa Hada ido dani..?
Tura Baki Tayi Lokaci Daya taji wani Rauni ya Shigeta Ta Dago Tana kallonsa a raunane tace"Nidai kada Fita Yau don Allah.."Abun nata sai yaso bashi Dariya ya Dafa kafadunta Duka Biyu yana Fadin"Meyasa yau kika Chanza Dizata..? Na saba Fita Har Tafiye Tafiye ma ammh baki Taba cemim kada na Fita ba sai yau..?Umh gayamin meke Damunki ne...?
Yafada Lokaci Daya yana Saka Hannunsa Guda Daya ya Dago Habarta Dashi kamar al"amara sai ga Hawaye Sharr Cikin Tsoro ya tsaya yana kallonta kafin yace"Subhanallah Diza..meyake Faruwa ne..? Cikin kuka Diza Ta Fada Jikinsa Tana Fadin"nidai Kawai ka Fasa Tafiya kadunan nan.Haka kurun nake ji araina in ka Tafi kamar bazan sake ganin ka ba..!ta karishe Fada Cikin gunjin kuka.
Kalamanta sun sakashi yaji wani Farinciki da karin Kaunarta bai Dagota ba sai ma Dukan Bayanta Dayake Cikin alamun Lallashi.
Sai da yaji ta samu natsuwa kana ya Dagota yana Share mata Hawaye Lokaci Daya yana Fadin"in jiwa yace in na Tafi bazan Dawo ba ehe..? Insha Allahu zam Dawo Gareki Firstladyta.."Yafada yana mai kura mata ido Cikin wani yanayi da kauna da Muradi mai Girma.
Kwalkwal Diza Tayi kafin tace"Nidai naji..Ammh kafasa Tafiyan nan Don Allah."Kansa ya Dafe kafin yace"Bazai yuyu na Fasa ba Diza..Taron na gwanna nefa..In ban je ba akwai mtsala yanzu haka nasan yan Tawagata suna nm....! Kir...kir...kir..!
Kiran wayarsa ya Katsesa da Mgana da Sauri ya Dauketa Tunda Cikin aljihunsa Take ganin mai kiran Sagir ne P.A Dinsa Da Sauri ya Daga,Shuru yayi bai yi mgana sai chan yace"Kuna wajen get din ne..? Sai chan kuma yace"Shikenangani nan Fitowa..!
Daga Haka ya yanke kiran yana kallon Diza agogonsa na Fata ya Dauka ya Daura a Tsitsiyan Hannunsa Lokaci Daya ya Duka yana Zura Takalmin da Diza ta Fitomai Dashi Sahu Ciki,sai da ya gama Sakawa kana ya Dago yana kallon Diza kafin yace"Ba Rakiya Uwar Biyu..?
Kasa Mgana Tayi Domin ita kadai taji me takeji Ganin taki Takowa garesa yaasa yayi Mirmishi kawai ya Juya yana Fadin"Sai na Dawo..Ki kula da kanki Kin ji ko..?
Sai da yakai kofa taji kuka yazo mata ta Runtuma da gudu ta isa Garesa sai dai yaji ta Rumgumoshi Ta Baya Tana kuka sai Lokacin Jikinsa yayi sanyi ya Waigo ya juyo da ita yana Share mata Hawaye Lokaci Daya yana Fadin"Ki daina kuka kin ji ko..? Zan Dawo da yardan Allah..!
Kai ta gyada mai kafin tace"Kayi min alkawari..? Shima kan ya gyada mata kafin yace"Nayi miki.."Mirmishi ta sakarmai kafin ta Kara Rumgumeshi Shima sai ya Riketa yana Fadin"Kinga Dauki mayafinki na ijiyeki wajen Mommy ko Hajja..Tunda Anty Rumanan bata nan Tana asibiti..!
Da musu ta koma ta Dauko Mayafinta wayarta suka Fice Tare amotarsa ta Shiga Direba na Jansu suna Fitowa Tawagarsa na waje suka Rufa musu baya amotar ma har suka kai kofar gidansu Hajja Kuka Diza take yi Tun Mansur na Daukan abun Wasa har shima Jikinsa yayi sanyi Shi ya karata Har Falon Hajja suka gaisa Lokacin Aiya na Ciki Tana Barci har yakai Kofa ya Dawo ya Tsugguna gaban Diza ya Sumbaci Cikinta kana ya Dago ya Sumbaci Goshinta ya Fice da Sauri Hajja dai na Daga Dakinta sai dai itama Haka kurum taji Zuciyarta ba Dadi tama kasa Cema Dizan kala.

Tun Bayan Tafiyarsa bata Minto Goma sai ta kirashi Taji Lafiyansa Haka shima,ta kasa Samun natsuwa sai da yace mata sun kusa isa Kaduna kana taji ta Dan sake,Hajja na Kitchen tana wanke wanke taso ta karba ta Hanata ganin Abunda take Dauke dashi sai ta Dawo Falon ta zauna Tana Cin wainar Fulawar da Hajja ta Soya mata yanzu da yaji.
Ko Minti Talatin basu yi da mgana da Mansur ba sai ga Kiransa wannan karon sai taji Mugun Faduwar gaba Har Hannunta na rawa wajen Daga kiran.

"Hello...Daga Hukumar Road Safety ne..Honourable Mansur Doguwa ya samu Hatsari a Hanyarshi ta Zuwa Kaduna yanzu haka muna Hanya zamo kawosa nan asibitin ABU dake Chika sai ku isa Asibitin Domin karin Ba....!
Iya abunda ta iya ji kenan wayar ta Subuce Daga hannunta ta Fadi kasa ita kuma ba inda Jikinta baya bari Gabadaya taji Numfashinta ya tsaya Cak Dan Cikinta ya Wani Wuntsila Lokaci Daya Taji Jinta ya Dauke da ganinta sai dai ta samu nasaran Yabka wani Razanannen Ihu Lokaci Daya Tana Fadin"Na shiga uku na Lalace Shikenan Mansur ya Tafi ya barni..Sai da nace kada ya Tafi..Shikenan ya Tafi ya barni..!

*Shakira..*
1/1/22, 18:55 - Maryam Badmsi: *SS...31*

*Ki biya ki karanta cikin salama da aminci 09069067488*

"Hajja dake Kitchen ne ta Rugo da gudu zuwa Falon jin ihun Diza atare suka Iso falon da Aiya wacce ke barci Ihun Diza ya Tada ita,Hajja ce ta Duka ta Rike Diza Tana Girgizata Lokaci Daya Tana Fadin"Hadiza meya ke Faruwa ne..? Lafiya.meya samu Mansur din..?
Take Fada Cikin Razana da Firgici jin kalaman da Diza ke Fadi.
Cikin kuka da Tsayawar Numfashi Diza ta Dago Tana kallon Hajja Lokaci Daya ta Riko Hannunta Tana Fadin"Hajja Mun bani mun Lalace..yanzu akakirani awaya ana Fadamin Mansur ya samu Hatsari a Hanyarsa ta zuwa kaduna..!
Dam gaban Hajja da na Aiya Bugawa Lokaci Daya Hajja ta Zabura ta saki Hannun Diza ita da Aiya suka Bude baki suka Furta Innalillahi wa"inna ilaihirraju"un Lokaci Daya cike da wani Firgici da Tashin Hankali Da ya bayyana a Fuskarsu Lokaci Daya.
Baya Hajja Taja cikin Tashin Hankali take fadin"Hasbunallahi wani"imal wakeel..Mansur..Allah yasa yana Lafiya Allah yasa wani Abu bai samu D'ana ba.."Tafada Lokaci Daya Hawaye suna wanke mata Fuska haka kurum Take jin wani Tsoro Daga kasan Ranta Diza kuwa kuka take yi kamar Ranta zai Fita Aiya ma Haka ga Rikicin Tsufa sai kuka Take Tana kiran Sunan Mansur Hajja Data Rasa ina Zata Nufa waje kawai Tayi ba Takalmi a kafarta ta Rarumi Zaninta data wanke saman igiya ta yafa ta Fice da Gudu sai Gidan Mommy Domin ta Shaida mata Abunda ke Faruwa.
Tana Shiga Falon Farko taci karo da Mama Fadime yadda Ta ganta ne yasa tace"Hajja Lafiya kuwa..?Hajja na Sharan kwallah tace"Ina Hajiya..?Mama Fadime tace'Tana Sama.."Ai batama gama Rufe baki ba Hajja ta Fara Taka Benen Da Gudu kamar Zata Kifa Mommy Dataji Kamar mgana Daga Sama ta Fito Daga Dakinta sukayi Kicibis da Hajja Cikin Tashin Hankalin ganin yadda Hajja ke kuka ne ya kusa saka Zanin Dake Jikin Mommy Sabulewa Cikin yanayin Firgici Tace"Mun Shiga uku Hajja Lafiya..? Wani abu ya Faru ne..?
Hajja ta Fashe da kuka cikin Raunin Zuciya tace"Yanzu aka kira Diza Aka gayamata Mansur ya Samu Hatsari a Hanyarsa ta Zuwa Kaduna..!
hannu Mommy ta dora akai Tana Fadin"Innalillahi wa"inna Ilaihirraju"un
Innalillahi wa"inna ilaihirraju"un
Tafada Lokaci Daya Cikin Tashin Hankali kafin ta Rike kafadun Hajja Tana Fadin"Yanzu yana ina..? Hajja tace"Bansani ba..Dizan bata min wani bayani ba sai kuka take.."Mommy tace"Ita Dizan tana ina..?
Hajja ta kara saka kuka Tana Fadin"Ko Minti Arba"in ba"ayi ba Dayazo ya kawota yayimin Sallama da zai je kaduna Taron su na Siyasa ya Dawo ga Diza ta zauna waje na Tunda gidan ba Kowa Ruma na asibiti..!
Ta karishe Fada Cikin karaya da Raunin Zuciya.
Juyawa kawai Mommy Tayi Zuwa Daki Tana Fadin"Bari na Kira Alhaji..Hasbunallahi Allah yasa Mansur yana Cikin kyakyawan yanayi ya Allah.."Take Fada itama Tana Gabda Fashewa da kuka jin Haka yasa Hajja itama ta Runtuma Zuwa Gida Domin ta kira Baba Habibu koda ta dawo ta iske ba yarda suke,Diza Tana ta kuka kamar Zata Shide,Aiya kuwa tama Gama Shiga rudani.
Ganin Halin da Diza take Ciki ne yasa Hajja ta Rikota Tana Fadin"Tashi..Tashi..Bar kukan nan Diza..Insha Allahu Babu Abunda zai samu Mansur..!
Diza kallon Hajja kadai take yi Tana jin kanta kamar ba Nata ba Cikin Juriya Hajja tace"A ina suka ce Mansur din yake yanzu..?
Diza ta Dafa Hannun Hajja Tana Fadin"Sunce suna Hanya zasu kai shi Asibitin ABU chika.."
Cikata kawai Hajja Tayi ta Nufi Daki Tana aro Jarumta wayarta ta Dauka ta kira Baba Habibu yana Tsakiyar kasuwa ta sanar mai Labarin Daya kusa sashi ya Fadi kasa Cikin Matsanancin Tashin Hankali ya Furta"Gare ka muke muka garekazamu koma ya Allah..Mu hadu a asibitin yanzu zamu tafi ni da Usman..'Yana gama Fadin haka ya Yanke kiran yana kiran Sunan Allah Kawu Usman Dake gefensa ke Tambayansa me ya Faru cikin Tashin Hankali nan yake gayamai Shima sai Salati Daman Baba Habibun ne yazo Sabon Shagon da Mastur ya tankamai Jari ya Farfado,nan da nan suka Hau Mashin din Baba Habibu suka Dumfari asibitin Chika Hankula tashe.
Haka ta Faru Daga Barayin Daddy Lokacin da Mommy ta kirashi,take gayamai shima Duk sai Hankula suka tashi yace yana Sabon gari ne yanzu haka Shima zai wuce asibitin In Mommy Zata iya Tuki ta tukasu Zuwa asibitin Haka kuwa akayi Mommy ko Duba mayafi ma batayi ba Hijabin Sallarta ta Zumbula ta Dauko key din Mota ta Zo Haraban Gidan ta Fito da Mota waje Bayan ta Sanar da Megadi da Mama Fadime Halin da ake Ciki.
Cikin gidan su Hajja ta Shiga ta iskesu Zukata sun Raunana Gwiwoyin sun yi Sanyi Diza ba yarda Take tun Tana iya kukan da Baki ta koma na Zucci sai Hawaye Hajja ce ma ta Zama mai Juriya tana Lallashinta Aiya kuma sai mganganu take Tana Fadin"Wayyo Mansur..Allah yasa yana Lafiya Allah ya karemana shi.."
Da Farko Mommy taso tace Diza da Aiya su zauna agida ammh ganin Irin yadda Suke ne yasa bata samu Damar yin mgana ba Suka Dumguma Dukkansu Zuwa asibitin Mommy ke karfin Halin jan Motan Su kuma zukata nata Salati da Ambaton Allah.
Chapter 68 · 0% Book details