← Book details Sadaukarwa So Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 78 OF 94

Sashe 78

Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 5 min read

Mastur bai yi Shawara da kowa ba yayi ma Sarget Inuwa mgana Matarsa Tana Harkan kasuwanci na Kaya kala kala ita ya bama Kudade masu kauri,tayo Mishi Siyayyar kayan Haihuwa na Jarirai Both Wanda za"a saka ma Mace ko Namiji,Da Siyayyan Atamfofi da lesuna na Diza akwati Biyu nata Daya na Abunda ke Cikinta Daya kuma ya Shirya Ya kawo su Har Zaria da kansa Batare da Rumana ma ta sanu ba Har yazo ya Tafi sai da ya wucen ne ya Kirata ya Fadamata yazo,ammh ya koma to me zata ce mai..?Bata da Abun cewa Tunda Hakan ya Zaba kuma yaga yafiyemai.
Tana Tashi Daga wajen aiki ta wuto nan Direct,Gidan Hajja ta Fara Biyawa suka gaisa ita ce ma Take Fara Fadamata abun Arzikin da Mastur ya kawo ma Diza tace ta Shiga gidan tagani Rumana sai taji Abun ya Daketa Sosai Ammh bata Nuna ma Hajja ba Tayi mata Sallama ta Shiga Wajen Diza.
Mommy bata nan taje gaisuwan Rasuwan Mijin kawarta ya Rasu Diza ce Kadai agidan sai Mama Fadime.
Afalon kasa suka gaisa da Mama Fadime Tana Tambayanta Diza tace Tana Dakinta Daganan ta Nufi Dakin Diza Zuciyarta Cike da Sake Sake.
Tana Shiga da Sallama Ta iske Diza zaune kan gado Akwatunan Duka Zube agabanta abude Tana Ta Dubawa Tana Mirmishi ita kadai Dagani Kila Tun zuwansa da kayan ne bata Rufesu ba..
Cikin Fara"a Ta Dago Tana amsama Rumana Sallaman nata Fara"an da Tun bayan Rasuwar Mansur batayi irinsa ba sai yau Cikin mamaki da Dariyan yake Rumana ta kariso Cikin Dakin Tana Fadin"Uwar Biyu..Me ake kallo ana Ta Sakin Mirmishi haka..?
Tafada Lokaci Daya tana Zama gefen gadi kuma Tana kare ma Tsadaddun kayan kallo Ranta na Suya wanda bai Rasa nasaba da Kishi..
Cikin Fara"a Diza ta Dago Idanuwanta ta Sauke kan Rumana Tana Fadin"Kedai bari Ruma..Daman yanzu nake Shirun Kiranki..Kalli ki gani Abun arzikin da ya Mastur ya kawomin Hatta komai na Bby ya siya Haihuwan kadai yake Jira.."Ta karishe Fada Tana Daga mata kayan Rumana ta karba Tana kallo Cikin yake tace"Kai Masha Allah Kaya sun yi kyau..Kinsan Uba ne shi..Shiyaa kamata ya Fara Tarban wannan Haihuwan.."Diza na Dariya tace"Ko..? Shima haka yace..Bai jima da Tafiya ba ina ta mamakin ina yasan Kaya nace ko kike kika Siyo sai yacemin A"a Matar yaronsa ne Achan Porthercourt ya bama kudi tayi Siyayyay ki Duba Harda Nima fa yamin kaya Akwati Guda na Fitar suna.."Ta karishe Fada tana Dago ma Rumana wasu atamfofi.
Rumana Tana kallo Tana yabawa Cikin Farinciki ko alama Bata Nuna ma Diza wani abu ba Har Mommy ta Dawo ta isketa itama sai alokacin Taga kayan Tunda bata Gida Tun Safe ta Fita
Rumana bata Dade ba Tayi musu Sallama ta koma gidansu Hajja suma Tayi musu Sallama ta wuce Gida Ranar dakyar ta iya Barci Abun ya Dameta Tana ganin Anya Abunda take ganin yana Faruwa in har tace Zatayi Gudurinta anya watarana Mastur bazai manta da ita Ba matukar Diza na gabansa ba Ta Fara Sarewa da Tunanin Anya..? Gabadaya gwiwanta yayi Sanyi ta rasa wannan karfin Gwiwan Datake Dashi Tun Farko.
Da safe da sukayi waya da Mastur din bata nuna mai komai ba sai ma Godiya Data Taya Diza yace kada ta Damu Diza da Abunda ke Cikinta suna Wuyansa ne koda Mansur yana Raye Ballatana Baya Raye,Da ace bata karanta Diary dinsa ba Data yarda da Shi ammh yanzu Jinsa kawai take ta Riga tagama Sanin Karfin Soyayyar da Mastur kema Diza bazai barsa yayi Sukuni ba sai yaga ta Sauka Lafiya.

******

Rumana ta kare Intenship dinta Har Tayi Cukun Cukun Tafiya Service dinta Anyi Posting dinta Camp din Kano,Data kira Mastur ta gayamai yace ba Mtsala sai ta Kwana Gidan Maryama haka kuwa akayi Dataje Kanon Bayan Taje Camp din Tagama abunda Zatayi Dayake Komawa Zatayi Tayi Marriage Certifcate Daganan Mijin Maryama yazo ya dauketa taje gidansa ta kwana Maryama itama Cikinta Har ya Fiti Ashe tun zuwanta Rasuwa da karamin Cikinta,nan ta kwana Maryama na ina ta saka da ita Washegari bata Tsaya ba ta Koma Zaria,Taje Abu Asibiti takai Takardunta nan Zatayi Service dinta Nan da Sati Hudu Zasu Fara kafin su Fara sai Ta Roki Mastur Tana so Taje gida Sokoto ko Sati Tayi ammh kafim ta Wuce Zata Biya kaduna Gidansu Basma ta duba mamarta bata da lafiya,Kuma Dayake Ita da iyayanta sun zo mata gaisuwan Mansur,Mastur bai Hanata ba ya barta da Cewar zai zo Nan Sokoto sai su Dawo zaria Tare da haka suka Rabu Tafiyar Mota Tayi bayan Taje kaduna ta kwana Daya Gidansu Basma Daganan ta Hau Jirgi Zuwa Sokoto Bayan tayi sallama dasu Hajja da Mommy da Diza wacce Cikinta ya shiga watan Haihuwansa.

Rumana Taje Sokoto ta Huta sosai ta samu kyakyawan Lokaci Tare da iyayanta,Allah Sarki Tana chan Sokoto Jikokin Goggo Jummai suka zo suka Tafi da ita Jikin yaki Dadi ba yadda Abba bai yi ba su barta Anan ya kaita asibiti suka nuna a"a Ashe Ajali ne ke kiranta da Tafiyarsu da kwana Daya Allah yayi mata Rasuwa Rumana taji Mutuwar nan ba ita kadai ba Hatta Umma da Abba Daman Jume Da ita suka Tafi Kwanan Rumana Biyar da zuwa suka Tafi wamako Gaisuwa suka kwana Daya suka Dawo Ranar Datayi kwana Shida da Zuwa sai ga waya Daga Zaria Mommy ta kira Umma Tana gayamata Diza ta sauka Lafiya ta samu Da Namiji Umma Tana ta Murna ita take Fadama Rumana Diza ta Haihuwa itama Tayi Murna Jin Lafiya ta Sauka Duk da a asibitin Abu Tudun wada ta Sauka inda take awo,Sai da ta Kira Mommy ne take Fadamata Tun Jiya Dizan ke Naguda asibiti suka kwana Tana ta kuka tace a Kira mata Mastur Shine aka Kirasa,yau da Safe ya Biyo Jirgi ya Taho yana asibitin ma Diza ta Sauka yanzu haka yaje Biyan Bill Dim asibitin ne an basu Sallama Zasu koma gida.
Rumana Taji mamaki,Ganin ga yadda suka Rabu da Mastur Meyasa bai kirata ya gayamata ba..? Wata Zuciya ta ankarar da ita Diza tafiki Muhimmanci Shiyasa,Ranar tayi kuka Sosai kukan Rashin Samun Zuciyar wanda take so.
Ko washegari da Umma taga batayi Shirin Tafiya ba Data Tambayeta sai tace zata jirata su koma Tare Umma tace Shikenan
Chapter 78 · 0% Book details