← Book details Sadaukarwa So Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 69 OF 94

Sashe 69

Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 5 min read

Sanda suka isa asibitin sai suka Rasa ina zasu gashi asibitin ta Cika da Motoci basu san Lokacin Tuni har tawagar mansur din sun iso dashi Tare da yan Sanda,Mommy ce ta kira Daddy ya Daga nan take gayamai gasu sun iso Cikin Tashin Hankali yace yana Hanya bai kariso ba Ammh Yanzu sunyi mgana da Baba Habibu yace Sagir P.A din Mansur ya kirashi suna Emergency Harda shi Baba Habibun da Usman din Balaraba sun iso Suna Tare."
Jin haka yasa da Tambaya suka isa Kofar Emergency din Tunda wajen suka Tabbatar da Ba Lafiya Domin gasu Sagir nan sai Sharan kwallah suke da Sauran Matasa ga yan Siyasa nan Abokan Mansur da kuma Yan Partynsu Gefe kuma Baba Habibu ne da Usman Tsaye kowane yana Kokuwa da Numfashinsa Hajja ce ta Fara Tunkarasa Sai ji kawai yayi ta Rikosa Tana Fadin"Ina Mansur din..? Babu abunda ya Sameshi ko?
take fada Cikin matsannancin Damuwa da kuma Zubar kwallah sai da ya Dago kai ne ya Ci karo da Mommy da Diza da Aiya Idanuwa sunyi Jajir Cikin Jarumta yace"Hajiya gabadaya kuka Taho..? Harda Hadiza Tana wannan halin ai da kun barta agida ita da Aiya..!
Mommy tace"Bazasu Zauna ba Baba Habibu..Yanzu dai ya ake Ciki..? An kawo Mansur din..? Kuma wani Hali yake Ciki..?
Baba Habibu ya saki Numfashi kafin yace"To bazan iya cewa komai ba Hajiya koda muka kariso an riga an iso Dasu har an Shiga dasu Ciki..Sagir ne ya Kirani ya gayamin sunaa Emergecy Hatsarin Shida Direbansa ne suka yi karo da Mitar Bua..!.
Dukkansu suka Hada Baki wajen Fadin"Innalillahi wa"inna illaihirraju"un.."Sai kuka Diza da Aiya Hajja kuma sai Hawaye Baba Habibu na Jin Abun aranshi yace"Mummunan Hatsari ne ya Faru sukace..Dayake Motarsace akan gaba Yanzu dai Tunda Likitoci suka Shiga Ciki basu Fito ba..Sai dai mu jira muga Abunda Allah Zai yi kuma.."Mommy na Sharan kwallah Tana Fadin"Allah ya Tashi kafadunka Mansur..'
Daidai Shigowar Daddy Hankali Tashe ganinsu Cikin wannan yanayin yasa Duk ya Razana Cikin Tsoro yace"Ya jikin Mansur din Habibu..? Bayanin Daya yi ma su Mommy Shi yayi ma Daddy wanda yasa Dole ya Cire Hula yana Fifita Cikin Tashin Hankali yace"Hasbunallahi wani"imal Wakeel Allah ka kawo ma wannan bawa naka da Sauki.."Yagama Rufe baki kenan sai ga Babban likitan Daya Jagorancin Sauran Likitocin Daga Emergency din ya Fito yana Cire Safar Hannunsa Duk Jini ya Jefa Cikin Abun Shara Da Sauri Su Daddy suka Nufeshe da Duka Jama"ar Dake wajen kowa Tambayansa yake Ya ya Mansur din yake..?
Dr. Din ya kallesu Daya Bayan Daya kafin yace"Su waye Ilayan Honourable Mansur acikin ku..? Da sauri Daddy da Baba Habibu suka Bayyana Gabansa Cikin Nazarinsu yace"Shi Dayan fa da aka kawo su Tare..'?Sagir ne yace"Direbansa ne Tare suka samu Hatsarin..!
Dr din Cikin Tsausayawa ya Dafa Kafadan Daddy ganin Duk yafi su Rudewa yace"Sai Hakuri..Dukkansu sun amsa Kiran Allah..Shi D'anku ma Tun kafin su iso nan ya Cika kansa ne ya Fashe..Dayan ne sai bayan da muka Shiga dashi Ciki..We are Sorry Mun kasa Ceton Rayuwarsu..yanzu wani Cikin kuzai Biyo ni Office Domin Cike Takardu Za"a baku gawarwarkinsu.!
"Daidai da kalma Daya na mganarsa Tamkar wata Dalmace ko nace Wuta A zukatan Ahalin Mansur Sai Ihu da kuka ya Tashi Baba Habibu Dashi da Daddy suka Tallafi juna Domin Dukkansu suna Neman Faduwa Diza Dataji komai acikin kunnunta ta kwala kara Ta Zube ajikin Mommy Data Tallafota Tana Girgizata Cikin kuka Take Fadin"Innalillahi Wa"inna Ilaihirraju"un..Allahu Akbar Allah ya jikan ka Mansur Allah yayu maka Rahma.."Take Fada Tana Rumgume Diza Ta Fashe da kuka Hajja kuwa ba Domin garun Dake gefenta ba sai ta Fadi kamkame Hannun Aiya Dake gefenta Tayi Lokaci Daya Taji kamar ta Daina Fahintar komai Sai da taji kukan Aiya Tana Fadin"Innalillahi yanzu Shikenan Mansur ya amsa kiran Allah..? Kai Innalillahi wa"inna Ilaihirraju"un zukata bazasu iya Daukan Wannan Rashin ba..!
Sai alokacin Hajja taji bakinta na Furta Salati ta Dire da Hasbunallahi wani"imal wakel Kafin ta Fashe da wani kuka mai Fitowa Daga karkashin Zuciyarta.
Baba Habibu yayi kokarin Danne kukansa ya Dafa Daddy yana Fadin"Sai Hakuri..Allah Shine ya Hallesa kuma yafimu Sonsa ya karbi Abunsa..Allah ya jikan ka Mansur."
Daddy sai Hawaye Sharr haka Kawu Usman Baba Habibu kuwa Wajen Su Sagir ya Nufa yana Fadin"ku kira Iyalan Direban nashi ku sanar dasu..Suzo sai su karbi gawarshi..Allah yayi musu Rahma.."Gabadayansu kallonsa suke suna ganinsa a mtsayin mai Jarumta da Dakiya Shi ya kara Tausan Daddy Dake kuka suka Tafi Office din Likita suka Cike Takardu nan da nan aka Fara Cukun Cukun Basu gawar Mansur Ba Dadewa sai ga Iyalan Direban sun iso Dan Cikin Zaria ne sai kuka suke Abun Tsausayi Matansa Biyu alokacin Hawayen Mommy Dake Diga kan Fuskar Diza ya Farkarta da ita sai bata mgana bata kuka sai Hawaye kadai Dan Cikinta na Har bawa kamar zai Fito aranar.
Zuwa Lokacin Tuni Mutuwar tayi Tambari ta Fara Yaduwa ta kafafen yada Labarai ta Internet gidajen Radio dai basu Fadi ba Tukunnah Gawan Direban aka Fara Fita da ita mansur Shi a Ambulance din asibiti za"aFita Dashi Saboda Jini Dake Zuba ta kansa.
Baba Habibu da kansa ya Kira Yayan Baba Sule ya Fadamai Rasuwar Mansur Allahu akbar Zukata Daga Chan maruka sun Raunana Maryama da Mardiya haka suka sume gau Daman Mardiya Tana chan Tun Biki Chan suka barta Baba Sule kuma sai Ciwo ya Tashi ya Fadi Allah yasa An Tareshi,Cikin Tashin Hankali suka kamo Hanya kwansu da kwakwatansu suna kuka kukan Fadin wani majingini kuma Bango Garesu Zuwa Lokacin Duk wanda ya kamata yaji Rasuwar yaji Daddy ya kira Abba ya Fadamai haka ya koma Gida yana Fadama Umma sai kuka nan da nan ya Fara musu Shirin Tahowa ta Jirgi.
Mastur ne kadai ba'a samu wayarsa ba Ana ta kiransa wayarsa Tana Kashe sai Rumana da kwata kwata Tashin Hankalin da suke ciki ya mantar dasu ita.

****

Rumana Da suke Zaune da Abokiyar aikinta Aisha Bala a Femele word na cikin asibitin Abu Chika,waya ce a Hannun Aisha Tana ta Danne Danne Lokaci bayan Lokaci Tana Sakin Mirmishi ita kuma Rumana Zaman ta kenan ta Dawo Daga Roud din Ta Duba wasu marasa Lafiya ne,Tazo ta zauna nan kujeran Dake Fuskatan Aisha a kebentattacen wajen da aka Tanada musu Domin irinsu.
Chapter 69 · 0% Book details