← Book details Sadaukarwa So Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 87 OF 94

Sashe 87

Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 9 min read

"Har Rumana ta Fice Mastur bai iya Motsawa Daga inda yake ba Gabadaya Jikinsa yayi sanyi Kirjinsa ya cika da Karamcin Rumana da Alherinta Gareesa sai yake ganin kamar bai kyauta mata ba Tamai komai a rayuwa TaRufamai asiri ta zauna Dashi Ahalin da bai taba kallonta a mtsayin matarsa ba Bata taba kai karansa ba,bata taba kuma Bude baki Tayi mai mgana ba,Shiyasa yake girmama Hallayarta acikin Zuciyarsa.
Diza Dake zaune Cikin mayafi Tana kallonsa Gabadaya sai ta Raina kanta ganin irin yanayin Daya shiga ya kurama Kofar da Rumana ta fita Tun dazu ya kasa Motsi sai taji kirjinta yayi nauyi Kishi ya Lullubeta har bata san Lokacin da Hawaye suka Ciko idanuwanta ba Ta Shirya ma Kanta Rayuwa da Mastur ita kadai a ton Farkon Fari sai dai ina Allah ya gama nashi Tsarin Dole Zatayi Sharing dinsa da Rumana.
Tana cikin wannan Halin ya juyo yana kallonta Hannayensa Goye a Bayansa Bai zauna ba illah Kwandon da Rumana Riko ne yake kallo Zuciyarsa na Harbawa waje Daya,Kamar kwallah Zata Zubomai saboda Tsananin Tsausayinta,da wani irin yanayin Da Har yau ya Kasa gane wani yanayi ne yake ji game da Rumana sai dai abu Daya ya sani ita din ta Cika Kirjinsa da karancinta da kyakyawan Dabi"unta wadanda suka sama Mata Gurabe masu Girma da Matsayi acikin Zuciyarsa.
Har yanzu Bai gama yarda ma kansa Diza ta zama matarsa ba Gani yake kamar a mafarki,Allah Sarki Rayuwa Ashe Rabon Mansur karami ne ya Tabbatar da Auranta da Mansur ashe shi din bamai Zama bane
Allah ya jikan Mansur da Rahma Rana bazata Fito ta Fadi bai ji Dacin Mutuwarsa ba, bai ji Hawaye sun kawo Idanuwansa ba Ya Tabbata Har gaban Abada bazai Taba mantawa Dashi ba Duka Khamsun Salatmwatul dinsa Baya mantawa Dashi yana Rokamai adddu"an Rahma da Gafara a wajen Ubangiji.
Kallon Bedroom din yake da alama Sabo ne ba"a Taba amfani Dashi ba kamar ya sani Diza ta Bukaci a Dayan Bedroom zata Zauna wanchan da sukayi Rayuwa da Mansur ba zata iya kara wata Rayuwa da waninsa ba,Haka kurum take ji kamar bata kyauta ma Marigayi ba,Shiyasa Datayi mgana kowaya yarda da ita Dayake Ita da Mansur Lokacin Bedroom Daya sukayi ta Sharing har bayan Rasuwarsa sai ya kasance Dayan ne suka barma Baki Dayan kuma Basu Taba amfani dashi ba Shi aka gyara Daman akwai komai na Bukatar Rayuwa sai dai an kara Abunda ba"a rasa ba.

Mastur Dake Tsaye gaban Diza ya saka Hannu ya kwabe Babbar Rigar Jikinsa ya Ijiyeta nan Saman gadon Lokaci Daya ya Duka yana Sabule Takalmin kafarsa kana ya Dago yana kallon Diza Lokaci Daya yace"Ki tashi kiyi alwala muyi Salla Hadiza...!
Daman haka yake kiranta Sai Lokaci Bayan Lokaci ne zakaji ya ambaci Diza.
Muskutawa Tayi ta Zuro kafafunta ta Sauko Daga kan gado Tana Rike mayafinta Cikin Sanyin Murya tace"Ina da alwala..Kuma nayi Sallar Isha"i..!
Sau Daya ya kalleta ya kauda kai Jin yadda Zuciyarsa ta Gaba ganin ta yaye mayafinta,Da Sauri ya karisa Saman Cafet din Dake bakin gadon ya Daidaita Sahu yana Fadin"Nima nayi isha"in aie..!
Ganin haka yasa ta Bude Wardrope ta Dauko Hijabinta Dayake Duk Anty Hadiza tazo mata da akwatunan kayanta Sauran dai suna gida,Takowa tayi ta Tsaya abayansa itama ta Daidaita Tabishi Sallar Raka"a Hudu yayi musu kafin su Sallame yayi addu"o"i sosai na Zaman Lafiya garesu daga karshe ya Rokama Dan"uwansa Gafara Dukkansu sun Shafa addu"an ne da Raunin Zuciya da Sanyi Jiki Gefe Daya Idanuwansa ya kawo Ruwa Saboda Tunawa da Mansur wanda Har Abada Zukata bazasu Manta dashi ba.
Shuru ya Biyo bayan Shafa addu"an nasu kowa da Tunanin Daya addafeshi,Diza Tana Gefe kanta na kasa Tana wasa da Gefen Hijabinta Yayinda Da Mastur yake gefe shima kansa na kasa ya Rasa ta ina zai Fara,Shi dai ba wata Shakuwa Tsakaninsa da Diza yau yanzu ma Bayan Rasuwar Mansur da Sauki Sauki kan Abaya Ganin ya raasa me zai ce mata ne ya Dago yana kallonta Cikin Sanyinsa yace"Kina jin yunwa..? Bai bata Zarafin mgana ba ya Cigaba da Fadin"Dauko ga kwandon Chan Rumana ta kawo muga Abunda ke Ciki..!
Ita dai Ranta ne ya baci jin Abunda ma zai riko mata Rumana ce ta kawo sai taji Duk Ta Raina kanta bazata mai gaddama ba yasa ta Mike Jikinta Sanyaye ta Dauko kwandon zuwa Gabansa Dayake a Zuge yake da zif Tana Shirin zama ya kalleta yana Fadin"Open it..!
Batayi musu ba ta Duka ta Budeshi,Sai ga Hollandian masu sanyi guda Biyu da kilishi da kazan Tayi Rapping dinsu Kura ido yayi yana kallonsu kafin ya Murmusa yace"Allah yayi miki albarka Rumana..!
Yafada yana Bayyana Jin Dadinsa ita dai Diza kanta na kasa Ta kasa Fassara wani Hali take Ciki Cikin Hakane taji yana Fadin"Ki samo Filet ki Dibi kici..!Batasan sadda tace"Ni fa a koshe nake.."
Tafada Cikin Kishi Daya taso mata Daga kasan Zuciya na yau Daran Farkonsu ammh kuma Mijinta na gabanta yana saka ma Wata albarka ita kuma ko Oho..!
Yana kallonta Ido Cikin ido Kafin yace"Ban yarda ba..Me kika ci..?
Yafada yana Tsareta da ido sai ta kasa mgana ganin haka yasa shi ya yunkura ya mike ya Fice Batare Daya tankata ba yana Fita ta Sauke Numfashi Tana kokarin Daidaita kanta Kada ya Fahimci Halin Datake Ciki.
Bai dade ba ya Dawo Dauke da Filet da Mug,sai Pork guda Daya shi ya Bude kazan ya Gutsiran ma Diza ya kuma Diban mata Kilishi da Dayawa Tunda shima yana son Kilishi,Sai ya Tsiyayamata Madaran Duka ya Turo gabanta bai mata mgana ba sai shi ya matso gabanta suka saka Filet din a Tsakiya yana Fadin"Oya Matso..!
Batayi gaddama ba ta Matso batare da wani Tunani ba ya saka Hannu yago Cinyar Kaza,ya Nufi Bakinta Dashi,Cikin mamaki Take kallonsa Sai ya Hade rai yana Fadin"Oya open ur Mouth..!
Dole ta Bude ya Tura mata yana Fadin"Nasan yunwa kike ji..ki Bude Ciki kici sosai..Rumana ta gasa kazan nan da kanta naji Test din gashinta..!
Tunda ya ambaci Rumana taji Dandanon Naman ya koma mata Daci Turawa kawai Takeyi ba wai Domin Tana jin Dadi ba,Dakyar ta karba sau Biyu ta kauda kai sai ya Girgiza mata kai yana Fadin"Ki bude Ciki fa..Ga Kilishi ga Madara..!
Dole bata da yadda Zatayi tayi mai gaddama haka ya Dinga bata Kilishin sai da yaga ta kusa Amai ya kyaleta,Ya mika mata Madaran ta karba tasha kadan ta Mikamai shima ya karba yasha,Ya ci Kilishin sosai ya Cinye Duka,Diza bata barsa ya Tattara komai shi kadai ba ita ta Tayashi suka maida komai Kirchen Sauran kilishin da kazan kuma ta sanya Cikin Fridge.
Kana suka Dawo Daki,Tiolet Mastur ya Shiga ita kuma Diza sai ta Bude Wardrope dinta ta Fito da kayan Barci itama Tana son Shiga Tiolet din Zatayi Brush ta wanke bakinta
Bai dade ba sai gashi ya Fito shima bakin ya wanke Yana Fitowa ya Kalleta irin kallon nan na wani yanayi da Sauri ta Raba ta Gefenshi ta Shige Tiolet,Kansa ya Dafe Tunanin bai Dauko kayan Barci bs ko Jallabiya bai iya kwana da kayan Jikinsa sai ya Cire Rigar yabar da Singlet din wandon Jikinsa ya Zauna nan gefen gado sai ga Diza ta Fito Sanye da Wata Rigar Barci mai Ruwan Madara bata da kauri Sosai Domin yana Hango Farin pant din Jikinta da kuma kan Nonuwanta Da bata Sanya Bra ba,Rigar ko gwiwa bata kai mata ba kunya yakamata taji kamar ta koma Tiolet din sai dai ya Riga ya ganta Ita da ba domin Anty Hadiza ta matsa sai ta saka wannan Rigar ba wlh bazata iya sakata ba Lokacin Mansur bata da wata Damuwa ba Ko ba aure Sun Shaku da juna bata wani jin Nauyinsa To Mastur ne fa akwai jim kunya da Nauyin juna a Tsskaninsu sosai.
Shi kuwa Daskarewa yayi a zaune yana kallonta Zuciyarsa na Harbawa yana jin yana yanayi na Sha"awar diza da matsananciyar Soyayyarta na kara Fizgansa wlh da Farko bai shigo da niyar yi mata wani abu ba ammhZuwa yanzu Daya ganta Cikin wannan yanayin Tunaninsa ya Sauya wanda Har bai san sadda ya Taso ya kariso gabanta ba daga ita Har shi basu Fargaba sai da suka jisu sun samu Muhalli a Cikin Kirjin junansu kana kowa ya Ssuke ajiyar Zuciya Diza sai ga Hawaye na kukan daman zata ga wannan Ranar da zataji tasaman Kirjin Mastur shima anashi Tunanin haka din yana Rike da ita yana Tunanin yau ga Dizan Daya kusa mutuwa akanta ta Zama mallakinsa sai da Hawaye suka Cika Idanuwansa kamkam ya Rumgumeta yajata Gefen gado ya Zauna Lokaci Daya yayi mata Masauki kan Cinyarsa kunya ta kama Diza sai ta kasa Dagowa ta Noke Bisa Kirjinsa.
Wani Kayattacrn Mirmishi ya saki kafin ya Dago Habarta suka Hada ido,Ido Cikin ido suke kallon Juna suna karantar yanayin da suke Ciki Diza Tana kallon Idanuwan Mastur tana jin kamar su dauwama ahaka yayinda Shi kuma yake kallonta Cikin Soyayyarta da kaunarta Hade da matsananciyar Sha"awarta Daya kamashi Loksci Daya.
Cikin Shakewar murya yace"Alfarma Daya zan Rokeki Hadiza ina Fatan zakimin..?
Kanta na kasa ta Dagamai kai Tana Fadin"Insha Allahu indai batafi karfina ba..
Jinjina kai yayi yana Fadin"Bata fi karfinki ba..Rokon ki zan yi Don Allah..Da Darajan iyayanmu Ki zauna Lafiya da Rumana..Ki Tayani Mutumta ki Tayani Girmamata ki Tayani yi mata alheri koda Rana daya kika Kalleta da wani Duba bazan ji Dadi ba..Ni kaina ina Girmamata ina kuma Ganin Darajanta ki Taimakamin kema ki Darajata ki girmamata Shi kadai nake Rokon ki.!
Diza tayi Jagale tana kallonsa Kai ya gyada mata alamun Tabbatarwa kafin ya Cigaba da Fadin"Eh Diza..Rumana ba irin Sauran mata bane..Tayi min Karamci da alherai masu Dimbin yawa wanda bazan iya mantawa dasu ba..Ba auran ki bane Alherinta gareni Rumana ita Ce Rufin asiri na Ta Dade tana Nuna Min Halin Girma Shiyasa bana son naga An batamata rai ko kuma Naga kunci ko Damuwar a saaman Fuskarta ta Chanchanci Tayi Farinciki har Karshen Rayuwarta..!
Yafada Kamar zai mata kuka,Ganin haka yasa Diza ta Danne abunda ke taso mata tace"Nayi maka alkawarin zan Tayaka Girmamata Har karshen Rayuwarmu.."
Ido ya sakar mata kafin yace"Are u sure..? Da sauri tace"Yes Very Sure..!
Ai batasan sadda yabata Wani Rumguma ba kamar zai Tsaga Kashinta,yana Tusa kansa Cikim Kirjinta yana Fadin"Tanque..So much..Allah yayi miki albarka.!bai bata Damar amsamai ba Taji yana Kaita wata Duniyar da ba wai bata sanda da ita bane sai dai kuma Bata tsammaceta alokacin ba kuma Diza bazata iya juyama Salon Mastur baya ba Balle bukatarsa ba Bata san ya akayi ba Tadai tsincesu Tsakiyar gado Cikin Bargo Dukkansu Naked Fatar su na Gogan na Juna Diza ta Haukace ta Rude jin Ta hannun gwarzon maza Wanda ya sata ta Fita Daga Hayyacinta Tana kuka Sharban batare Data sani ba Bazata iya Dora komai ba Abubuwan da suka Faru ba sai dai abu Daya ta sani Duniyar da Mastur ya kaita tasha Bambam da wanda ta saba zuwa abaya wannan wata Duniya ce ta Dabam
Shi kanshi Hakan ce ta kasance a wajensa baxai iya Dora komai ba,ba kuma zai Furta komai ba Sai dai zai iya cewa ya samu gamsuwa da Diza 100% ,Mata suna suka Tara,kuma duka mace sunanta Mace Shidai yasan mai Sa""a ne Duka matansa yan Baiwa ne Rumana zumarta na Gigitashi Har ya Fice Daga Hayyacinsa yau ga Diza itama Daya sami Gamsuwa da ita sosai Wanda yaasa Har bayan sun yi wanka sun koma sun kwanta Da suka Tashi sukayi sallar asuba bai iya Kyaleta ba Sai da ya kara maimaitawa yana kara Godema Allah da Tarin Ni"imar Daya yi Mishi na Zuka zukan mata masu Lafiya Da Kuruciya.
Chapter 87 · 0% Book details