← Book details Sadaukarwa So Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 74 OF 94

Sashe 74

Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 8 min read

Daddy ne ya Durkusan da Mastur gaban gawan Mansur yana Fadin"Kayi ma Dan"uwanka Addu'a kafin afita Dashi..Kayi Hakuri kada kayi mai kuka kaine Komai nashi Tun yana Duniya yau ma da zai yi bankwana Damu ka Zama komai nashi.."Yafada Lokaci Daya Shima Hawaye na kawo mai da Sauri ya juya ya Fita yana Sharan Kwallah Hakama Baba Habibu,Rumana Data ke kallon Mastur haka take Toshe Bakinta Saboda kuka Hajja ma kallonsa take ji Rauninta ya kara Bayyana Mommy da Umma suma sai Sharan kwallah Diza dai ido kawai ta sakamai Har yanzu din nan Kanzil Diza bata Bude baki tace ba Kuma Tunda ta Zauna awajen bata Motsa ba,har aka Fita da Mansur akayi mai wankan gawa wanda Baba Habibu ne da limamin masslacin anguwan sukamai wanka suka Shiryashi
Mastur Durkushe yake yana Bin gawan da akace ta Mansur ne da kallo Hawaye koDigo bai Sauko Daga Cikin kwarmin Idanuwansa sai dai Radadi da Zafin Dayake Fitomai Daga kasan Zuciyarsa sai ya Gummaci Dama Faduwa yayi a kasa yayi ta Birgima yana kuka kila zai samu wani Sauki.
Mansur fa..?Mansur dan"uwansa Dayafi Kowa Shakuwa Dashi Duk Duniya ,Mansur kaninsa wanda suka Taso Tare..? Mansur wanda ya kasance Farincikinsa madubinsa,Komai nashi Yau Shine ake so ace mai Cikin Likafini acikin makara Za"a kaishi Kabari..?
kai Innalillahi wa"inna Ilaihirraju"un sai alokacin Yaji acikin Zuciyarsa ya iya ambaton Haka Sai ya samu kansa da Sulalewa ya Zauna Dabas gaban gawan Hannuwansa na Rawa ya saka ya Jaye mayafin Fuskar Mansur mai Cike da Mirmishi a kullim ta Bayyana Cikin Likafi an Daddaueshi gam,Sai Mastur ya saki Zanin yanaji kamar wani Duhu zai mamaye Cikin Idanuwansa Lokaci Daya ya kurama Mansur ido Yana Turo Rayuwarsu Daki Daki Tun suna yara Har matakin Girmansu  baisan sadda ya Fada kan gawan fa yana so ya Fashe da kuka ne ammh kuma kukan yaki Zuwa sai dai Soya da Radadi Daga kasan Ransa kamkame gawan Mansur yayi yana ji kamar mafarki ne Mansur zai Tashi yace Dagani Ya Mastur Dagani da Rai na.
Gabadaya su Umma sai suka Fashe da kukan Tsausayin Mastur Rumana kuwa Kasa Zama Tayi sai ta mike ta Fice da Gudu Tana kuka Hajja ta Mike Cikin ganin Jiri ta isa kusa da Mastur ta Durkusa ta Dafashi Tana Fadin"Kada kayi mai kuka Mastur..Tashi ka Dago kanka kayi mai addu"a..Mansur ya Riga ya Tafi ya barmu..Ya tafi ya barmu Cikin Tsananin kewa Sai dai muyi Fatan Allah ya jikansa da Rahma.."Ta karishe Fada Tana Danne kukanta kafin ta Mike Tsaye Jiri ya kwasheta Tayi kamar Zata Fadi Umma ta Mike da Sauri Ta tarota ta Fado Jikinta suka Fashe da kuka da Sauri tajata suka Fita Falo suna kuka.
Jin kalamam Hajja yasa kamar Wani Allura tayi ma Mastur ya Dago kansa yana kallon Fuskar Mansur ya Dafashi yana Fadin"Allah ya jikan ka Kanina..Allah ya Rahamsheka..Allah yayi maka Rahma..Allah ya kyautata zuwanka..Allah ya sadaka da Mala"ikun Rahma Allah ya sa Kyakyawan Hallayanka su Bika..Allah Allah ina Rokonka Allah ya jikan Mansur Allah Allah ka Tsausayamai..Allah..Ya Allah.."Kawai yake Fada yana jin wani karyewan Zuciya Lokaci Daya Wasu Hawaye masu Dimi Suka Biyo Kuncinsa Baba Habibu da Daddy da Abba da Baba Sule Dake Tsaye Bayansa Tun Dazu suka rika amsawa da Ameen kafin Abba ya Duka ya Saka Zanin ya Rufe gawan Mansur Daddy kuma ya Saka Hannu ya Dago Mastur yana Fadin'"Ameen Mastur...Tashi..Tashi..Ka kama gawan Dan"uwanka mu Tafi mu Sallacesa Mu mikasa gidansa na Gaskiya.."Kamar Rakumi da alaqahaka ya Mike sai Alokacin ya ga Diza Zaune gaban gawan ta kura ma gawan ido Tana jam Carbi Bakinta na Motsi da karfi kamar wacce ta Tabu Tsuri yayi mata da ido yana kallonta suma su Abba ita suka maida Hankali suna kallo Baba Habibu ya Girgiza kai yana Fadin"Tun da aka Fadi Rasuwar take Cikin wannan Halin..Ina Rumana tazo ta kamata zuwa Falo tasha Iska.."Yafada yana lekawa Falon yace akira Rumana wacce ke chan Bakin kofa Durkushe Tana kuka Aisha Bala ce ta Rikota Zuwa Dakin Abba ne yace mata ta kama Diza,su Fita Falo Za'a Fitar da gawan Mansur Zuwa Waje Cikin kuka da Hawaye ta isa Gareta ta kamata Tana Fadin"Taso muje Falo Diza..Taso..'Kamar wata Yarinyar haka ta kalleta kafin ta juya ta kalli gawan Mamsur Cikin Wata Murya tace"In je inyi me a falon Ruma..?Ga Mijina kwance anan ai ba inda Zani..!
Tafada Tana kwace hannuwanta Da Sauri Rumana ta sake Rikota Tana Fadin"Eh na sani Falo Zamu je..Shima chan za "a Fito da shi yanzu nan..'Sai da tayi Kamar ba zata tashi ba kafin Rumana ta Kamata ta Mike Dakyar da Cikinta Daya Bayyana Mastur yana kallonta yana kallon Cikin Jikinta sai yaji kamar Ya Fadi a wajen ya Dinga Rusa kuka.
Dakyar Rumana ta Fita da Diza Falo Lokacin Tuni kowa ya mike jin Z"a Fita da gawa ne zuwa Waje Diza bata ankara ba Taga an Dauko Gawan Mansur za"a Fita Dashi Waje Mastur ne ke gaba yana Rikeda Makaran Saman kafadansa yana jinsa Tamkar Bashi ba yana ji kamar acikin Barci ne komai ke Faruwa.
Diza Data ga Fita Za"ayi dashi Ta Nemi bin bayansu Tana Fadin"Na Shiga uku ina zaku kaimin Mijina kuma.?
Tafada Cikin Rauni da wani Sarewa Rumanace ta Rikota Tana Fadin"Diza ki bari..Mansur ya Tafi ya barmu..ki bari aje sallacesa Zuwa gidansa na gaskiya.."Da wani karfi ta Fizge hannunta Tana Fadin"uban na barin ne..?nace na bari yaci kaxa kaxansa Rumana Mijina za"a Daukemin shi araba ni dashi kuma kice na bari..?kina Haukane ko Kin Fara Shaye Shaye ne..? Tafada tana kwalalo mata Ido Cikin Kuka ta Fizge kanta ta Rumtuma da gudu Tana Fadim"Mijina..Kuna gani..Zasu FitaDashi..Wayo Allah na Shiga uki wani ya Taimakamin mana"Take Fada Tana kuka Gabadaya Falom sai ya Gauraye da kuka masu addu"a nayi masu Surutai nayi Umma ce da Mommy suka Rike Diza tana kuka Tana Tirjiya Tana kiran Mijinta Itama Rumana Kamar ta Shide ganin an Fita Dashi Daga Falon gabadaya yasa Diza ta saki kara ta Zube kasa asume Alokacin itama Rumana ta Sume,Hajja ma Ta Sume,haka su Maryama dasu Mardiya suka Sume suma sai Waje ya Rude mata na Gujen Gujem Dauko Ruwa suna Sheka musu inda akaci Sa"a Duk wacce aka Sheka ma Ruwa sai ta Farfado Tana Gunjin kuka Diza sai da Mutane suka Rirriketa Tana ta kuka da Ihun abarta Tabi Mijinta Aiya kuwa Tama Rude ga Jikin Tsufa ga Mutuwa Mutuwa ma irin Mutuwar Mansur Dole ta Dimauce,Inna karime ne ke Riketa da ita itama kukan take sosai kamar Ranta Zai Fita.

A Kofar gidansu aka Sallaci gawan Mansur ko awajen Sallar Tsaye kawai Mastur yake ammh Baya Fahimtar komai har aka Idar aka Fara Shirin Tafiya Allahu Akbar Mansur ya Dace Allah ya bamu irin nashi Dan"adam din da suka Sallaceshi sunfi 400 ba adadi kuma Dasu aka Rankaya Rakasa Gidansa na Giskiya a Makabarta Dambo Mastur a Motar Daddy sukaje Dukkansu,kuma Dashi da Baba Habibu da Baba Sule da Daddy suka Saka Mansur Cikin Kabarinsa Suna ji suna gani suka saka kasa suka Binneshi ta ko"ina Baba Habibu sai alokacin Yaji yana ta kuka ba Tsayawa Harda Shessheka sai da Baba Sule ya Rikosa yana Bashi Baki Mastur kadai ya Rage gaban gawan Mansur ya Duke ya Dafa Kasam kabarin yana ta mai addu"an Saduwa da mala"ikun Rahma yana Zubar kwallah,kwallah mafi Zafi da Ciwo acikkn Rayuwarsa,Dakyar Su Baba Habibu suka iya Janyensa Daga Kabarin Bayan an saka Budo awajen anjera Domin Shaida gane kabarin koda watarana anxo Ziyarsa.
Har suka Dawo Gida Mastur bai ma kowa mgana ba Shidai gashi nan ne kawai abubuwan ne yake ganinsu kamar mafarki suna zuwa aka Firfto da Manyan Dardume da Tabarmu Daga waje kuma aka Saka kujeru da Tantuna Saboda Rana Mastur Suna Daga Cikin Haraban suna Zazzaune su da su Daddy dasu Abba dasu Baba Sule Daddy Shi ya sanya aka Sauke Motocin Ruwan Gora dana Lemuka abincin kuwa Oder ya bada Dago Restaurant Har na Tsawon kwama bakwai nan da nan akayi ta Shiga da komai Cikin Gida ana Raba mutane Daganan waje haka yan Siyasan su Mansur suma suna ta Sauke Lemuka da Ruwa da su Snacks haka ana Ta Rabama Mutane masu ci daai sun Faraci ammh wadanda Mutuwar ta Shafa ko kallon Lamarin ma basayi ba Mastur dai gashi nanne yana amsa gaisuwan mutane Daga saman Lebensa kawai ba Domin yana Cikin Hayyacinsa ba nan da baki sai zuwa suke gaisuwa mata da Maza sai ga Zuga guda Daga ma"ikatan Diza da kuma wadanda Rumana take aiki Dasu asibitin Chika da kuma abokan aikinta yan Intemship duk sunzo gaisuwa Dayake Aisha Duk ta Kirasu ta gayamusu Mansur Sulaiman Doguwa kanin Mijin Rumana muhammed wamako ne.
Koda suka shiga Cikin Falon Hajja Zukata sun gama Raunana Gabai sunyi Sanyi,Idanuwa sun gaji da Zubar kwallah sun komaa ma na Zucci Zuwa Lokacin Tuni Diza ta Daina kuka da Ihu sai Tayi Shuru kawai Duk wanda yayi mata gaisuwa ta amsa ta gama Shaida cewa Mansur ya Tafi ya Barta Tafiya ta Har Abada hakama Hajja Ta saka ma Ranta Rumana ma haka kannensa ma sai kukam Zucci kawai suma ga ababen sha da ci ammh ba wanda ya Kalleshi Sai Dai Dai,basu Tashi Daga wajen ba sai da sukaji kiran Sallah kana masu Kuxarin suka Mike Domin gabatar da Sallah Harda wadanda basu da Kuzarin sun mike Domin sun yarda kuma sun amince cewa Allah Daya Hallicesu Shi ya karbi Mansur suma din basu yi Tsaiko kuma basu jinkiri ba Ballatana gaggawa akowani Lokaci suma Zata iya Riskansu suna masu kai kukansu ga Allah da kuma Rokan ma Mansur Yafiya da Gafara wajen Allah.
Haka ta Faru su Mastur shima yayi addu"an neman gafara ga Mastur acikin Sujjadansa kamar Zai Cire bakinsa Tsoron Allah ya karama Kamashi yau ga watarana da Mansur zai yi kwanan kabari ba Diza ba Mastur a gefensa ba Hajja ba Baba Habibu Lalle Rayuwa Bawa ba abakin komai yake ba Allah ya Jadaddama Rahma gareka Mansur Allah ya jikan iyayanmu da suka Rigamu gidan gaskiya Allah yasa in tamu tazo mu cika da kyau da imani Ameen ya Allah.

*Shakira.*
1/1/22, 18:55 - Maryam Badmsi: *SS...34*
Chapter 74 · 0% Book details