← Book details Mafarkin Farida Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 62 OF 95

Sashe 62

Mafarkin Farida Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tuni Yan Sanda sukayi gaba da Malam Dan Haru tare da cewa Hajiya kema ki Zama cikin shiri zamu nemeki,Yan Jarida zasu magana da Hajiya ta fisge abar daukar tayi jifa da ita ta tashi ta tafi gidan yayanta tana kurma Ihu.
Gaba daya Gidan biki ba Dadi,Farida tana Jin labarin komai wani kukan ya karu a Kan na Baya,gashi ance aure ba fashi, Ranar daurin aure da safe aka kawo Manal a wasu Shegun motoci Ana Mata kirari ga mace Daya me take Mata Baya da ita Suka shiga gidan,wani irin Material Manal ta zuba na Gaban kwatance sai kallonta akeyi Jakarta ma rike Mata aka Yi tafi karfin ta rike,Jikin Annatu ta fada su Hajiya Sharifa duk Suka saki Baki,Tace nahigai yanzu Kece Haka Manal kin Kara girma kinyi kiba kinyi kyau Haka kalli Fatarki Manal Kamar jini zai fito gaskiya angonki ya iya kiwo,larai tace yo ba Dole ba irin wannan koriyar Hinkafa da suke ci da yaluwa harda da ja,ga nama iri iri,Manal tana Dariya tace tare muke da shi fa,Sharifa da sauri Tace Allah? Iyye Wato bazai Zo ma ya Gaida surukansa ba ai Hike Nan ya kyauta ah nace kice Masa ya kyauta,suna Haka sai ga Fuzail kayansa ruwan kwai irin na Manal Amma nasa shadda,Nan take Sharifa tace anko sukayi ahe lobayya,Fuzail yaji Sanda tayi Gulmar ya fuske,gaba Daya kamshi ya turare su,Durkusawa yayi tare da gaisar da su suka amsa da Fara'a sai kunyarsa suke ji Wai suruki,Hajiya Sharifa tace ah Yasin abinku Ras duk Kun samu nutsuwa kaima kibar ahe kayita,Dariya Fuzail yayi kawai Annatu ta wani boye fuskarta Wai kunya,Masu take Masa baya suna daga kofa suna jiransa,Yana Gaida su ya Mike tare da riko Hannun Manal a gabansu,kunya ta Kama su Annatu ji suke Kamar su nutse suna ji yace sai karfe nawa zanzo daukanki? ,kwace Hannunta tayi Tace ba kwana zanyi ba na ebo kaya fa,Haka Mukayi Dake? Shike Nan Ni bazan ga Uwata ba,Baki Annatu ta bige Mata Tace biyar na yamma na yi azo a tafi da ita me zata Yi a Nan biki yau za ayi a Gama kwanan me Zaki Yi ga Baki ga Hanci,yaushe zaku koma? Sharifa tace jibi Inshaallah da Sassafe,yace to ba damuwa Allah ya kaimu.

Yana fita Ya wuce wajen daurin aure,Yayin da Yan Sanda tun jiya da daddare suka sa Malam Dan Haru ya karya asiri Nan take,tun a daren Tanko yake Jin haushin Kansa me yasa ma zai auri wacce Bata kaunarsa,kwanan bakin ciki Tanko yayi Yana tuna irin wulakancin da Farida ta Masa,Ranar daurin auren ma da kyar ya shirya ya fito jikinsa ba kwari Haka suka Zo da su Sani,Kowa ya hallara tare da wakilan ango Dana Amarya da Kuma wakilin Maimartaba Sarki Abban Ameer,Haka Kawai Tanko a wajen Ana Shirin Fara khuduba yace a tsaya na fasa Kar a daura na fasa wallahi tunda Bata kaunata bana sonta nima,me zakayi da Wanda baya sonka,duk Wanda ya nuna Bai kaunarka Bai kamata Kai kaci gaba da sonsa ba ko ta karfi ka rabu da shi,ko anyi auren Nan ba inda zai je a Bata Wanda take so ni Tanko na janye Allah ya kawo Mata Dangote ta Aura.

Malam shima Bai matsa ba Ana ta mamaki dama Amaryar Bata so,Fuzail yace Tanko kalau kake Kuwa? Tanko yace kalau nake Ranka ya Dade ayi min afwa wallahi na fasa har abada bana sonta Kamar yanda Bata kaunata,Abban Ameer me saukin Kai yace to yanzu ya za ayi Belloti Yana kusa yace Ni Ina sonta dama muna gaisawa idan tana so na a daura Dani,Tanko Yace ni Kuma duk abinda na kashe na bar maka a matsayin kaine kayi Sadaki Kawai zaka biya,har lefen na bar maka,Amma ba ita na barwa ba Kai na Bawa bawan Allah sabo Ni idan mutum Bai kaunata kwandalata bazai ci ba,Belloti yace Nima Haka nake bawan Allah zuciya ce Dani,sai da akayi Dariya a wajen, Malam da Kansa ya Nemo Farida har dakinta yace ki daina kuka ki godewa Allah Tanko yace ya fasa da kansa,Ihu Farida ta saki na murna,Malam yace ga Belloti Dan garin su Manal Kinga wannan mun San asalinsa sosai duk da cewa yanzu halin mutum ake so a duba ba gidansu ba ya kika gani? Farida ta rufe Ido tace gwara koma waye Malam,Ki daina cewa gwara Koma waye Haka zakice Allah yasa Haka shine mafi alkhairi,Alkhairi Allah ake Nema Farida,Farida Tace to tana murna a ranta tana zagin Tanko.
Komawa Malam Yayi akace Belloti ya kawo Sadaki,Tanko yace Nawa aka yanke Zan biya Masa,Fuzail ya kalli Tanko Yana mamaki,Dan kudin Tanko da ya Tara ragowar su kenan dubu Hamsim Kuma dubu Hamsim aka yanke Nan take Tanko ya zaro ya biyawa Belloti,Belloti ya dinga Mamaki abinda Tanko yayi ya girgiza kowa sannan ya birge mutane wannan yasa kowa yaji kaunar Tanko a ransa,Tanko Farin jini yayi aka dinga Kallonsa Ana yaba masa,Baki dubu sai Allah San Barka ake Masa,Belloti ba walliyyai yace Kar a damu zai zaba a Nan Baida matsala a gidansu,Malam duk da Haka sai da Yaja Belloti gefe yaji sana'arsa da inda gidansa yake, sannan yace bazai yuwu ba sai Dangin Belloti sun sani ko a waya ne.

Belloti sai ranar ya lalubi Babarsa yasan itace zata Goya Masa baya,tunda taji Danta yana nan da Rai murna tasa Tace yaushe zaka dawo yace Gwaggo sai Kun Amince an daura min aure Haka ya Dan Bata labari a takaice,murna yasa Gwaggo ta Kira Baban Belloti shima sabo da Murna yace Matukar Belloti zai dawo Kuma yaji Baban Manal ne ya bashi 'ya ai sai godiya yace a daura a wakilce su.
Malam hankalinsa ya kwanta
Nan Kuma aka nadawa Belloti wakilansa tare da Daura Auren Farida da Muhammad Bello Wato Belloti,Belloti ya tsinci dami a kala a banza yazo daga sama duk wannan jarabar fafutukar da Farida keyi Ashe Belloti ne,Belloti burinsa ya cika ya samu Yar birni wayayya me iya love hirarsu da sukeyi kullum a Majalisa da su Lawi kenan.

Belloti ya Kira su Lawi a waya yace to fa Ni nayi gaba Allah ya amsa ba Manal din ma Allah ya bani ba Yayarta na samu,shi yasa Idan zaka roki Allah ka rokeshi da Babban masaki sai ya bani Yayar Manal ma wacce tafi Manal wayewa sai dai Ita ba wata kyakyawa bace gata Nan dai ba laifi sai iya gayu,Lawi yace Yar Mai ce? Belloti yace tabbas akwai shiga kanti,ka shiga Uku Belloti siyen manta kadai sai ya karya ma jari,Belloti yace ba komai akan ta zauna min a baka gwara ko na kanti ne farin ta siya ba matsala Ni tayi min,Malam Dan Haru kuwa tuni an shigar da shi Kotu zata yanke Masa hukunci,Yan biki maza da Mata labari ya watsu Ana ta mamaki Ana yabawa Tanko,Manal ta dinga mamaki Wai Belloti Bata San Bellotinta ya goge ba,bayan mutane sun watse Fuzail ya kirata a waya yace tazo waje zai tafi,Manal tana fita taga Ango Belloti Dake Bai San za a daura Masa aure ba da kananan Kaya yazo wajen yasha shegen black jean dinsa me Dan kyau,da kyar ta Gane shi,Yana ganin Manal sai da zuciyarsa ta kusa bugawa sabo da tsananin kyan da tayi,da ganin Yanda ta wani goge ta waye ta zuba kyau ga Kaya na nunawa sarki,tun a Nan yasan Manal tafi karfinsa,Fuzail ya kalla ya sake kallo da motoci da masu take Masa baya ga Dogarai,Nan Belloti ya dinga kallon Naira da Mulki.

Manal ce ta Masa Magana Belloti Ango Kaine tayi Wajensa sai suka koma Fulatanci suna ta yaren,Kishi ya Kama Fuzail yaji labari ance tsohon Saurayin Manal ne,sai ya Shiga mota Kawai yayi tafiyarsa Yana ta Fushi zuciyarsa tana Jin zafi yanzu shike Nan tana can tana yiwa Belloti murmushinta me kyau Wanda shi ya kamata ya kalla,Manal sai juyowa tayi taga ya tafi tuni,sai da suka Sha Hira da Belloti sannan ta shiga gida ta Iske Farida cikin kayan lefenta ta Sha lace brown and milk,tayi kyau Tace Manal Dj za a kawo fa Yanzu su Walida Kawayena zasu Zo ku shirya tikar rawa,Murmushi Manal tayi Tace Farida ki rage murnar Nan kiyi Addua sannan tam,da Masifa Farida ta yo Kan Manal da abani Tanko gwara na auri ko waye wallahi,Wannan Bellotin yafi birgeni sau dubu akan Tanko,dama ai tsohon saurayinki ne nasan kishi kike,Waiyazubillah da Auren Nawa? Me zanyi da Belloti Ni Kam da Ina sonsa da tun a Kauye ban aure shi ba,Belloti shine Silar gudowa ta Birni amma Allah ya Baki Hakuri.
Farida tana shafa jambaki Tace Ameen yanzu zai kaini wajen Hajiya naji halin da take ciki,su Walida zasu Zo ki kula da su Dan Uwarki Saura ki tsaya mulki ke ga matar Yarima to su Walida ne kin San halin Kawayena gogeki zasu Yi,Manal Tace kutmar wa suka Isa su goge wallahi da sun jama kansu,Mrs Fuzail Guda ai kallo na ma sukayi Basu Isa ko kallon banza su min ba,Ance Miki Manal din da ce me Awara? Ko yanzu na Zo daga Kauye? Farida ta girgiza Kai Naga yanzu kin sake fetsarewa wallahi Zaki San Ni ba Sa'arki bace,Manal Tace ke kin Sanni tun a baya duka nake Miki yanzu ma badan Allah yasa Ina tsoro ko Ina da ciki ba Hmmm...

Dariya Farida tayi Tace to Manal munji kina da cikin Fuzail sai me? Anji kin auri me kudi so what? Farida tana fita motar Belloti ta shiga wacce Bata San ta Uche ba ce ya figeta sai wajen Hajiya wacce ta rame lokaci Guda sai Ido zuru zuru kamar tayi zawon wata Guda,Taga Faridanta ta Sha wanka a sanyaye Tace An daura da Tanko ko? Farida tace a'a da wannan Bellon aka Daura Dan gayu Wanda yazo gidanmu Wanda jiya Muka zo da shi ya kawo Ni da dare? Hajiya Tace Alhmdllh gwara shi,Ina su Falaqi su Sa'iha? Farida Tace sun tafi Wai gidan kwalliya Falaqi Yana wajen Yaya Yazed.
Chapter 62 · 0% Book details