Sashe 51
Mafarkin Farida Complete Hausa Novel · about 8 min read
Malam Farida ya sawa takunkumi ya takura ta ya hanata fita duk abinda zata siya Yana Bata kudin sabo da kar taje ta bi Namiji sabo da sakakin Iyayenmu ace Always pad ma wasu Iyayen Basu iya siyawa yaransu Mata sai dai su Nema da kansu bare su pant da su Bra,wasu Iyayen Mata ne na yanzu idan Uwa tana Aiki ko tana Business take iya siyawa yaranta wannan wasu Kuwa ba abinda ya damesu,ko anga yarinya da Abu baza a tambayeta a Ina ta samo kudin ba,Akwai bukatu na rayuwa da yawa da Iyaye suna da halin da zasu siyawa Yaransu wasu abubuwan na bukatu musamman Yan Mata Amma ba a iya hakan,Month yayi Dole yarinya tana bukatar Always amma sai dai tayi fafutuka ta siya da kanta Dole ta dinga Bari mazaje suna latse ta tana samun kudi,Wannan Malam ya tuna a baya tunda baida shi ba yanda zaiyi Amma yanzu Allah ya Buda Masa shi yasa ya dage duk wata har kudin Kati yake bawa Farida Su Masatura Basu fara rike waya ba dama Farida ce Yan matan,Duk da Haka Farida Bata gode ba,ganin Ana takura Mata sai ta faki Idon Malam da Yazed ta gudu a hakan ma Sai ta kwashe kwana biyu Uku ba a ganta ba sai anyi cigiya an gaji har gidajen Radio Hankalin Kowa ya tarshi Har Hajiya Kuwa yanzu ita kanta Halin Farida ya dameta taci kuka har ta gode Allah duk Randa Farida ta so dawowa gida sai ta samu saman bola a wata Unguwar taje ta zauna a cikin Bola,mutane su tsinceta budu budu da ita a samu da cigiya a dawo da ita gida da wannan Farida ta tasa kowa ya Gane Aljanu gareta Wanda suke saceta Wanda karya takeyi salon da Yan Mata Suka dakko yanzu kenan wasu,sai su gudu yawon duniyar su,su canja suna a bariki da komai sai sun tashi dawowa a dinga tsinto su cikin kango ko bola ko wani waje marar kyau su fake da Aljanu ke sace su ,abubuwa zasu dinga Yi a gida Kamar masu Aljanu alhalin karya suke dai dai ku ne masu na gaskiya.
Wannan salon da Farida ta dakko kowa ya yarda akace shi yasa Bata ji Ashe Aljanu ke sata,Kawayenta a boye zasu kirata waje su Bata su Apples sai Kawai anyi bacci ta zube a saman katifar ta da yawan gaske tayi bacci,da safe Hajiya idan ta shigo tashinta sai aga Apples a katifa da yawa Farida Kuma tana ta sheka bacci bayan Kuma an San Bata fita yanzu ko aikenta ba ayi sai in Aljanu sun sace ta,Hajiya yau ma taga farida tafi sati ko Kofar gida Bata leka ba Amma sai ga Green Apples da su Yinibi da yawa a gefen katifarta,Hajiya ihu ta kurma ta Kira Malam da Yazed lokacin komai a kunnen Farida Amma sai tayi likimo tana ji Suna ta CeCe kuce,Malam ya fara zargin Farida sabo da tsohon Dan tsubbu ne duk irin karyar Nan sun Sha bugata a baya.
Yazed ma tun Yana yarda ya fara tantama,Sabo da Yan sa idon Unguwa suna Masa Gulmar Kawayen Farida suna zuwa har gida,Malam ne ya kalli Apple din tare da kallon Hajiya yace sai kuci tare tunda komai tare kuke Yi ai Bai kamata kiji tsoro ba,Hajiya ta dafe kirji tare da ja baya tace Allah ya kiyaye min Rannan da mutanen boyen Suka kawo Mata na dauki Daya naci yini nayi da ciwon Kai ba ruwana taci abarta ita kadai,Malam yace ai kece mutanen boyen gaskiya zata Yi halinta wallahi Ina Nan Ina Bincike duk Sanda zargina ya Zama gaskiya Farida baza ta Kara sati ba sai na Daura Mata aure,Falaqi ya fara tsalle zamu Sha biki yeeeweeeee,Hajiya duka ta durmawa Falaqi a gadon Baya,Malam ya fisge Falaqi daga Hannun Hajiya Suka fita abinsu.
Bayan Farida ta farka Hajiya tace Farida na kasa Gane inda kika sa gaba,yanzu ma Ni kaina boye min abubuwa kike a gidan nan,Waya ma baka Yi a Gaban kowa duk an kasa Gane kanki,Farida kina sani kuka Lokuta da dama karki watsa kanki Farida Mijin aure kika Ce Zaki Nemo,Baki Farida ta turo tace nifa kin takura min Allah ya gani,Mijin Aure mutum shi yake nemowa Kansa ba Allah ne ke kawo shi ba,duk duniyar da yake sai Allah ya kawo silar da zata hada ku,Ita Manal Gashi a banza ta samu har gida Allah ya kawo Mata shi,Dan Ubanki wallahi bazan yafe Miki ba idan har kika shiga harkar banza daga Ana so a samo Miki me kudi na rufin asiri sai ki kauce hanya ki fada Harkar banza,tun kina shafa Mai me kyau kina Yin Dan kyau kince sai kin koma baturiya jibi yanda kika maida Fatarki,Dan Ubanki irin wannan hasken baya yiwa Mata kyau duk Fatarki ta goge tayi ja ja Haka Ana ganinki anga Yar duniya kawai,Tsaki Farida ta ja ta tashi tayi tafiyarta,Farida Ni kike yiwa Tsaki? Ni Farida? Duk abinda nake kokarin Yi akanki,Dan kutmar......ub... Zaki zo ki sameni wallahi sai kinci burar........abin sisi na daina Miki tunda Baki da mutunci Baki San arziki ba,Hajiya ta sake gallawa Harara tare da tafiya tana kunkuni,Hajiya taga Farida yanzu Fadi in fada suke da ita Kuma duk Maganar da taga dama Haka take fadawa Hajiya direct sannan Bata Isa ta sata wani Abu tayi ba.
Washe Gari bakin cikin Farida ne ya sawa Hajiya Zazzabi ta kwanta ga su Masatura suna school ba kowa sai Farida,Kira Hajiya ta kwala Mata Tace Farida Dan Allah share dakin Nan da gidan Nan kiyi mopping yanzu an Mana Tiles kazantar mu zata Yi yawa,Dama Masatura ke gyarawa Kuma tana school,Farida ko kallon Hajiya Bata Yi Wayarta taci gaba da latsawa tana Chatting tana faman Dariya,Sake maimaitawa Hajiya tayi har sau Uku sai da ta gaji tana daga kwance ta dannowa Farida Ashar sannan Farida Tace Nifa na gaji gaskiya da can ni nake aikin a gidan,Farida karfa ki manta Ni na Haife ki,Farida ta tabe Baki ta Mike tare da shigewa dakinta sai wurin karfe biyu Farida ta Gama abinda take ta fito ta danyi shara sama sama ta koma dakinta tana Shirin tafiya gidan gala yau wani sabon mawaki zai zo yayi Show gashi ance Drivern Gomna zaizo zai bada kyautar mota Dole suje su Sha kallo,Kwana Uku za ayi Ana wasan,wani Danmajisar Tarayya shima zai je ya watsa Naira Farida Shiryawa tayi tsaf da Jakarta,waya sukayi da babbar kawarta Walida tazo ta Bayan gida Farida ta jefa Mata Jakarta ta katanga,a Gaban Hajiya Kuma tazo ta dauki Buta ta shiga Toilet,Hajiya tana shiga kitchen Farida ta fice da sauri ta bar gidan,Yazed dama Yana sa Ido a Idonsa yaga komai har jefa jakar kayanta da Farida tayiwa kawarta Suka shige Napep suka tafi,Yazed Malam ya sanarwa,Hajiya Kuma taga Farida Shuru Shuru ta gaji ta leka Bayi wayam,ta leka ko Ina Bata Nan,Kuka Hajiya ta barke da shi kawai tana wayyo Aljanu Kuna cutata a rayuwa,me 'yata tayi muku zaku kangarar min da ita,bacin Rai yasa Hajiya ko Malam Bata jira ba ta figi mayafinta Sai gidan Malam Dan Haru.
Sai da Malam Dan Haru ya Gama bincikensa sannan ya kalli Hajiya yace Yarki ta kusa aure,ki ma kwantar da hankalinki wannan yawon da take karya take Bata da wasu Aljanu wannan hanyar itace silar samun mijinta Kuma me kudi burunku,Baki Hajiya ta washe tace Alhmdllh yanzu dai na daina damuwa ko? Malam Yace kwarai ma kuwa yarki itama zata Dace kwana Nan,Hajiya tace Malam a dinga samu a Addua dai dan Allah da Wani dafa'i da jalabi duk a dinga Dan hehehe Bamu cikin karamar da Allah ya muku.
Malam Dan Haru yayi Murmushi yace har kin tuna min jiya 3am mun shiga meeting da bakaken Aljanu wani babban Sanata a cikinsu,Hajiya Tace au Suma suna da Yan siyasa? Sosai ma ai su siyasarsu ma tafi tamu Zafi, su da har yanzu zabe suke na Kato bayan Kato ba a daina ba, shekarata goma Ina zabe a wani yanki nasu na Aljanu,sai Wani Gomna me ci a yanzu yace zai tsai Dani takara ganin za ayi rikici da zaratan Aljanu sai nace bana son tashin hankali a barsu su Yan jinsun su suyi,Hajiya ta rike Baki tana mamakin shaharar Malam Dan Haru,Malamin yaci gaba da cewa ai sanatan da yaro na ne shi nake aika Yana binne min asiri idan nayiwa wasu,yo na kishiyarki ma da kika taba Kora ai shi ya binne asirin,Hajiya tace kace Ina gaishe shi Dan Allah,zai ji...zai ji cewar Malam,Jiya Muna Meeting sai da ya tambayeki yace Ina kika shige ne,ai yace Bai taba ganin macen da take da nasibi a rayuwa ba irinki,kina da nasarori a rayuwarki Amma idan kina sawa Ana Miki Addua,Hajiya ta sheke da dariya tare da Furta Haka na taso tun Ina yarinya bana ci baya,kaga tallan goro tunda na fara shi ban taba kwantai ba har aka min aure,Lokacin da Gyatimata tana min Alalar siyarwa kafin na fita talla an kusa siyewa,sannan duk Saurayin danayi ko ya gudu da kafarsa yake dawowa,Malam yace kinji ko sai Nan gaba ma Zaki ga yanda ci gaba zaizo Miki,wallahi kinji na rantse yarki da motoci sun Kai takwas za a rako Mijin da zai aureta,Ummi ta kwala ihun murna tana cewa mun Karo wulakanci na daina hanata yawo yanzu,Malam yace ya Kuwa Yar kishiyar Taki a can dakinta?
Wannan salon da Farida ta dakko kowa ya yarda akace shi yasa Bata ji Ashe Aljanu ke sata,Kawayenta a boye zasu kirata waje su Bata su Apples sai Kawai anyi bacci ta zube a saman katifar ta da yawan gaske tayi bacci,da safe Hajiya idan ta shigo tashinta sai aga Apples a katifa da yawa Farida Kuma tana ta sheka bacci bayan Kuma an San Bata fita yanzu ko aikenta ba ayi sai in Aljanu sun sace ta,Hajiya yau ma taga farida tafi sati ko Kofar gida Bata leka ba Amma sai ga Green Apples da su Yinibi da yawa a gefen katifarta,Hajiya ihu ta kurma ta Kira Malam da Yazed lokacin komai a kunnen Farida Amma sai tayi likimo tana ji Suna ta CeCe kuce,Malam ya fara zargin Farida sabo da tsohon Dan tsubbu ne duk irin karyar Nan sun Sha bugata a baya.
Yazed ma tun Yana yarda ya fara tantama,Sabo da Yan sa idon Unguwa suna Masa Gulmar Kawayen Farida suna zuwa har gida,Malam ne ya kalli Apple din tare da kallon Hajiya yace sai kuci tare tunda komai tare kuke Yi ai Bai kamata kiji tsoro ba,Hajiya ta dafe kirji tare da ja baya tace Allah ya kiyaye min Rannan da mutanen boyen Suka kawo Mata na dauki Daya naci yini nayi da ciwon Kai ba ruwana taci abarta ita kadai,Malam yace ai kece mutanen boyen gaskiya zata Yi halinta wallahi Ina Nan Ina Bincike duk Sanda zargina ya Zama gaskiya Farida baza ta Kara sati ba sai na Daura Mata aure,Falaqi ya fara tsalle zamu Sha biki yeeeweeeee,Hajiya duka ta durmawa Falaqi a gadon Baya,Malam ya fisge Falaqi daga Hannun Hajiya Suka fita abinsu.
Bayan Farida ta farka Hajiya tace Farida na kasa Gane inda kika sa gaba,yanzu ma Ni kaina boye min abubuwa kike a gidan nan,Waya ma baka Yi a Gaban kowa duk an kasa Gane kanki,Farida kina sani kuka Lokuta da dama karki watsa kanki Farida Mijin aure kika Ce Zaki Nemo,Baki Farida ta turo tace nifa kin takura min Allah ya gani,Mijin Aure mutum shi yake nemowa Kansa ba Allah ne ke kawo shi ba,duk duniyar da yake sai Allah ya kawo silar da zata hada ku,Ita Manal Gashi a banza ta samu har gida Allah ya kawo Mata shi,Dan Ubanki wallahi bazan yafe Miki ba idan har kika shiga harkar banza daga Ana so a samo Miki me kudi na rufin asiri sai ki kauce hanya ki fada Harkar banza,tun kina shafa Mai me kyau kina Yin Dan kyau kince sai kin koma baturiya jibi yanda kika maida Fatarki,Dan Ubanki irin wannan hasken baya yiwa Mata kyau duk Fatarki ta goge tayi ja ja Haka Ana ganinki anga Yar duniya kawai,Tsaki Farida ta ja ta tashi tayi tafiyarta,Farida Ni kike yiwa Tsaki? Ni Farida? Duk abinda nake kokarin Yi akanki,Dan kutmar......ub... Zaki zo ki sameni wallahi sai kinci burar........abin sisi na daina Miki tunda Baki da mutunci Baki San arziki ba,Hajiya ta sake gallawa Harara tare da tafiya tana kunkuni,Hajiya taga Farida yanzu Fadi in fada suke da ita Kuma duk Maganar da taga dama Haka take fadawa Hajiya direct sannan Bata Isa ta sata wani Abu tayi ba.
Washe Gari bakin cikin Farida ne ya sawa Hajiya Zazzabi ta kwanta ga su Masatura suna school ba kowa sai Farida,Kira Hajiya ta kwala Mata Tace Farida Dan Allah share dakin Nan da gidan Nan kiyi mopping yanzu an Mana Tiles kazantar mu zata Yi yawa,Dama Masatura ke gyarawa Kuma tana school,Farida ko kallon Hajiya Bata Yi Wayarta taci gaba da latsawa tana Chatting tana faman Dariya,Sake maimaitawa Hajiya tayi har sau Uku sai da ta gaji tana daga kwance ta dannowa Farida Ashar sannan Farida Tace Nifa na gaji gaskiya da can ni nake aikin a gidan,Farida karfa ki manta Ni na Haife ki,Farida ta tabe Baki ta Mike tare da shigewa dakinta sai wurin karfe biyu Farida ta Gama abinda take ta fito ta danyi shara sama sama ta koma dakinta tana Shirin tafiya gidan gala yau wani sabon mawaki zai zo yayi Show gashi ance Drivern Gomna zaizo zai bada kyautar mota Dole suje su Sha kallo,Kwana Uku za ayi Ana wasan,wani Danmajisar Tarayya shima zai je ya watsa Naira Farida Shiryawa tayi tsaf da Jakarta,waya sukayi da babbar kawarta Walida tazo ta Bayan gida Farida ta jefa Mata Jakarta ta katanga,a Gaban Hajiya Kuma tazo ta dauki Buta ta shiga Toilet,Hajiya tana shiga kitchen Farida ta fice da sauri ta bar gidan,Yazed dama Yana sa Ido a Idonsa yaga komai har jefa jakar kayanta da Farida tayiwa kawarta Suka shige Napep suka tafi,Yazed Malam ya sanarwa,Hajiya Kuma taga Farida Shuru Shuru ta gaji ta leka Bayi wayam,ta leka ko Ina Bata Nan,Kuka Hajiya ta barke da shi kawai tana wayyo Aljanu Kuna cutata a rayuwa,me 'yata tayi muku zaku kangarar min da ita,bacin Rai yasa Hajiya ko Malam Bata jira ba ta figi mayafinta Sai gidan Malam Dan Haru.
Sai da Malam Dan Haru ya Gama bincikensa sannan ya kalli Hajiya yace Yarki ta kusa aure,ki ma kwantar da hankalinki wannan yawon da take karya take Bata da wasu Aljanu wannan hanyar itace silar samun mijinta Kuma me kudi burunku,Baki Hajiya ta washe tace Alhmdllh yanzu dai na daina damuwa ko? Malam Yace kwarai ma kuwa yarki itama zata Dace kwana Nan,Hajiya tace Malam a dinga samu a Addua dai dan Allah da Wani dafa'i da jalabi duk a dinga Dan hehehe Bamu cikin karamar da Allah ya muku.
Malam Dan Haru yayi Murmushi yace har kin tuna min jiya 3am mun shiga meeting da bakaken Aljanu wani babban Sanata a cikinsu,Hajiya Tace au Suma suna da Yan siyasa? Sosai ma ai su siyasarsu ma tafi tamu Zafi, su da har yanzu zabe suke na Kato bayan Kato ba a daina ba, shekarata goma Ina zabe a wani yanki nasu na Aljanu,sai Wani Gomna me ci a yanzu yace zai tsai Dani takara ganin za ayi rikici da zaratan Aljanu sai nace bana son tashin hankali a barsu su Yan jinsun su suyi,Hajiya ta rike Baki tana mamakin shaharar Malam Dan Haru,Malamin yaci gaba da cewa ai sanatan da yaro na ne shi nake aika Yana binne min asiri idan nayiwa wasu,yo na kishiyarki ma da kika taba Kora ai shi ya binne asirin,Hajiya tace kace Ina gaishe shi Dan Allah,zai ji...zai ji cewar Malam,Jiya Muna Meeting sai da ya tambayeki yace Ina kika shige ne,ai yace Bai taba ganin macen da take da nasibi a rayuwa ba irinki,kina da nasarori a rayuwarki Amma idan kina sawa Ana Miki Addua,Hajiya ta sheke da dariya tare da Furta Haka na taso tun Ina yarinya bana ci baya,kaga tallan goro tunda na fara shi ban taba kwantai ba har aka min aure,Lokacin da Gyatimata tana min Alalar siyarwa kafin na fita talla an kusa siyewa,sannan duk Saurayin danayi ko ya gudu da kafarsa yake dawowa,Malam yace kinji ko sai Nan gaba ma Zaki ga yanda ci gaba zaizo Miki,wallahi kinji na rantse yarki da motoci sun Kai takwas za a rako Mijin da zai aureta,Ummi ta kwala ihun murna tana cewa mun Karo wulakanci na daina hanata yawo yanzu,Malam yace ya Kuwa Yar kishiyar Taki a can dakinta?