Sashe 95
Yar Tsanar Zinari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tsira mashi ido tayi sai dai sam ta kasa gane shi,
Nan ma kara girgiza kai tayi,
"To wannan da kike gani Yusuf ne,Yusuf dai da kika sani tsohon mijin ki shine,"
Wani irin zaro ido tayi tana kara zuba mai ido,sai yanzun abin ya zo zuciyar ta,tabbas shine,
Muryarta har rawa yake yi wurin fadin "Yaya me ya same shi?
" Abinda ya shuka ne yake girba,Salma shi yasa nace Allah yana son ki,domin ya gama maki duk rahama da zai maki,amma kina ƙoƙarin yi ma kanki mummunan hisabi,
Ki duba irin jinyar da Baba yayi duk da baƙi nan,komai sai an mashi,har zuwa karshen rayuwar shi yayi mutuwa irin ta rashin jin daɗi wannan ma wani ishara ce,ki duba mutuwar Mama da ko haɗuwa Allah bai nufa za ku yi ba duk da irin burin haɗuwar da kuka ci ma juna,ko samu taga fuskar ki ta nime yafiyar ki ba tayi ba,sannan ki duba wannan na gaban ki na yanzun,ko magana baya iya yi,gabaɗaya wurin bahayarshi ya zazzago kashi baya iya tsayawa,fitsari baya iya tsayawa,wurin tsutsotsi ne kawai ke fita suna rarake wurin,shi kuma ke zaki ce a kanshi,
Ke kuma me ya same ki Salma,Ubangiji ba tsoronki yake yi ba da kika tafi yawon duniya da sunan fushi kina ta aikata barna,amma bai hukunta ki ba sai ma ya baki miji na gari wanda zai iya sadaukar da komai domin ke,
Kin san ma kuwa cewar shi ya bada Kodar shi daya aka sai ya maki"
Da sauri ta gado jikakkun idanunta ta daura a kanshi,
"Kwarai kuwa,domin a lokacin an duba namu a ciki babu wanda ya maki,kuma idan har aka bata lokaci to kina iya rasa ranki saboda coyon dake kanki,shi ya yace zai baki nashi ba tare da tunanin komai ba,kuma ya bada,
Kin ma san irin rashin lafiya da yayi a lokacin,domin kuwa wannan da kike gani a kwance so yayi ya kashe shi ta hanyar dukan shi a ciki,
Kiyi tunanin irin raɗaɗi da azabar daya fuskanta,A ranar da za'ayi aikin a ranar Kakar shi da tayi shekara goma sha ɗaya a kwance a ranar ta tashi,ranar da suka dauki tsayin shekaru suna addu'a da fatan zuwan ta,amma haka ya hakura ya kwanta aka yanka jikin shi aka cire wani bangare nashi mai muhimmanci aka saka maki,ba tare da sanin shin zai kara buɗe ido ko bazai iya ba,ko kuma shima tafiyar ke nan,ya watsar da komai nashi da burin shi ya zaɓe ki,
What sannan har kike fadin baya son ki dan kawai bai faɗa maki cewar yana son ki ba,
Wallah kin ban kunya!kin bani kunya Salma! Amma fa babu komai rayuwa ce kuma duniya ce ta isa kowa riga da zani,amma ki tuna da wannan misalin dake gaban ki,yanzun zabi ya rage naki"har ya juya ya juyo ganin yanda take sharbar kuka"muje na kaiki gida"
Bin bayanshi tayi,har cikin mota yana jin yanda take rusa kuka sai dai ko alamar dakatar da ita bai yi ba,gara tayi ko zai taimaka wurin dawo da ita haoyacin ta,
A ƙofar gida ya ajiye tana fita yaja motar shi ya bar kofar gidan.
Babu kowa a tsakar gidan dan haka dakinsu ta shiga ta zauna ta lungun gado tana cigaba da kuka,
Ganin Yusuf a yau a haka kuma ya matukar tayar mata da hankali,Yusef dan gayu mutum mai ji da iya wanka da saka kaya,yau sai gashi kwance ko riga babu,duk irin kudin da yake kashe ma fatar jikin shi sai gashi yau fatar ta mutu ta yakushe ko gane shi ba'a yi,
To yanzun ina duniyar daya nime,ina arzikin da ya tara,ina kuma lafiyar da yake takama da shi,duk basu amfana masa komai ba,gashi kwance tamkar gawa,zai tayi yabar komai,
Suraj zuciyar ta ya ambaci sunan,tabbas Allah ya bata shine domin ya kara gwada imanin ta,sai gashi duhun kai yana nima ya kai ta ga aikata aikin da na sani,
Idan har zata tuna irin zaman ta da tayi da Yusuf da kuma kwana daya kawai da tayi da Suraj sai yanzun take ganin Allah ne ya amsa addu'ar ta ta bata miji wanda zai iya da ita har ma ya fita saboda ya tsayar da ita a wuri da,amma makantar zuci ya shafi ido,
Tabbas ta cancanci da a kira ta da bulu mara godiyar Allah,
Ya kamata tun yanzun ta koma hankalinta ta nuna godiyar ta ga Allah kafin ita ma lokaci ya kure mata ta tafi tana nadamar rayuwar ta.
Sai lokacin sallah ta fito tayi Alwallah tayi sallah,
Ganin har lokacin bata zo ta dauki abinci bane yasa Kaka ta tashi ta shigo dakin,
A zaune take har lokacin saman darduma,
Zama tayi a bakin gado tana fuskantar ta tunda ba komai take yi dan ba carbi take ja ba,
Duk da Abdulmajid ya kira ya faɗa mata yanda suka yi amma tana buƙatar jin ta bakin ta,
"Me ya same ki?
" Yau zanbi Suraj gobe zamu koma tare dashi"
Wani irin murmushi ta saki mai sanyi"Alhamdulillah,Allah mun gode maka,na yi farin ciki sosai da wannan hukuncin da kika yanke,ina kuma fata zaki karɓi mijinki hannu biyu ki yi masa biyayya domin samun Aljannar ki,ta hakan ne kawai zaki iya nuna ma Allah godiyar ki ta hanyar yin bauta a gare shi,domin aure ma yana daga cikin bautar Ubangiji,"
Kara share hawayen ta tayi"na gode Kaka da hakurin da kike tayi da ni"
Saukowa tayi ta rungume ta"ke din dole ta ce dole ne nayi haƙuri dake,ina maki fatan samun farin ciki a rayuwar ki Ummu Salma"
Ita ma rungume Kaka tayi"na gode Kaka"
Auty Hulaira ce ta shigo nan ta tared dasu a haka,
Zolayar su ta shiga yi,kafin daga baya su sakata a tsakiya suna mata nasiha,dan ita Aunty Hulaira shekara biyu kenan da ta dawo gida dan mijin ta rasuwa yayi kuma Allah bai taba basu haihuwa ba,yanzun nan ne ma ta tsayar da wani sai dai shi saurayi ne kuma haka ya nace sai ita,kuma ƴan uwan shi sun yi na'am da ita,
Tare ta zubo masu Gurasa a plate da Balango sai kayan ganye suka shiga ci suna janta da hira dan kawai su ɗebe mata kewa,dan a wannan stage din da take ciki ba a buƙatar wani abu da zai dame rayuwar ta,
Su suka haɗa mata kayan ta wuri ɗaya a cikin babban akwati,sannan Kaka ta kira mata yannin ta,har da Abdulmajid ta nime tafiyarsu akan bata masu rai da tayi tun lokacin auren ta na farko da Yusuf har i zuwa yau,ta kuma kara da masu godiya akan dawo da ita hanya da suke ƙoƙarin yi a ko yaushe,
Sun yi farin ciki sosai sun kuma yi mata fatan Alkhairi,
"To sauran ku Allah yasa ina da rabon ganin auren ku" Cewar kaka,
"Insha Allah zaki gani har ma ki goya tattaɓa kunne"duk dariya suka saka jin amsar da Abdulmalik ya bata,
" Yauwa ni fa na samu mata,dama jira nake komai ya daidaita ayi magana "
Duk kallon sa suka yi,
"Shi yasa nake son ka yaya Abdulmajid nasanka ba kada sanya,a ina take?cewar Salma,
" Ai Balki ce ta Kano yar gidan Gaggon yara "
Baki ta buɗe "da yaushe kuka haɗu,yanzun idan ka kaure yarinyar nan kana nufin dole nace mata Aunty"
"Sosai ma kuwa,ai tun lokacin jinyar ki muka dunki"
"Kuma tana son ka?
" Sosai ma kuwa,ban cin haka ai har da mamarta muna waya tana yawan tambayar ki,ta kuma shaida min in har da gaske nake yi na kwantar da hankali na ta bani "
Duk dariyar farin ciki suke yi,
"To kai fa Abdulrahman?
" Yarinyar limamin unguwar mu ce,Nusaiba "
Duk hamdala suka saka,
Abdulmalik ne kafin ma a juyo kanshi yace "ni fa kar ma a tambaye ni domin har yanzun ina kan bincikawa ne"
Dariya ya basu"Allah ya tayaka zaɓar na gari"
"Yaunzun Abunda za'ayi zan kira kanne na maza zasu zo a gudanar da bincike sannan a shiga gida ayi magana"
Da haka suka tsayar da maganar sannan aka dauko wani hirar,anan suka ci abinci dare bayan sallar Magrib sannan suka wuce bayan sun sallame ta.
Sai da ta idar da sallah Magrib sannan ta kira number shi,wanda bugu biyu ya ɗauka da sallamah,
Amsawa tayi "idan ka idar da Sallah Isha'i ka zo "
"Ina fatan lafiya?
" Lafiya glau kai dai kazo"
"To shi kenan sai na zo"
"Um hmm" Ta faɗa ta na sauke wayar.
Tun ƙarfe takwas take jiran kiran shi har sai takwas da rabi ya kira dan sai da ya idar da jan carbi,
Shi yasa yana kira ta dauka cikin jin haushi tace"Me ne"
Murmushi ya saki domin ya haminci haushi ta ji,to ya zai yi da ita dole sai haƙuri ya san ba laifin ta bane wannan yawan fushin da jin haushi,
"Yi haƙuri gimbiya gani a ƙofar gida"
"Na riga na kwanta sai gobe"
"Dan Allah kiyi haƙuri ki taimake ni,yau ba zan iya bacci ba idan ban gan ki ba"
Dan shiru tayi tana sauraren yanda yake magiya kafin tace "gani nan zuwa"
Sai da ta dauki lokaci dan kanta tana tsaye kofar gida yana kira kafin taga sun fito ita da Aunty Hulaira dake janye da katon Akwati,da sauri ya karasa ya amsa"Aunty ina zaku"
"Akwatin matar ka ce,yau dai Allah yayi wai binka zata yi"
Wato ido yayi yana kallon ta,dauke kai tayi kamar bata ganshi ba,
"Kai da kata na ka bita a hankali domin kasan ba ita kadai ba,ina maku fatan Alkhairi da fatan sauka lafiya,"
Ji yayi kamar ya rungume Aunty Hulaira tsabar murna"na gode sosai Aunty,Allah ya biya ku"
Da Amin ta amsa tana shegewa gida tare da daga masu hannu,
Murmushi ya saki yana buɗe mata gidan gaba,
Shiga tayi ya mai da kofar ya kulle,
Har suka bar unguwar bata ce mashi komai ba,sai da suka hau babban titi sannan ya dan juyo "kina bukatar wani abu ne?
" Fruits"
"Ok"
Nan ma kara girgiza kai tayi,
"To wannan da kike gani Yusuf ne,Yusuf dai da kika sani tsohon mijin ki shine,"
Wani irin zaro ido tayi tana kara zuba mai ido,sai yanzun abin ya zo zuciyar ta,tabbas shine,
Muryarta har rawa yake yi wurin fadin "Yaya me ya same shi?
" Abinda ya shuka ne yake girba,Salma shi yasa nace Allah yana son ki,domin ya gama maki duk rahama da zai maki,amma kina ƙoƙarin yi ma kanki mummunan hisabi,
Ki duba irin jinyar da Baba yayi duk da baƙi nan,komai sai an mashi,har zuwa karshen rayuwar shi yayi mutuwa irin ta rashin jin daɗi wannan ma wani ishara ce,ki duba mutuwar Mama da ko haɗuwa Allah bai nufa za ku yi ba duk da irin burin haɗuwar da kuka ci ma juna,ko samu taga fuskar ki ta nime yafiyar ki ba tayi ba,sannan ki duba wannan na gaban ki na yanzun,ko magana baya iya yi,gabaɗaya wurin bahayarshi ya zazzago kashi baya iya tsayawa,fitsari baya iya tsayawa,wurin tsutsotsi ne kawai ke fita suna rarake wurin,shi kuma ke zaki ce a kanshi,
Ke kuma me ya same ki Salma,Ubangiji ba tsoronki yake yi ba da kika tafi yawon duniya da sunan fushi kina ta aikata barna,amma bai hukunta ki ba sai ma ya baki miji na gari wanda zai iya sadaukar da komai domin ke,
Kin san ma kuwa cewar shi ya bada Kodar shi daya aka sai ya maki"
Da sauri ta gado jikakkun idanunta ta daura a kanshi,
"Kwarai kuwa,domin a lokacin an duba namu a ciki babu wanda ya maki,kuma idan har aka bata lokaci to kina iya rasa ranki saboda coyon dake kanki,shi ya yace zai baki nashi ba tare da tunanin komai ba,kuma ya bada,
Kin ma san irin rashin lafiya da yayi a lokacin,domin kuwa wannan da kike gani a kwance so yayi ya kashe shi ta hanyar dukan shi a ciki,
Kiyi tunanin irin raɗaɗi da azabar daya fuskanta,A ranar da za'ayi aikin a ranar Kakar shi da tayi shekara goma sha ɗaya a kwance a ranar ta tashi,ranar da suka dauki tsayin shekaru suna addu'a da fatan zuwan ta,amma haka ya hakura ya kwanta aka yanka jikin shi aka cire wani bangare nashi mai muhimmanci aka saka maki,ba tare da sanin shin zai kara buɗe ido ko bazai iya ba,ko kuma shima tafiyar ke nan,ya watsar da komai nashi da burin shi ya zaɓe ki,
What sannan har kike fadin baya son ki dan kawai bai faɗa maki cewar yana son ki ba,
Wallah kin ban kunya!kin bani kunya Salma! Amma fa babu komai rayuwa ce kuma duniya ce ta isa kowa riga da zani,amma ki tuna da wannan misalin dake gaban ki,yanzun zabi ya rage naki"har ya juya ya juyo ganin yanda take sharbar kuka"muje na kaiki gida"
Bin bayanshi tayi,har cikin mota yana jin yanda take rusa kuka sai dai ko alamar dakatar da ita bai yi ba,gara tayi ko zai taimaka wurin dawo da ita haoyacin ta,
A ƙofar gida ya ajiye tana fita yaja motar shi ya bar kofar gidan.
Babu kowa a tsakar gidan dan haka dakinsu ta shiga ta zauna ta lungun gado tana cigaba da kuka,
Ganin Yusuf a yau a haka kuma ya matukar tayar mata da hankali,Yusef dan gayu mutum mai ji da iya wanka da saka kaya,yau sai gashi kwance ko riga babu,duk irin kudin da yake kashe ma fatar jikin shi sai gashi yau fatar ta mutu ta yakushe ko gane shi ba'a yi,
To yanzun ina duniyar daya nime,ina arzikin da ya tara,ina kuma lafiyar da yake takama da shi,duk basu amfana masa komai ba,gashi kwance tamkar gawa,zai tayi yabar komai,
Suraj zuciyar ta ya ambaci sunan,tabbas Allah ya bata shine domin ya kara gwada imanin ta,sai gashi duhun kai yana nima ya kai ta ga aikata aikin da na sani,
Idan har zata tuna irin zaman ta da tayi da Yusuf da kuma kwana daya kawai da tayi da Suraj sai yanzun take ganin Allah ne ya amsa addu'ar ta ta bata miji wanda zai iya da ita har ma ya fita saboda ya tsayar da ita a wuri da,amma makantar zuci ya shafi ido,
Tabbas ta cancanci da a kira ta da bulu mara godiyar Allah,
Ya kamata tun yanzun ta koma hankalinta ta nuna godiyar ta ga Allah kafin ita ma lokaci ya kure mata ta tafi tana nadamar rayuwar ta.
Sai lokacin sallah ta fito tayi Alwallah tayi sallah,
Ganin har lokacin bata zo ta dauki abinci bane yasa Kaka ta tashi ta shigo dakin,
A zaune take har lokacin saman darduma,
Zama tayi a bakin gado tana fuskantar ta tunda ba komai take yi dan ba carbi take ja ba,
Duk da Abdulmajid ya kira ya faɗa mata yanda suka yi amma tana buƙatar jin ta bakin ta,
"Me ya same ki?
" Yau zanbi Suraj gobe zamu koma tare dashi"
Wani irin murmushi ta saki mai sanyi"Alhamdulillah,Allah mun gode maka,na yi farin ciki sosai da wannan hukuncin da kika yanke,ina kuma fata zaki karɓi mijinki hannu biyu ki yi masa biyayya domin samun Aljannar ki,ta hakan ne kawai zaki iya nuna ma Allah godiyar ki ta hanyar yin bauta a gare shi,domin aure ma yana daga cikin bautar Ubangiji,"
Kara share hawayen ta tayi"na gode Kaka da hakurin da kike tayi da ni"
Saukowa tayi ta rungume ta"ke din dole ta ce dole ne nayi haƙuri dake,ina maki fatan samun farin ciki a rayuwar ki Ummu Salma"
Ita ma rungume Kaka tayi"na gode Kaka"
Auty Hulaira ce ta shigo nan ta tared dasu a haka,
Zolayar su ta shiga yi,kafin daga baya su sakata a tsakiya suna mata nasiha,dan ita Aunty Hulaira shekara biyu kenan da ta dawo gida dan mijin ta rasuwa yayi kuma Allah bai taba basu haihuwa ba,yanzun nan ne ma ta tsayar da wani sai dai shi saurayi ne kuma haka ya nace sai ita,kuma ƴan uwan shi sun yi na'am da ita,
Tare ta zubo masu Gurasa a plate da Balango sai kayan ganye suka shiga ci suna janta da hira dan kawai su ɗebe mata kewa,dan a wannan stage din da take ciki ba a buƙatar wani abu da zai dame rayuwar ta,
Su suka haɗa mata kayan ta wuri ɗaya a cikin babban akwati,sannan Kaka ta kira mata yannin ta,har da Abdulmajid ta nime tafiyarsu akan bata masu rai da tayi tun lokacin auren ta na farko da Yusuf har i zuwa yau,ta kuma kara da masu godiya akan dawo da ita hanya da suke ƙoƙarin yi a ko yaushe,
Sun yi farin ciki sosai sun kuma yi mata fatan Alkhairi,
"To sauran ku Allah yasa ina da rabon ganin auren ku" Cewar kaka,
"Insha Allah zaki gani har ma ki goya tattaɓa kunne"duk dariya suka saka jin amsar da Abdulmalik ya bata,
" Yauwa ni fa na samu mata,dama jira nake komai ya daidaita ayi magana "
Duk kallon sa suka yi,
"Shi yasa nake son ka yaya Abdulmajid nasanka ba kada sanya,a ina take?cewar Salma,
" Ai Balki ce ta Kano yar gidan Gaggon yara "
Baki ta buɗe "da yaushe kuka haɗu,yanzun idan ka kaure yarinyar nan kana nufin dole nace mata Aunty"
"Sosai ma kuwa,ai tun lokacin jinyar ki muka dunki"
"Kuma tana son ka?
" Sosai ma kuwa,ban cin haka ai har da mamarta muna waya tana yawan tambayar ki,ta kuma shaida min in har da gaske nake yi na kwantar da hankali na ta bani "
Duk dariyar farin ciki suke yi,
"To kai fa Abdulrahman?
" Yarinyar limamin unguwar mu ce,Nusaiba "
Duk hamdala suka saka,
Abdulmalik ne kafin ma a juyo kanshi yace "ni fa kar ma a tambaye ni domin har yanzun ina kan bincikawa ne"
Dariya ya basu"Allah ya tayaka zaɓar na gari"
"Yaunzun Abunda za'ayi zan kira kanne na maza zasu zo a gudanar da bincike sannan a shiga gida ayi magana"
Da haka suka tsayar da maganar sannan aka dauko wani hirar,anan suka ci abinci dare bayan sallar Magrib sannan suka wuce bayan sun sallame ta.
Sai da ta idar da sallah Magrib sannan ta kira number shi,wanda bugu biyu ya ɗauka da sallamah,
Amsawa tayi "idan ka idar da Sallah Isha'i ka zo "
"Ina fatan lafiya?
" Lafiya glau kai dai kazo"
"To shi kenan sai na zo"
"Um hmm" Ta faɗa ta na sauke wayar.
Tun ƙarfe takwas take jiran kiran shi har sai takwas da rabi ya kira dan sai da ya idar da jan carbi,
Shi yasa yana kira ta dauka cikin jin haushi tace"Me ne"
Murmushi ya saki domin ya haminci haushi ta ji,to ya zai yi da ita dole sai haƙuri ya san ba laifin ta bane wannan yawan fushin da jin haushi,
"Yi haƙuri gimbiya gani a ƙofar gida"
"Na riga na kwanta sai gobe"
"Dan Allah kiyi haƙuri ki taimake ni,yau ba zan iya bacci ba idan ban gan ki ba"
Dan shiru tayi tana sauraren yanda yake magiya kafin tace "gani nan zuwa"
Sai da ta dauki lokaci dan kanta tana tsaye kofar gida yana kira kafin taga sun fito ita da Aunty Hulaira dake janye da katon Akwati,da sauri ya karasa ya amsa"Aunty ina zaku"
"Akwatin matar ka ce,yau dai Allah yayi wai binka zata yi"
Wato ido yayi yana kallon ta,dauke kai tayi kamar bata ganshi ba,
"Kai da kata na ka bita a hankali domin kasan ba ita kadai ba,ina maku fatan Alkhairi da fatan sauka lafiya,"
Ji yayi kamar ya rungume Aunty Hulaira tsabar murna"na gode sosai Aunty,Allah ya biya ku"
Da Amin ta amsa tana shegewa gida tare da daga masu hannu,
Murmushi ya saki yana buɗe mata gidan gaba,
Shiga tayi ya mai da kofar ya kulle,
Har suka bar unguwar bata ce mashi komai ba,sai da suka hau babban titi sannan ya dan juyo "kina bukatar wani abu ne?
" Fruits"
"Ok"