Sashe 87
Yar Tsanar Zinari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A hankali ya girgiza mata kai,
"Abdulmalik?
Nan ma girgiza mata kai yayi,
" Abdulmajid ne?
Nan ma girgiza kai ya kuma yi,
So take ta furta suna na gaba amma ta kasa,tsoro take ji,tsoro take ji akan abinda kunnuwanta tasu jiye mata,
Jawota kirjin shi yayi ya rungume ta gaba ɗaya,
Kuka ta fashe dashi sosai tana kara kankame shi tare da kara cusa kanta a kirjin shi,"na fasa zuwa,ba zan je ba"
Dago ta yayi yana share mata hawayen fuskarta wanda suka kasa tsayawa da hannun shi,"look at me"
Girgiza kai tayi tana kara dukar da kai,
Dago fuskar ta yayi"kalle ni Bebin"
Dago rinannun idanun ta tayi ta zuba masa,
"I Trust you,no matter what comes I no you will overcome it,na maki Alkawarin nan da kwana uku zan zo,do you want me to come?ya faɗa da alamun tambaya,
A hankali ta jinjina kai,
Mai da ita kirjin shi yayi ya rungume yana shafa bayanta" That is my Girl "
Dagota yayi ya bata light kiss a goshi kafin ya mike rike da hannun ta jin ana faɗar lokacin shiga jirgin su yayi,har iyakar in da zai iya rakata yaje sai da yaga ta shige kafin ya juya ya koma,cike da jimamin halin da zata sake shiga idan ta isa gida,
Wannan hukunci ne na Ubangiji wanda babu wanda ya isa yayi hakan bayan shi.........
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*87*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*
Jirgin su a Abuja ya sauka,tana fitowa daga Airport ganin motoci tayi jere kusan guda uku,tayi mamakin ganin Bala sosai,
Akwatin hannun ta ya ansa cikin girmamawa yace"barka da isowa Uwar ɗaki na"
Murmushi ne ya kucce mata,domin ko ba komai ta ji daɗin ganin wanda ta sani,"Bala kana lafiya?
"Lafiya qlau nake"ya faɗa yana buɗe mata motar tsakiya,
Sai da ta daidaita zaman ta sannan ta juyo" Me kazo yi anan?
"Tarbar ki muka zo yi"
Dan waro ido tayi"tun daga Kano?
"Muhimmancin ki a wurin shugaba ya kawo hakan"
Tabe taki tayi tana mai da kanta ta jinginar,
Ganin haka yasa shima ta saki murmushi yana shiga dayar motar tare da bada umarni tafiya,
Tafiyar awa daya da rabi ne ya shigo dasu garin Minna,kallon ko'ina take yi kamar yau ta taɓa shigowa garin,hannu ta saka ta dafe kirjinta jin yanda bugun zuciyar ta ke tsananta bugawa,addu'a kawai take yi akan Allah yasa yanda ta tafi ta bar kowa lafiya a cikin gidan Allah yasa ta same su lafiya,
Jin tsayuwar mota ga ƙarar buɗe Get ne ya dawo da ita cikin hayyacinta,da sauri ta ƙara buɗe idon ta ganin in da suke,wato a harabar gidan su,mamaki take yi dama sun san gidan ne,sai dai mamakin ya tsaya ne a lokacin da taga mutane ta ko'ina a cikin gidan,sannan duk wanda zaka gani baya cikin daɗin rai,
Kamar yanda yawancin hankalin mutane dake zazzaune saman tabarmi ya dawo kan waɗannan jerin motocin haka ita ma hankalin ta yake kansu,sai da ta kasa fito,kuma bata da shirin fitowa,
Abdulrahman ne ya fito daga cikin gidan da sauri sai Aunty Hulaira dake biye dashi,kallo daya zaka masu ka shaida rashin natsuwa a tare dasu,
Ganin isowar su ne yasa Bala bude ƙofar motar da take ciki,
Lekawa Aunty Hulaira tayi tana kiran sunan ta,"Ummu Salma!
Ita din ma kallon kanwar mahaifiyar ta tayi,ganin yanda take ƙoƙarin son ɓoye hawayen da ya kasa tsayawa a idonta ne yasa ta kasa ce mata komai sai binta da kallo da take yi,
Hannun ta ruko ta na fitowa da ita,
"Ina Mama?shine tambayar da ya fito daga bakin ta,
Kallon juna sukayi,sai dai babu wanda ya bata amsa,sai ma jan hannun ta da tayi suka doshi cikin gidan,
Duk in da tabi da kallo kawai mutane ke bin ta,duk da basu san Me ya faru ba amma sun san cewar ta daɗe bata gida,a tunanin su kila tana zaune ne a kasar waje,
Kale_kale ta hau yi a falon,ganin babu wacce take nima ne yasa ta nufi dakin Mama,sai dai har bayi ta leka babu kowa,dakin Baba ma ta shiga,shima baya ciki,duk wannan nimar da take masu babu wanda da dakatar da ita kamar yanda babu wanda yace mata komai,
Cikin tashin hankali ta fito falo in da duk suke tsaye cirko cirko ta riko hannun Abdulmajid "Yaya!ina Baba da Mama?
Cikin sauri Aunty Hulaira ta rungume ta tana saka kuka" Kiyi haƙuri Salma,wanda ya fimu son ta ya karɓi abin shi,"
Ji tayi kamar mata fahince me take nufi ba,dan haka zane jikin ta daga na ta tayi"Aunty ni fa ban gane in da maganar ki ta dosa ba"
Tana ƙoƙarin yin magana Abdulrahman ya dakatar da ita ta hanyar daga mata hannu,sannan ya kama hannun Salma"biyo ni "
Bin bayan shi tayi har suka zauna a daya daga cikin kujerun dakin,
"Mama takasance cikin jiran ki na tsayin waɗannan shekarun da suka wuce,kulun cikin kuka take rike da hoton ki tana begen sake kasancewa dake domin ta nime tafiyar ki,sai dai Allah bai yi fuskokin ku zasu sake haɗuwa ba har izuwa numfashin ta na karshe,har i zuwa lokacin kuma sunan ki ka dai take kira,
Tayi data sanin abubuwan data aikata a baya,tayi data sanin biyewa son zuciya,
Muna roƙon ki a matsayin ki na ƴar uwar mu da ki yafe ma mahaifiyar mu kawo ki wannan duniyar da tayi bata hanyar da Ubangiji ya shardanta mata ba,mu mun jima da yafe masu"
Ta kasa kuka ta kasa zubar da hawaye,jin idanun ta take suna mata raɗaɗi kamar ana zuba mata barkono,
"Ina Mama?shine tambayar data ƙara gefa masu yayin da take daura idanun ta a kanshi,
Ji yayi gaban shi ya ɗan faɗi,ganin yanda idanu ta sukayi ja yanda kasan wanda jini ke ƙoƙarin kwantawa a ciki,tsoro yake yi kar ta zo ta cutar da kanta,
" A yau da karfe hudu na Asuba Allah ya karɓa abin shi"
Wani irin shiru ne ya ratsa falon,jira suke suga tayi kuka ko ta saka salati,sai dai ko daya ba ta yi ba sai ma dukar da kai da tayi,
"Baba fa?
" Yana Asibiti a kwance,tunda ya samu labarin rasuwarta"
Mikewa tayi tsaye"mu je ka kai ni wurin shi"
"Ki bari ki huta ko ruwa fa baki sha ba"
Wani irin kallo ta jefa mashi,ba tare da tace komai ba tayi gaba yana biye da ita a baya,
Tana fitowa gaisuwa mutane suka shiga yi mata,sai dai babu wanda ta amsa sai shi dake bayan ta ne yake karbawa,
A wurin parking ne ta iske su Bala zaune suna cin abinci,ganin ta yasa duk suka mike,da hannu tai masa alama a kan yazo,cikin sauri kuwa ya ajiye plate dun dake hannun shi ya iso in da take,
Kallon Agogon hannun ta tayi"ƙarfe biyu yanzun,zamu iya komawa Abuja ku kwana gobe sai ku koma Kano,idan kuma har zaku iya tafiya Kano a yau kuna iya wucewa na gode"
Dukar da kai yayi dan sai yake ganin ta kara masa kwarjini har balle da babu wani digon fara'a a fuskar ta,
"Ubangida na yace mu tsaya dake,duk in da zaki muna iya kai ki,sannan akwai gidan saukar bakin sa a nan garin a can zamu sauka"
"Bana bukatar ku,ku faɗa masa ni nace ku wuce damun ba komawa zan yi ba" Tana gama fadar haka ta buɗe motar da Abdulmajid ke ciki,ba tare da ta kara kallon in da suke ba,
Tunda taga sun doshi hanya har sun wuce Tunga ta san I.B.B Hospital zasu nufa kenan,hakan na nufin jikin shi yayi tsani kenan,
Mai da kanta tayi jikin windo tana hadiyar wani abu mai ɗaci da tauri da ya tsaya mata a makoshi.
Har suka isa Asibitin babu wanda yayi magana a cikin su,
Shi ya buɗe mata kofa ta fito sannan suka shiga ciki,a wani daki na musamman aka kwantar dashi shi kaɗai,
Buɗe ƙofar yayi suka shi,sai dai kasa karasawa tayi in da take hango mutum kwance sanye da Oxygen,
Janyo hannun ta yayi har bakin gadon,
"Roƙon Allah yake yi a koda yaushe a kan kar ta ɗauki rayuwar shi ba tare da ya ganki ba,gashi yau Allah yayi kin dawo"
Ita kanta ba zata iya shaida me take ji ba a zuciyar ta,lallai duniya ba bakin komai take ba,yanzun Baba da ta sani tsayayyen mutum mai nagarta da lafiya shine ya zama haka,shine kwance a nan kamar wani tsumma,shine haka ya koma kamar mai ciyon kanjamau,har tana iya ganin kashin awazan shi,
Lallai Ubangiji ba'a mashi isgili,yanzun ina lafiyar da yake takama da ita,ina kuɗin da yake takama da shi,ina ɗaukakar da yake ganin yana dashi,yau gashi kwance duk abinda yake takama dashi ba su isa su mai maganin komai ba.
Numfashin ta har wani rawa taji yanayi,
Ganin kamar jiri yana ɗibar ta ne yasa ya dauko kujera ya ajiye mata tare da zaunar da ita gaban gado yana ɗaukar hannun Baba dake ajiye ya damka a cikin hannun ta,
"Ki yi masa magana zai jiki"ya faɗa yana barin dakin tare da bar mata dakin,
Ta kwashi mintunan da ita kanta bata san adadin lokacin da ta bata ba a zaune, tana riƙe da hannun shi,jin yana motsawa ne yasa ta daura idanun ta a kanshi,a hankali har ya gama buɗe idanun shi,
" Baba!
Lumshe ido yayi yana buɗewa,
"Baba! Ta ƙara kiran sunan shi a hankali,
Jiyowa yayi ya tsira mats idanu,dan kara matse hannun nashi tayi" Salma ce"
Ta cikin oxygen din ya maimaita abinda ya faɗa,kokari yake yi ya cire oxygen din sai dai ya kasa,
Taimaka mashi tayi ya cire,ta daga gadon kaɗan,
Ƙara rike hannun ta yayi,"kin dawo ne?
Jinjina mashi kai tayi"ka yafe min Baba"ta faɗa tana dukar da kai,
"Abdulmalik?
Nan ma girgiza mata kai yayi,
" Abdulmajid ne?
Nan ma girgiza kai ya kuma yi,
So take ta furta suna na gaba amma ta kasa,tsoro take ji,tsoro take ji akan abinda kunnuwanta tasu jiye mata,
Jawota kirjin shi yayi ya rungume ta gaba ɗaya,
Kuka ta fashe dashi sosai tana kara kankame shi tare da kara cusa kanta a kirjin shi,"na fasa zuwa,ba zan je ba"
Dago ta yayi yana share mata hawayen fuskarta wanda suka kasa tsayawa da hannun shi,"look at me"
Girgiza kai tayi tana kara dukar da kai,
Dago fuskar ta yayi"kalle ni Bebin"
Dago rinannun idanun ta tayi ta zuba masa,
"I Trust you,no matter what comes I no you will overcome it,na maki Alkawarin nan da kwana uku zan zo,do you want me to come?ya faɗa da alamun tambaya,
A hankali ta jinjina kai,
Mai da ita kirjin shi yayi ya rungume yana shafa bayanta" That is my Girl "
Dagota yayi ya bata light kiss a goshi kafin ya mike rike da hannun ta jin ana faɗar lokacin shiga jirgin su yayi,har iyakar in da zai iya rakata yaje sai da yaga ta shige kafin ya juya ya koma,cike da jimamin halin da zata sake shiga idan ta isa gida,
Wannan hukunci ne na Ubangiji wanda babu wanda ya isa yayi hakan bayan shi.........
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*87*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*
Jirgin su a Abuja ya sauka,tana fitowa daga Airport ganin motoci tayi jere kusan guda uku,tayi mamakin ganin Bala sosai,
Akwatin hannun ta ya ansa cikin girmamawa yace"barka da isowa Uwar ɗaki na"
Murmushi ne ya kucce mata,domin ko ba komai ta ji daɗin ganin wanda ta sani,"Bala kana lafiya?
"Lafiya qlau nake"ya faɗa yana buɗe mata motar tsakiya,
Sai da ta daidaita zaman ta sannan ta juyo" Me kazo yi anan?
"Tarbar ki muka zo yi"
Dan waro ido tayi"tun daga Kano?
"Muhimmancin ki a wurin shugaba ya kawo hakan"
Tabe taki tayi tana mai da kanta ta jinginar,
Ganin haka yasa shima ta saki murmushi yana shiga dayar motar tare da bada umarni tafiya,
Tafiyar awa daya da rabi ne ya shigo dasu garin Minna,kallon ko'ina take yi kamar yau ta taɓa shigowa garin,hannu ta saka ta dafe kirjinta jin yanda bugun zuciyar ta ke tsananta bugawa,addu'a kawai take yi akan Allah yasa yanda ta tafi ta bar kowa lafiya a cikin gidan Allah yasa ta same su lafiya,
Jin tsayuwar mota ga ƙarar buɗe Get ne ya dawo da ita cikin hayyacinta,da sauri ta ƙara buɗe idon ta ganin in da suke,wato a harabar gidan su,mamaki take yi dama sun san gidan ne,sai dai mamakin ya tsaya ne a lokacin da taga mutane ta ko'ina a cikin gidan,sannan duk wanda zaka gani baya cikin daɗin rai,
Kamar yanda yawancin hankalin mutane dake zazzaune saman tabarmi ya dawo kan waɗannan jerin motocin haka ita ma hankalin ta yake kansu,sai da ta kasa fito,kuma bata da shirin fitowa,
Abdulrahman ne ya fito daga cikin gidan da sauri sai Aunty Hulaira dake biye dashi,kallo daya zaka masu ka shaida rashin natsuwa a tare dasu,
Ganin isowar su ne yasa Bala bude ƙofar motar da take ciki,
Lekawa Aunty Hulaira tayi tana kiran sunan ta,"Ummu Salma!
Ita din ma kallon kanwar mahaifiyar ta tayi,ganin yanda take ƙoƙarin son ɓoye hawayen da ya kasa tsayawa a idonta ne yasa ta kasa ce mata komai sai binta da kallo da take yi,
Hannun ta ruko ta na fitowa da ita,
"Ina Mama?shine tambayar da ya fito daga bakin ta,
Kallon juna sukayi,sai dai babu wanda ya bata amsa,sai ma jan hannun ta da tayi suka doshi cikin gidan,
Duk in da tabi da kallo kawai mutane ke bin ta,duk da basu san Me ya faru ba amma sun san cewar ta daɗe bata gida,a tunanin su kila tana zaune ne a kasar waje,
Kale_kale ta hau yi a falon,ganin babu wacce take nima ne yasa ta nufi dakin Mama,sai dai har bayi ta leka babu kowa,dakin Baba ma ta shiga,shima baya ciki,duk wannan nimar da take masu babu wanda da dakatar da ita kamar yanda babu wanda yace mata komai,
Cikin tashin hankali ta fito falo in da duk suke tsaye cirko cirko ta riko hannun Abdulmajid "Yaya!ina Baba da Mama?
Cikin sauri Aunty Hulaira ta rungume ta tana saka kuka" Kiyi haƙuri Salma,wanda ya fimu son ta ya karɓi abin shi,"
Ji tayi kamar mata fahince me take nufi ba,dan haka zane jikin ta daga na ta tayi"Aunty ni fa ban gane in da maganar ki ta dosa ba"
Tana ƙoƙarin yin magana Abdulrahman ya dakatar da ita ta hanyar daga mata hannu,sannan ya kama hannun Salma"biyo ni "
Bin bayan shi tayi har suka zauna a daya daga cikin kujerun dakin,
"Mama takasance cikin jiran ki na tsayin waɗannan shekarun da suka wuce,kulun cikin kuka take rike da hoton ki tana begen sake kasancewa dake domin ta nime tafiyar ki,sai dai Allah bai yi fuskokin ku zasu sake haɗuwa ba har izuwa numfashin ta na karshe,har i zuwa lokacin kuma sunan ki ka dai take kira,
Tayi data sanin abubuwan data aikata a baya,tayi data sanin biyewa son zuciya,
Muna roƙon ki a matsayin ki na ƴar uwar mu da ki yafe ma mahaifiyar mu kawo ki wannan duniyar da tayi bata hanyar da Ubangiji ya shardanta mata ba,mu mun jima da yafe masu"
Ta kasa kuka ta kasa zubar da hawaye,jin idanun ta take suna mata raɗaɗi kamar ana zuba mata barkono,
"Ina Mama?shine tambayar data ƙara gefa masu yayin da take daura idanun ta a kanshi,
Ji yayi gaban shi ya ɗan faɗi,ganin yanda idanu ta sukayi ja yanda kasan wanda jini ke ƙoƙarin kwantawa a ciki,tsoro yake yi kar ta zo ta cutar da kanta,
" A yau da karfe hudu na Asuba Allah ya karɓa abin shi"
Wani irin shiru ne ya ratsa falon,jira suke suga tayi kuka ko ta saka salati,sai dai ko daya ba ta yi ba sai ma dukar da kai da tayi,
"Baba fa?
" Yana Asibiti a kwance,tunda ya samu labarin rasuwarta"
Mikewa tayi tsaye"mu je ka kai ni wurin shi"
"Ki bari ki huta ko ruwa fa baki sha ba"
Wani irin kallo ta jefa mashi,ba tare da tace komai ba tayi gaba yana biye da ita a baya,
Tana fitowa gaisuwa mutane suka shiga yi mata,sai dai babu wanda ta amsa sai shi dake bayan ta ne yake karbawa,
A wurin parking ne ta iske su Bala zaune suna cin abinci,ganin ta yasa duk suka mike,da hannu tai masa alama a kan yazo,cikin sauri kuwa ya ajiye plate dun dake hannun shi ya iso in da take,
Kallon Agogon hannun ta tayi"ƙarfe biyu yanzun,zamu iya komawa Abuja ku kwana gobe sai ku koma Kano,idan kuma har zaku iya tafiya Kano a yau kuna iya wucewa na gode"
Dukar da kai yayi dan sai yake ganin ta kara masa kwarjini har balle da babu wani digon fara'a a fuskar ta,
"Ubangida na yace mu tsaya dake,duk in da zaki muna iya kai ki,sannan akwai gidan saukar bakin sa a nan garin a can zamu sauka"
"Bana bukatar ku,ku faɗa masa ni nace ku wuce damun ba komawa zan yi ba" Tana gama fadar haka ta buɗe motar da Abdulmajid ke ciki,ba tare da ta kara kallon in da suke ba,
Tunda taga sun doshi hanya har sun wuce Tunga ta san I.B.B Hospital zasu nufa kenan,hakan na nufin jikin shi yayi tsani kenan,
Mai da kanta tayi jikin windo tana hadiyar wani abu mai ɗaci da tauri da ya tsaya mata a makoshi.
Har suka isa Asibitin babu wanda yayi magana a cikin su,
Shi ya buɗe mata kofa ta fito sannan suka shiga ciki,a wani daki na musamman aka kwantar dashi shi kaɗai,
Buɗe ƙofar yayi suka shi,sai dai kasa karasawa tayi in da take hango mutum kwance sanye da Oxygen,
Janyo hannun ta yayi har bakin gadon,
"Roƙon Allah yake yi a koda yaushe a kan kar ta ɗauki rayuwar shi ba tare da ya ganki ba,gashi yau Allah yayi kin dawo"
Ita kanta ba zata iya shaida me take ji ba a zuciyar ta,lallai duniya ba bakin komai take ba,yanzun Baba da ta sani tsayayyen mutum mai nagarta da lafiya shine ya zama haka,shine kwance a nan kamar wani tsumma,shine haka ya koma kamar mai ciyon kanjamau,har tana iya ganin kashin awazan shi,
Lallai Ubangiji ba'a mashi isgili,yanzun ina lafiyar da yake takama da ita,ina kuɗin da yake takama da shi,ina ɗaukakar da yake ganin yana dashi,yau gashi kwance duk abinda yake takama dashi ba su isa su mai maganin komai ba.
Numfashin ta har wani rawa taji yanayi,
Ganin kamar jiri yana ɗibar ta ne yasa ya dauko kujera ya ajiye mata tare da zaunar da ita gaban gado yana ɗaukar hannun Baba dake ajiye ya damka a cikin hannun ta,
"Ki yi masa magana zai jiki"ya faɗa yana barin dakin tare da bar mata dakin,
Ta kwashi mintunan da ita kanta bata san adadin lokacin da ta bata ba a zaune, tana riƙe da hannun shi,jin yana motsawa ne yasa ta daura idanun ta a kanshi,a hankali har ya gama buɗe idanun shi,
" Baba!
Lumshe ido yayi yana buɗewa,
"Baba! Ta ƙara kiran sunan shi a hankali,
Jiyowa yayi ya tsira mats idanu,dan kara matse hannun nashi tayi" Salma ce"
Ta cikin oxygen din ya maimaita abinda ya faɗa,kokari yake yi ya cire oxygen din sai dai ya kasa,
Taimaka mashi tayi ya cire,ta daga gadon kaɗan,
Ƙara rike hannun ta yayi,"kin dawo ne?
Jinjina mashi kai tayi"ka yafe min Baba"ta faɗa tana dukar da kai,