Sashe 10
Yar Tsanar Zinari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Wallahi yaya ban san yanda aka yi ba,amma ko jiya da muka gama girkin dare sai da na share kicin dinnan sannan na goge ko ina nayi wanke-wanke,ni bansan ta in da man gyaɗa ya fito ba har ya zuba a ƙasa,tunda ba a kicin muke ajiye kayan abinci ba"
Shiru yayi yana ɗan nazari,ganin bai fahimce ko mai bane yasa yace"is ok, kukan ya isa haka "
Jin ana sallamah ne yasa yace mata"je ki dauko ma Ammi Hijabi"shi kuma ya tashi ya fita,
Bai wani jima ba ya shigo tare da mutumin,wanda anan ya duba kafar ya kuma tabbatar masa da cewa ta samu targade a babban ɗan yatsa,sai tsagewar kashi ta gefen ƙafar,
Sai da ya koma gida yazo da abubuwan da yake bukata kafin ya fara mata ɗaurin kafa wanda ba karamin azaba ta ji ba,
Allah dai ya taimaka an samu nasaran kyarawa,sai dai ba daman Kata kafar sosai,
A ɗan kwana biyun da tayi wannan ciyon ƙafar aiki kamar zai kashe Amira,wacce ga zuwa makaranta ga kuma islamiya,
Hakan ne yasa Kaka da kanta ta bada shawara akan dole a dauki ƴar aiki domin ba ta yanda za'a yi Amira ta iya waɗannan aiyuka ita kaɗai,
Duk da Ammi bata soba ba yanda ta iya tunda lalura ne ya kamata wanda dole tana buƙatar mataimakiya,
Matar da take kawo masu masu aiki Kaka ta kira ta sanar da ita suna buƙatar me aiki,kamar dai ko wani lokaci mace mai tsafta suke so,
Ce mata tayi zuwa yamma za'a kawo ta.
_____misalin karfe biyar,zaune take a saman tabarmar da aka shimfida mata,ta turo bakin nan nata gaba,wanda kallo daya zaka mata ka fahimce irin bacin rai dake tare da ita,
Matan nan ce naga ta zo ta zauna kusa da ita tana miko mata wata waya Nokia wanda tasha lobali ko marfi ba ta dashi,
"Biba karba mana"
Kin karɓar wayar tayi tana mai da hannun ta baya kamar wata karamar yarinya,
Duk yanda taso ta ɓoye dariyar ta dan karta ƙara tunzura kasawa tayi sai da ta saka dariya,ganin yanda tayi yanda kasan yarinya ƴar shekara shida,ga kayan data saka riga da zani wasu masu kalan tsofaffin,zanin leɓe daya yafi ɗaya kasan ya matse wanda da ƙyar ma in zata iya tafiya dashi,rigar gashi nan babu fasali dan ya mata yawa ajiki,
Fuskarta dai yayi wani fari tas dashi mai ban sha'awa,gashi sumul babu wani ɗigon baki ko kurji,idanun ta sun kara haske domin ko kwalli babu,sai ƴan madai_daitan labbanta jawur dasu ta turo su gaba,
Idan har kai mai lura ne kallo daya zaka ma hallittar jikin Biba kasan jikinta ba kalan wanda ya saba aikin wahala bane.
"Kinga Biba haƙuri zaki yi ki karɓi wannan wayar haka,na saka maki sim a ciki,akwai kuma number ta a ciki,idan kina buƙatar wani abun sai ki sanar dani,kuma ta wannan layin VIP zai neme ki"
Amsa tayi ba tare data ce mata komai ba ta mike tana daukar jakkan dake gabanta zata goshi ƙofa,
"A'a tsaya kinga sai kin saka hijabi" Ta faɗa tana dauko hajabin dake ajiye a gabanta,tabi bayan ta,
Sai da suka shiga Adaidaita sannan ta karɓi hijabin ta saka.
"Kinga karki damu,ba wani daɗewa zaki yi a gidan ba,da zaran kin dauko masa abinda yake buƙata shikenan aikin ki a gidan ya kare,ko da kuwa a yau ne,kuma akwai littafin girki a cikin jakkan ki na saka maki,wanda zai taimaka maki"
Ita dai bata ce mata komai ba domin bacin randa take ciki ma ya ishe ta,
Jin mai Adaidaita ya saya ne yasa ta dago kanta tana kare ma wani tafkeken kofar Get din da suke tsaye,wanda akwai babban masallaci a kofar Get ɗin,
Fitowa suka yi daga cikin Adaidaita suka doshi kofar gidan tare da jakkan ta a hannun yayin da take jin bugun zuciyar ta na sauyawa a ko wani taku da tayi......
*Last free page*
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*12*
*Na mai da Littafina mai suna a sama na kuɗi,tare da JAURO,idan kina son daya 300,dari uku,guda biyu kuma da Yar Tsanar Zinari tare da Jauro,dari biyar 500,ko wani daya dari uku*
*Hauwa Umar,Zenith Bank, 2284905309*
*ko katin waya na MTN,tare da turo shedar biya ta 08141644865*
Mai gadi ne ya buɗe masu Get suka shiga bayan sun faɗa mashi wurin Kaka zasu,duk da dama ya santa,
Tunda suka shiga gidan take kallon ko ina cikin taka tsantsan,yayin da matar wacce taji yaran gidan na kiranta da A'i take nuna mata da ido waɗannan shiyoyin guda huɗu,"wannan dake kallon Arewa anan zaki yi aiki,sauran kuma duk na Ya'yan Kakar ce,sai na karshe wanda ɗiyarta ke ciki da nata yaran,idan mun shiga wurin tsohuwar dan Allah ki yi mata ladibi sannan waɗannan idanun naki da suke a tsaye ki dinga rusunar dasu"ta faɗa tana turo kofar wani shiya,"kinga kuma ta can baya ne dakin samarin gidan yake"
Sallamah tayi a ɗan madaidaicin tsakar gidan wanda yake a share tas,
Jin ba'a amsaba yasa suka karasa har kofar shiga cikin falon Kaka,
Nan ma wata sallamah tayi,wanda suka ji an amsa masu ta bayan su,
Duk juyowa suka yi suna kallon ta,ƴar budurwa ce wacce bata wuce sha tare,kusan tsaran Biba ce,dauke da ninkakkun kayan da aka wanke,alamun ta kwaso ne daga shanya,duk da kayan jikinta ba laifi amma daga dukkan alamu yar aiki ce,
Murmushi ta sakar masu"barkar ku da zuwa,wa kuke nima"
"Wurin Kaka muka zo tana ciki?
" Eh ku shigo"ta faɗa tana shiga gaba,har cikin falon kafin ta nuna masu wurin zama,ta shiga kicin da dauko masu gorunan ruwa tare da kofi,domin yin haka dokar Kaka ne,in dai baƙo zai shigo wurinta,
Wani daki tashiga bata jima ba sai gashi ta fito"ku jira tana zuwa"
"To mungode ƴan mata"
Basu wani jima ba saiga wata kyakkyawar tsohuwa ta fito daga cikin daki,ƙafarta tasha lalli na Hausa,tayi kyau abinta,
Da murmushi ta karaso inda suke,
Da sauri taga A'I ta tsugunna kasa tana gaishe ta,wanda ita ma ganin hakan ne yasa ta tsugunna,
Zama tayi a kushin din dake fuskantar nasu tana dan dariya,"a'a maza ku tashi ku zauna,A'I kinsan bana son irin wannan gaisuwar"
Komawa suka yi suka zauna kan kushin,
"Ga ta na kawo kaka,da fatan tayi maki"
Kallon ta take tun daga sama har kasa tana jinjina kai,"ya sunan ki yan mata"ta tambaya
Kanta a duke yake domin matar ta mata kwarjini sosai,"Habiba,amma ana kira na da Biba"
"Masha Allah suna mai daɗi,Habiba,shakaranki nawa"
"Ishirin nake"
Maida kallon ta tayi kan A'I wacce ke addu'a a zuciyar ta akan Allah yasa ta amsheta"wannan din tayi A'I,da fatan ba zamu samu matsala da ita ba"
"Insha Allah Kaka domin ita ba tada matsala ga tsafta,na tabbatar sai kin yaba"
"Allah yasa,yanzun dai za'a dinga biyanta ta hannun ta ne ko kuwa ke za'a ba"
"A'a Kaka kawai ku dinga bata a hannun ta,shi zai fi,"
Yarinyar dazu ce ta fito zata wuce,kaka ta ce "Nafisa kawo masu abinci"
"A'a Kaka a barshi domin sauri nake ina son in shaga kasuwa ne kafin a tashi,"
"To ba matsala,zubo ma Habiba ita," Kuɗi ta ciro wanda zai iya kaiwa dubu goma taba A'I "gashi kiyi kudin komawa "
Amsa tayi tana washe baki"nagode sosai kaka Allah ya biya,ya ƙara lafiya "
Cikin sanyin murya tace"kaka nima na koshi"
"Ki saki jikin ki sosai damu Habiba,na tabbatar ba zaki yi dana sani ba"
Dukar dakai kawai tayi domin haka kawai ta ji matar ta kwanta mata.
Sallamah A'I taimasu ta wuce,
Daukar waya tayi ta shiga wurin kira,bugu daya aka ɗauka,amsa sallamah tayi"ki turo min Amira "
Sai kuma tace "to" Tana sauke wayar.
"Iyayenki ƴan wasu gari ne Habiba"
"Daura a Katsina" Ta bata amsa domin haka aka tsara mata,
"Aikuwa nasan katsina sosai,a wata unguwa"
Kafin ta bata amsa ne taji anyi sallamah a bakin ƙofa,
Amsawa suka yi,kaka na bada umarni ta shigo,
Tana zuwa zama tayi kusa da kaka tana rike hannun ta tana jujjuyawa "Wow kaka hannun nan naki yamin kyau,kamar muyi canje"
"Ko dai zamu yi canjen ne,ai ku yaran yanzun kyuya ke hanaku kwalliya"
"Ni dai banda ni,idan na samu lokaci zan zo kimin da kanki"
"Sake min hannu karki karya ni,ga sabuwar mataimakiya nasa an kawo wacce zata dinga taimaka ma Ammi,kafin taji sauki,idan har ta mata kuma tana iya riƙe ta,idan kuma taga bata butarta zuwa lokacin ni zata dawo shiyana da aiki"
Juyowa tayi inda Biba ke zaune tana kallon su,"Wow kaka ina kika samo ƴar aiki mai kyau haka? Tasowa tayi ta dawo kusa da Biba tana shafa fuskarta"Wow,gaskiya kina da kyau,kamar ba yar ƙauye ba"
"Ke ni bani son zuba,tashi ki kaita ta gaida Ammi ki kuma nunnuna mata wuraren daya kamata ta sani"
Tashi tayi tana rike hannun Biba,wacce ta dauki jakkanta da hannu daya,"muje"
Tare suka fito da Amiran wacce take ta zuba mata surutu akan kyanta,ita dai sai dai tayi murmushi,
Babban falo ne suka shiga wanda ba laifi komai an zuba shi daidai hankali,cewa tayi"ki ajiye jakkanki anan kafin muji me Ammi zata ce"
Ajiye jakkan tayi a gefen kushin suka nufe wani ƙofa,nan ma cewa tayi"tsaya na sanar da ita shigowar mu"
Nan ma tsayawa tayi,ita kuma ta shiga ciki,
Bata jima ba ta fito fuskarta dauke da murmushi"muje tace ki shigo"
Bin bayanta tayi,har cikin wani madaidaicin falo in da anan suka tarad da wata mata kyakkyawan zaune a kan kushin tasha kwalliya sai kamshi take zubawa,
Samun kanta tayi da zama a ƙasa tana gaishe ta"ina wuni"
Kallon yarinyar take yi cikin kulawa"lafiya ya kike"
"Lafiya"
"Ya sunan ki"
"Habiba,amma ana kira na da Biba"
"Daga wani gari kike"
"Katsina a Daura"
"Yayi kyau,da fatan dai ba kiɗa matsala,domin bana son kazanta ko kadan,ta ko wani bangare ya kasance kina da tsafta,idan har kin kiyaye zamu zauna lafiya"
"Insha Allah Hajiya"
Shiru yayi yana ɗan nazari,ganin bai fahimce ko mai bane yasa yace"is ok, kukan ya isa haka "
Jin ana sallamah ne yasa yace mata"je ki dauko ma Ammi Hijabi"shi kuma ya tashi ya fita,
Bai wani jima ba ya shigo tare da mutumin,wanda anan ya duba kafar ya kuma tabbatar masa da cewa ta samu targade a babban ɗan yatsa,sai tsagewar kashi ta gefen ƙafar,
Sai da ya koma gida yazo da abubuwan da yake bukata kafin ya fara mata ɗaurin kafa wanda ba karamin azaba ta ji ba,
Allah dai ya taimaka an samu nasaran kyarawa,sai dai ba daman Kata kafar sosai,
A ɗan kwana biyun da tayi wannan ciyon ƙafar aiki kamar zai kashe Amira,wacce ga zuwa makaranta ga kuma islamiya,
Hakan ne yasa Kaka da kanta ta bada shawara akan dole a dauki ƴar aiki domin ba ta yanda za'a yi Amira ta iya waɗannan aiyuka ita kaɗai,
Duk da Ammi bata soba ba yanda ta iya tunda lalura ne ya kamata wanda dole tana buƙatar mataimakiya,
Matar da take kawo masu masu aiki Kaka ta kira ta sanar da ita suna buƙatar me aiki,kamar dai ko wani lokaci mace mai tsafta suke so,
Ce mata tayi zuwa yamma za'a kawo ta.
_____misalin karfe biyar,zaune take a saman tabarmar da aka shimfida mata,ta turo bakin nan nata gaba,wanda kallo daya zaka mata ka fahimce irin bacin rai dake tare da ita,
Matan nan ce naga ta zo ta zauna kusa da ita tana miko mata wata waya Nokia wanda tasha lobali ko marfi ba ta dashi,
"Biba karba mana"
Kin karɓar wayar tayi tana mai da hannun ta baya kamar wata karamar yarinya,
Duk yanda taso ta ɓoye dariyar ta dan karta ƙara tunzura kasawa tayi sai da ta saka dariya,ganin yanda tayi yanda kasan yarinya ƴar shekara shida,ga kayan data saka riga da zani wasu masu kalan tsofaffin,zanin leɓe daya yafi ɗaya kasan ya matse wanda da ƙyar ma in zata iya tafiya dashi,rigar gashi nan babu fasali dan ya mata yawa ajiki,
Fuskarta dai yayi wani fari tas dashi mai ban sha'awa,gashi sumul babu wani ɗigon baki ko kurji,idanun ta sun kara haske domin ko kwalli babu,sai ƴan madai_daitan labbanta jawur dasu ta turo su gaba,
Idan har kai mai lura ne kallo daya zaka ma hallittar jikin Biba kasan jikinta ba kalan wanda ya saba aikin wahala bane.
"Kinga Biba haƙuri zaki yi ki karɓi wannan wayar haka,na saka maki sim a ciki,akwai kuma number ta a ciki,idan kina buƙatar wani abun sai ki sanar dani,kuma ta wannan layin VIP zai neme ki"
Amsa tayi ba tare data ce mata komai ba ta mike tana daukar jakkan dake gabanta zata goshi ƙofa,
"A'a tsaya kinga sai kin saka hijabi" Ta faɗa tana dauko hajabin dake ajiye a gabanta,tabi bayan ta,
Sai da suka shiga Adaidaita sannan ta karɓi hijabin ta saka.
"Kinga karki damu,ba wani daɗewa zaki yi a gidan ba,da zaran kin dauko masa abinda yake buƙata shikenan aikin ki a gidan ya kare,ko da kuwa a yau ne,kuma akwai littafin girki a cikin jakkan ki na saka maki,wanda zai taimaka maki"
Ita dai bata ce mata komai ba domin bacin randa take ciki ma ya ishe ta,
Jin mai Adaidaita ya saya ne yasa ta dago kanta tana kare ma wani tafkeken kofar Get din da suke tsaye,wanda akwai babban masallaci a kofar Get ɗin,
Fitowa suka yi daga cikin Adaidaita suka doshi kofar gidan tare da jakkan ta a hannun yayin da take jin bugun zuciyar ta na sauyawa a ko wani taku da tayi......
*Last free page*
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*12*
*Na mai da Littafina mai suna a sama na kuɗi,tare da JAURO,idan kina son daya 300,dari uku,guda biyu kuma da Yar Tsanar Zinari tare da Jauro,dari biyar 500,ko wani daya dari uku*
*Hauwa Umar,Zenith Bank, 2284905309*
*ko katin waya na MTN,tare da turo shedar biya ta 08141644865*
Mai gadi ne ya buɗe masu Get suka shiga bayan sun faɗa mashi wurin Kaka zasu,duk da dama ya santa,
Tunda suka shiga gidan take kallon ko ina cikin taka tsantsan,yayin da matar wacce taji yaran gidan na kiranta da A'i take nuna mata da ido waɗannan shiyoyin guda huɗu,"wannan dake kallon Arewa anan zaki yi aiki,sauran kuma duk na Ya'yan Kakar ce,sai na karshe wanda ɗiyarta ke ciki da nata yaran,idan mun shiga wurin tsohuwar dan Allah ki yi mata ladibi sannan waɗannan idanun naki da suke a tsaye ki dinga rusunar dasu"ta faɗa tana turo kofar wani shiya,"kinga kuma ta can baya ne dakin samarin gidan yake"
Sallamah tayi a ɗan madaidaicin tsakar gidan wanda yake a share tas,
Jin ba'a amsaba yasa suka karasa har kofar shiga cikin falon Kaka,
Nan ma wata sallamah tayi,wanda suka ji an amsa masu ta bayan su,
Duk juyowa suka yi suna kallon ta,ƴar budurwa ce wacce bata wuce sha tare,kusan tsaran Biba ce,dauke da ninkakkun kayan da aka wanke,alamun ta kwaso ne daga shanya,duk da kayan jikinta ba laifi amma daga dukkan alamu yar aiki ce,
Murmushi ta sakar masu"barkar ku da zuwa,wa kuke nima"
"Wurin Kaka muka zo tana ciki?
" Eh ku shigo"ta faɗa tana shiga gaba,har cikin falon kafin ta nuna masu wurin zama,ta shiga kicin da dauko masu gorunan ruwa tare da kofi,domin yin haka dokar Kaka ne,in dai baƙo zai shigo wurinta,
Wani daki tashiga bata jima ba sai gashi ta fito"ku jira tana zuwa"
"To mungode ƴan mata"
Basu wani jima ba saiga wata kyakkyawar tsohuwa ta fito daga cikin daki,ƙafarta tasha lalli na Hausa,tayi kyau abinta,
Da murmushi ta karaso inda suke,
Da sauri taga A'I ta tsugunna kasa tana gaishe ta,wanda ita ma ganin hakan ne yasa ta tsugunna,
Zama tayi a kushin din dake fuskantar nasu tana dan dariya,"a'a maza ku tashi ku zauna,A'I kinsan bana son irin wannan gaisuwar"
Komawa suka yi suka zauna kan kushin,
"Ga ta na kawo kaka,da fatan tayi maki"
Kallon ta take tun daga sama har kasa tana jinjina kai,"ya sunan ki yan mata"ta tambaya
Kanta a duke yake domin matar ta mata kwarjini sosai,"Habiba,amma ana kira na da Biba"
"Masha Allah suna mai daɗi,Habiba,shakaranki nawa"
"Ishirin nake"
Maida kallon ta tayi kan A'I wacce ke addu'a a zuciyar ta akan Allah yasa ta amsheta"wannan din tayi A'I,da fatan ba zamu samu matsala da ita ba"
"Insha Allah Kaka domin ita ba tada matsala ga tsafta,na tabbatar sai kin yaba"
"Allah yasa,yanzun dai za'a dinga biyanta ta hannun ta ne ko kuwa ke za'a ba"
"A'a Kaka kawai ku dinga bata a hannun ta,shi zai fi,"
Yarinyar dazu ce ta fito zata wuce,kaka ta ce "Nafisa kawo masu abinci"
"A'a Kaka a barshi domin sauri nake ina son in shaga kasuwa ne kafin a tashi,"
"To ba matsala,zubo ma Habiba ita," Kuɗi ta ciro wanda zai iya kaiwa dubu goma taba A'I "gashi kiyi kudin komawa "
Amsa tayi tana washe baki"nagode sosai kaka Allah ya biya,ya ƙara lafiya "
Cikin sanyin murya tace"kaka nima na koshi"
"Ki saki jikin ki sosai damu Habiba,na tabbatar ba zaki yi dana sani ba"
Dukar dakai kawai tayi domin haka kawai ta ji matar ta kwanta mata.
Sallamah A'I taimasu ta wuce,
Daukar waya tayi ta shiga wurin kira,bugu daya aka ɗauka,amsa sallamah tayi"ki turo min Amira "
Sai kuma tace "to" Tana sauke wayar.
"Iyayenki ƴan wasu gari ne Habiba"
"Daura a Katsina" Ta bata amsa domin haka aka tsara mata,
"Aikuwa nasan katsina sosai,a wata unguwa"
Kafin ta bata amsa ne taji anyi sallamah a bakin ƙofa,
Amsawa suka yi,kaka na bada umarni ta shigo,
Tana zuwa zama tayi kusa da kaka tana rike hannun ta tana jujjuyawa "Wow kaka hannun nan naki yamin kyau,kamar muyi canje"
"Ko dai zamu yi canjen ne,ai ku yaran yanzun kyuya ke hanaku kwalliya"
"Ni dai banda ni,idan na samu lokaci zan zo kimin da kanki"
"Sake min hannu karki karya ni,ga sabuwar mataimakiya nasa an kawo wacce zata dinga taimaka ma Ammi,kafin taji sauki,idan har ta mata kuma tana iya riƙe ta,idan kuma taga bata butarta zuwa lokacin ni zata dawo shiyana da aiki"
Juyowa tayi inda Biba ke zaune tana kallon su,"Wow kaka ina kika samo ƴar aiki mai kyau haka? Tasowa tayi ta dawo kusa da Biba tana shafa fuskarta"Wow,gaskiya kina da kyau,kamar ba yar ƙauye ba"
"Ke ni bani son zuba,tashi ki kaita ta gaida Ammi ki kuma nunnuna mata wuraren daya kamata ta sani"
Tashi tayi tana rike hannun Biba,wacce ta dauki jakkanta da hannu daya,"muje"
Tare suka fito da Amiran wacce take ta zuba mata surutu akan kyanta,ita dai sai dai tayi murmushi,
Babban falo ne suka shiga wanda ba laifi komai an zuba shi daidai hankali,cewa tayi"ki ajiye jakkanki anan kafin muji me Ammi zata ce"
Ajiye jakkan tayi a gefen kushin suka nufe wani ƙofa,nan ma cewa tayi"tsaya na sanar da ita shigowar mu"
Nan ma tsayawa tayi,ita kuma ta shiga ciki,
Bata jima ba ta fito fuskarta dauke da murmushi"muje tace ki shigo"
Bin bayanta tayi,har cikin wani madaidaicin falo in da anan suka tarad da wata mata kyakkyawan zaune a kan kushin tasha kwalliya sai kamshi take zubawa,
Samun kanta tayi da zama a ƙasa tana gaishe ta"ina wuni"
Kallon yarinyar take yi cikin kulawa"lafiya ya kike"
"Lafiya"
"Ya sunan ki"
"Habiba,amma ana kira na da Biba"
"Daga wani gari kike"
"Katsina a Daura"
"Yayi kyau,da fatan dai ba kiɗa matsala,domin bana son kazanta ko kadan,ta ko wani bangare ya kasance kina da tsafta,idan har kin kiyaye zamu zauna lafiya"
"Insha Allah Hajiya"