Sashe 23
Yar Tsanar Zinari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Allah yasa da gaske ne"
"Sosai ma"
"Kaka to ya naga ke baki shirya ba?
" Shirin me kuma"
"Na zuwa party mana"
Dariya tayi "raba ni da shirme"
Nafisa ce ta shigo tana tambayar Kaka"a saka kayan yaji a ruwan shayin dake kan wuta?
"A'a barshi kinsan Surajo baya son yaji ko kaɗan,har balle barkono,idan ya nuna kawai ki tace sai a saka a fulas"
Da to ta amsa tana wucewa,
Hiran su suka cigaba dayi tana danna mata kafa,
Daga bisani tace ma kaka bari ta je tayi fitsari,tana shiga dakin Nafisa ta same ta a ciki tana ninke kaya,dan haka fita tayi ta zagaya ta kicin,
Ganin karamin fulas mai kyau yasa ta buɗe,ganin shayin ne a ciki yasa da sauri ta shiga dudduba durowoyin kicin ɗin,ganin garin Barkono yasa da sauri ta diba ta zuba a kofi,sannan ta zuba ruwa,yana dan kwantawa ta samu karamin lariya ta tace,sannan ta buɗe karamin fulas din ta zuba kusan rabi a ciki sannan ta mai da komai ta ajiye ta fito,
Dawowa falo tayi ta zauna ta cigaba da danna ma kaka ƙafa,
Ba jimawa sai kuwa gashi ya shigo shida Salman yana rike da wani karamin jakka a hannun shi,
Sai da ya gaida kaka kafin ya zauna,
"Kai kuma jakkan waye a hannun ka?cewar Kaka tana kallon Salman,
Mai da jakkan gefe yayi" Na yaya Suraj ne"
"Salmanu shiga kicin ka dauko ma yayanku ƙaramin fulas da kofi ka kawo mai"
Murmushi yayi"yauwa dama shi yasa na biyo Yaya dan in sha "ya faɗa yana shigewa kicin,
Ba jimawa sai gashi ya dawo harda kofuna guda biyu a hannun shi,
Budewa yayi ya fara zuba ma yayan shi sannan ya miƙa mashi,
Ajiye wayar dake hannun shi yayi ya karba kofin yana faɗin " Thank "
Kai Kofin bakin shi yayi yana shakan ƙanshin shayin idanun shi a lumshe,sai kuma ya buɗe ya juyo yana fuskantar Kaka,
Da sauri ta kauda kai daga haɗa idon da suka yi tana cigaba da matsa ma Kaka kafa,
"Waye ya dafa shayin?
" Khadija na saka tayi haɗin komai,sai kuma Nafisa dana saka ta tace shayin ta zuba a fulas"
Ajiye kofin yayi,ya kalle Salmanu dake ƙoƙarin kai kofin bakin shi"je ka kiramin Khadijah "
Ajiye kofin yayi ya fita da sauri dan Allah_Allah yake ta dawo ya shaya shayin ahi,
Ba jimawa kuwa sai gashi ta shigo cikin yanga tana wani juyi cikin wani dogon riga na material data saka mai bala'in daukar ido,gashi ta sha makeup sosai,
Zama tayi gefen shi dan nisa da shi kaɗan,sai dai kuma ko kallo bata ishe shi ba,dan bai ma juya ya kalli inda take ba "Yaya Suraj gani"
Ba tare daya juyo ba yace"kira Nafisa "
Ta gane wa yake nufi dan haka a bakin kofar dakin Nafisa ta tsaya ta faɗi mata,
Tana dawowa tana kokarin zama ya nuna mata gaban shi,"dawo nan ki tsaya"
Nan take gabanta ya yanke ya faɗi,ganin yanda yayi maganar a dake,babu alamar fara'a a fuskar shi,ko wasa,to me tayi,domin ta san duk wanda zai ce ma ya tsaya a gaban shi to ba alkhairi bane,tambayar kanta ta fara tana tunanin abinda tayi a yinin yau,
Cikin sanyi jiki ta tako ta tsugunna a banshi tana karanto duk addu'ar dake bakin shi,
Kallon Nafisa yayi wacce ta iso tana kokarin dukawa a gefe ya nuna mata gaban shi kusa da Khadija,alamun ta tsaya a wurin ita ma,
Sake ƙafar Kaka tayi ta juyo tana jiran taga meke shirin faruwa,
Gani tayi ya juyo kanta kafin su haɗa ido da sauri ta kauda kai gefe,amma duk da haka sai da yace"ke ma dawo nan"
Da sauri ta juyo tana waro mai dara_daran idanun ta tana buɗe su a kanshi,tare da nuna kanta"Ni?
Mai bata amsaba shima sai madaidaitan adanunshi daya sauke a kanta,alamun tabbatar wa,
Ita dai Kaka tana kallon ikon Allah,
Ganin yanda ya jera su a gaban shi duk su uku......
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*25*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*
Kallon Salman yayi "ɗauko wani kofin a kicin"
Tashi yayi ya dauko mai yana mamakin me zai yi da wani kofi kuma,"dauko shayin ka"
Nuna ma Khadija wanda ke cikin kofin yayi,"ɗauka"
Cikin sauri ta dauka babu musu,
Ɗayan kofin da Salman ya kawo ya nuna ma Nafisa "juye na cikin fulas ki ɗauka"ita ma haka tayi,
Shi kuma Salman cikin girmamawa yace"yaya gashi"
Nuna Biba yaya,domin shayin kofin Salman yafi nashi yawa"bata"
Kallon yayan nashi yayi ya kalli shayin shi da ya kwallafa ma rai,sai dai ba damar tambaya in ba haka ba ya ja ma kanshi,mika ma Biba yayi,
Sai dai sam taki karɓa sai ma kauda kai da tayi,kara mika mata Salman yayi amma taki kula shi,
Ɗan murmushin gefen baki ya saki wanda lokacin yayi dai-dai da dago kai da tai ta kalle shi,bata san sanda ta furta masha Allah ba a zuciyar ta,tunda take ganin shi bata taba tsayawa ta mai kallo koda sakon goma ba ne sai yau,idan ana maganar kyau da gayu aka zo nan an kai iyaka,fari ne shi sosai irin tas ɗin nan,idanun shi matsakaita ne farare tas dasu,sai dai kuma bakin cikin idanun ba baƙi bane brown ne mai matukar daukar hankali irin wanda ba kowa bane ke iya jure haɗa idanu da shi,
Giran shi a cike yake gazar_gazar baki kirin,sai dai ita tunda take bata taba ganin namiji mai tsayin giran ido mai matuƙar jan hankali ba irin nashi,idan yana kallon kasa zaka ɗauka idanun shi a rufe suke kamar dai yanzun da duk umurnin da yake basu hankalin shi nakan wayar da yake dannawa,idan kuma aka gangaro kan Lips din shi,ji tayi tsigar jikin ta na tashi kallon su kawai da tayi,domin gasu yan kanana jawur da su,har wani maiko suke na daukar hankali yanda kasan ya shafa masu man baki,
Gaskiya ba shi ba babban baki yanda kasan na mata,zuciyar ta ne ya raya mata ko dai mace Allah ya so ya halicce shi,sai kuma aka yi shi namiji,
Sai dai kuma suman kanshi ba mai laushi bane,ko irin mai kwantawar nan a'a,mai ƙarfi ne dan a tsaye yake yashe kyara an aske gefe_da gefe sai kyallin maiko yake yi,gashi baki kirin yanda kasan ta saka bakin abu,
Nan take taji kishi ya kamata,wallahi wannan ko tantama bata yi yafita kyau nisa ba kusa ba,haba dan Allah ai dole yayi yanga ya kuma wulakanta mata,
Tun ranar farko da ta fara tsayawa kusa dashi take maitan ta gano wani kalan turare yake amfani dashi,sai dai ta kasa gani wani irin kanshi ne wannan,
Domin kamshi ne dake fita a hankali_a hankali yake mamaye wurin da yake,sabanin wani turaren da tun mutum na nisa da kai zaka fahimci zuwan shi saboda kamshin turaren shi,amma nashi sai ya iso daf da daf sannan kamshin zai fara tashi yana mamaye wuri har balle idan ace ya zauna ne to ba'a magana,a takaice kamshi ne mai kashe zuciya da saka nasuwa,
Ji tayi cikin sanyin muryar nan nashi wanda baya fita da hayaniya yace"idan kin gama ƙare min kallo ki amsa abinda ake baki"
Lumshe ido tayi sannan ta buɗe a hankali saboda sai da ya ɗan matso kusa da ita kaɗan sannan yayi maganar,yayin da daddadar ƙanshin dake fitowa daka bakin shi ya dake fuskarta,
Ba tare data ce komai ba ta amsa kofin da Salman din ke mika mata,kanta a duke saboda tsare ta da ido da yayi,
Nurudeen ne ya shigo da sallamah yana faɗin "Kaka ina kayan dana baki ajiya?
Miƙa mashi hannu tayi" Kaga zo ka taimaka min na shiga ciki,tunda an gama wa'azin "
Kallon su yayi ya Suraj dake zaune ya daura kafa daya kan daya,nuna su yayi"su kuma waɗannan fa kamar masu niman gafara "
"Aikin ɗan uwan ka ne,ni zo ka daga ni"
Kallon Biba yayi,sannan yaje ya taimaka ma Kaka ya kai ta daki,sannan ya fito dakin riƙe da leda a hannun shi,
A maimakon ya wuce sai niman wuri yayi ya zauna yana kallon su,
Kiran sunan ta yayi"Khadija "
Da sauri ta amsa"Na'am Yaya"
"Ajiye kofin ki wuce,'ya nuna Nafisa" Ke ma tashi ki tafi"
Cikin sauri duk suka ajiye kofin suka mike,
Ganin haka yasa itama ta ajiye kofin tana kokarin mikewa,
Wani irin tsawa daya daka mata sai da taji hanjin cikinta ya kaɗa,"who the hell are you to stand up ?
Ba ita kaɗai ba har su kansu basu san sanda suka koma suka tsugunna ba,
Domin ba zasu iya tuna randa yayan nasu yayi irin wannan tsawar ba,
Lallai yau an tabo shi,
Mugun kallon daya sakar masu ne yasa ba shiri suka ƙara mikewa suka bar shiyan gabaɗaya,har ita Nafisa da Salman,domin sun san yau kan Biba sai kuma ta Allah.
Nuna mata kofin dake gaban shi yayi"ɗauka ki shanye "
Duk da a tsananin tsorace take dashi karo na farko,amma hakan bai hana ta zaro ido ba tana girgiza kai,
Cikin sanyi da son sulhunta komai Nurudeen yace"Bro pls kayi haƙuri koma me ta maka ka yafe mata"
Nan take ya saki fuska harda sakin dan guntun murmushi yanda kasan ba shi ya gama tsorata su ba yace"is ok ni Bani da damuwa,kawai in kana son na haƙura ta ɗauki shayin nan ta shanye "
Kallon Biba yayi wacce tuni ta fara hawaye,saboda ta san Me a cikin shayin wanda gashi har tururi yake na zafi,
"Ok zata sha,badai shayin bane matsalar?to zata sha"
Ɗaga kafaɗa yayi"ok then"
Cikin muryar lallashi ya kira sunan ta"Biba "
Allah sarki jikin ta har bari yake ga hawaye duk ya wanke fuska ta juyo tana kallon shi"is ok ya isa,ki kwantar da hankalin ki I am with you,shayi ne kawai zaki sha,dan haka ki ɗauka ki sha sai ki wuce"
"Sosai ma"
"Kaka to ya naga ke baki shirya ba?
" Shirin me kuma"
"Na zuwa party mana"
Dariya tayi "raba ni da shirme"
Nafisa ce ta shigo tana tambayar Kaka"a saka kayan yaji a ruwan shayin dake kan wuta?
"A'a barshi kinsan Surajo baya son yaji ko kaɗan,har balle barkono,idan ya nuna kawai ki tace sai a saka a fulas"
Da to ta amsa tana wucewa,
Hiran su suka cigaba dayi tana danna mata kafa,
Daga bisani tace ma kaka bari ta je tayi fitsari,tana shiga dakin Nafisa ta same ta a ciki tana ninke kaya,dan haka fita tayi ta zagaya ta kicin,
Ganin karamin fulas mai kyau yasa ta buɗe,ganin shayin ne a ciki yasa da sauri ta shiga dudduba durowoyin kicin ɗin,ganin garin Barkono yasa da sauri ta diba ta zuba a kofi,sannan ta zuba ruwa,yana dan kwantawa ta samu karamin lariya ta tace,sannan ta buɗe karamin fulas din ta zuba kusan rabi a ciki sannan ta mai da komai ta ajiye ta fito,
Dawowa falo tayi ta zauna ta cigaba da danna ma kaka ƙafa,
Ba jimawa sai kuwa gashi ya shigo shida Salman yana rike da wani karamin jakka a hannun shi,
Sai da ya gaida kaka kafin ya zauna,
"Kai kuma jakkan waye a hannun ka?cewar Kaka tana kallon Salman,
Mai da jakkan gefe yayi" Na yaya Suraj ne"
"Salmanu shiga kicin ka dauko ma yayanku ƙaramin fulas da kofi ka kawo mai"
Murmushi yayi"yauwa dama shi yasa na biyo Yaya dan in sha "ya faɗa yana shigewa kicin,
Ba jimawa sai gashi ya dawo harda kofuna guda biyu a hannun shi,
Budewa yayi ya fara zuba ma yayan shi sannan ya miƙa mashi,
Ajiye wayar dake hannun shi yayi ya karba kofin yana faɗin " Thank "
Kai Kofin bakin shi yayi yana shakan ƙanshin shayin idanun shi a lumshe,sai kuma ya buɗe ya juyo yana fuskantar Kaka,
Da sauri ta kauda kai daga haɗa idon da suka yi tana cigaba da matsa ma Kaka kafa,
"Waye ya dafa shayin?
" Khadija na saka tayi haɗin komai,sai kuma Nafisa dana saka ta tace shayin ta zuba a fulas"
Ajiye kofin yayi,ya kalle Salmanu dake ƙoƙarin kai kofin bakin shi"je ka kiramin Khadijah "
Ajiye kofin yayi ya fita da sauri dan Allah_Allah yake ta dawo ya shaya shayin ahi,
Ba jimawa kuwa sai gashi ta shigo cikin yanga tana wani juyi cikin wani dogon riga na material data saka mai bala'in daukar ido,gashi ta sha makeup sosai,
Zama tayi gefen shi dan nisa da shi kaɗan,sai dai kuma ko kallo bata ishe shi ba,dan bai ma juya ya kalli inda take ba "Yaya Suraj gani"
Ba tare daya juyo ba yace"kira Nafisa "
Ta gane wa yake nufi dan haka a bakin kofar dakin Nafisa ta tsaya ta faɗi mata,
Tana dawowa tana kokarin zama ya nuna mata gaban shi,"dawo nan ki tsaya"
Nan take gabanta ya yanke ya faɗi,ganin yanda yayi maganar a dake,babu alamar fara'a a fuskar shi,ko wasa,to me tayi,domin ta san duk wanda zai ce ma ya tsaya a gaban shi to ba alkhairi bane,tambayar kanta ta fara tana tunanin abinda tayi a yinin yau,
Cikin sanyi jiki ta tako ta tsugunna a banshi tana karanto duk addu'ar dake bakin shi,
Kallon Nafisa yayi wacce ta iso tana kokarin dukawa a gefe ya nuna mata gaban shi kusa da Khadija,alamun ta tsaya a wurin ita ma,
Sake ƙafar Kaka tayi ta juyo tana jiran taga meke shirin faruwa,
Gani tayi ya juyo kanta kafin su haɗa ido da sauri ta kauda kai gefe,amma duk da haka sai da yace"ke ma dawo nan"
Da sauri ta juyo tana waro mai dara_daran idanun ta tana buɗe su a kanshi,tare da nuna kanta"Ni?
Mai bata amsaba shima sai madaidaitan adanunshi daya sauke a kanta,alamun tabbatar wa,
Ita dai Kaka tana kallon ikon Allah,
Ganin yanda ya jera su a gaban shi duk su uku......
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*25*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*
Kallon Salman yayi "ɗauko wani kofin a kicin"
Tashi yayi ya dauko mai yana mamakin me zai yi da wani kofi kuma,"dauko shayin ka"
Nuna ma Khadija wanda ke cikin kofin yayi,"ɗauka"
Cikin sauri ta dauka babu musu,
Ɗayan kofin da Salman ya kawo ya nuna ma Nafisa "juye na cikin fulas ki ɗauka"ita ma haka tayi,
Shi kuma Salman cikin girmamawa yace"yaya gashi"
Nuna Biba yaya,domin shayin kofin Salman yafi nashi yawa"bata"
Kallon yayan nashi yayi ya kalli shayin shi da ya kwallafa ma rai,sai dai ba damar tambaya in ba haka ba ya ja ma kanshi,mika ma Biba yayi,
Sai dai sam taki karɓa sai ma kauda kai da tayi,kara mika mata Salman yayi amma taki kula shi,
Ɗan murmushin gefen baki ya saki wanda lokacin yayi dai-dai da dago kai da tai ta kalle shi,bata san sanda ta furta masha Allah ba a zuciyar ta,tunda take ganin shi bata taba tsayawa ta mai kallo koda sakon goma ba ne sai yau,idan ana maganar kyau da gayu aka zo nan an kai iyaka,fari ne shi sosai irin tas ɗin nan,idanun shi matsakaita ne farare tas dasu,sai dai kuma bakin cikin idanun ba baƙi bane brown ne mai matukar daukar hankali irin wanda ba kowa bane ke iya jure haɗa idanu da shi,
Giran shi a cike yake gazar_gazar baki kirin,sai dai ita tunda take bata taba ganin namiji mai tsayin giran ido mai matuƙar jan hankali ba irin nashi,idan yana kallon kasa zaka ɗauka idanun shi a rufe suke kamar dai yanzun da duk umurnin da yake basu hankalin shi nakan wayar da yake dannawa,idan kuma aka gangaro kan Lips din shi,ji tayi tsigar jikin ta na tashi kallon su kawai da tayi,domin gasu yan kanana jawur da su,har wani maiko suke na daukar hankali yanda kasan ya shafa masu man baki,
Gaskiya ba shi ba babban baki yanda kasan na mata,zuciyar ta ne ya raya mata ko dai mace Allah ya so ya halicce shi,sai kuma aka yi shi namiji,
Sai dai kuma suman kanshi ba mai laushi bane,ko irin mai kwantawar nan a'a,mai ƙarfi ne dan a tsaye yake yashe kyara an aske gefe_da gefe sai kyallin maiko yake yi,gashi baki kirin yanda kasan ta saka bakin abu,
Nan take taji kishi ya kamata,wallahi wannan ko tantama bata yi yafita kyau nisa ba kusa ba,haba dan Allah ai dole yayi yanga ya kuma wulakanta mata,
Tun ranar farko da ta fara tsayawa kusa dashi take maitan ta gano wani kalan turare yake amfani dashi,sai dai ta kasa gani wani irin kanshi ne wannan,
Domin kamshi ne dake fita a hankali_a hankali yake mamaye wurin da yake,sabanin wani turaren da tun mutum na nisa da kai zaka fahimci zuwan shi saboda kamshin turaren shi,amma nashi sai ya iso daf da daf sannan kamshin zai fara tashi yana mamaye wuri har balle idan ace ya zauna ne to ba'a magana,a takaice kamshi ne mai kashe zuciya da saka nasuwa,
Ji tayi cikin sanyin muryar nan nashi wanda baya fita da hayaniya yace"idan kin gama ƙare min kallo ki amsa abinda ake baki"
Lumshe ido tayi sannan ta buɗe a hankali saboda sai da ya ɗan matso kusa da ita kaɗan sannan yayi maganar,yayin da daddadar ƙanshin dake fitowa daka bakin shi ya dake fuskarta,
Ba tare data ce komai ba ta amsa kofin da Salman din ke mika mata,kanta a duke saboda tsare ta da ido da yayi,
Nurudeen ne ya shigo da sallamah yana faɗin "Kaka ina kayan dana baki ajiya?
Miƙa mashi hannu tayi" Kaga zo ka taimaka min na shiga ciki,tunda an gama wa'azin "
Kallon su yayi ya Suraj dake zaune ya daura kafa daya kan daya,nuna su yayi"su kuma waɗannan fa kamar masu niman gafara "
"Aikin ɗan uwan ka ne,ni zo ka daga ni"
Kallon Biba yayi,sannan yaje ya taimaka ma Kaka ya kai ta daki,sannan ya fito dakin riƙe da leda a hannun shi,
A maimakon ya wuce sai niman wuri yayi ya zauna yana kallon su,
Kiran sunan ta yayi"Khadija "
Da sauri ta amsa"Na'am Yaya"
"Ajiye kofin ki wuce,'ya nuna Nafisa" Ke ma tashi ki tafi"
Cikin sauri duk suka ajiye kofin suka mike,
Ganin haka yasa itama ta ajiye kofin tana kokarin mikewa,
Wani irin tsawa daya daka mata sai da taji hanjin cikinta ya kaɗa,"who the hell are you to stand up ?
Ba ita kaɗai ba har su kansu basu san sanda suka koma suka tsugunna ba,
Domin ba zasu iya tuna randa yayan nasu yayi irin wannan tsawar ba,
Lallai yau an tabo shi,
Mugun kallon daya sakar masu ne yasa ba shiri suka ƙara mikewa suka bar shiyan gabaɗaya,har ita Nafisa da Salman,domin sun san yau kan Biba sai kuma ta Allah.
Nuna mata kofin dake gaban shi yayi"ɗauka ki shanye "
Duk da a tsananin tsorace take dashi karo na farko,amma hakan bai hana ta zaro ido ba tana girgiza kai,
Cikin sanyi da son sulhunta komai Nurudeen yace"Bro pls kayi haƙuri koma me ta maka ka yafe mata"
Nan take ya saki fuska harda sakin dan guntun murmushi yanda kasan ba shi ya gama tsorata su ba yace"is ok ni Bani da damuwa,kawai in kana son na haƙura ta ɗauki shayin nan ta shanye "
Kallon Biba yayi wacce tuni ta fara hawaye,saboda ta san Me a cikin shayin wanda gashi har tururi yake na zafi,
"Ok zata sha,badai shayin bane matsalar?to zata sha"
Ɗaga kafaɗa yayi"ok then"
Cikin muryar lallashi ya kira sunan ta"Biba "
Allah sarki jikin ta har bari yake ga hawaye duk ya wanke fuska ta juyo tana kallon shi"is ok ya isa,ki kwantar da hankalin ki I am with you,shayi ne kawai zaki sha,dan haka ki ɗauka ki sha sai ki wuce"