Sashe 71
Yar Tsanar Zinari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ranar a gidan ya kwana,yayin da yanda yaga rana haka yaga dare,sai dai banbancin shine bai bata lokacin shi a banza ba,domin Alwallah ya dauro yana mika kukan shi da godiyar shi a wurin Allah mai yin yanda ya so.
Bashi ya kwanta ba sai bayan ya dawo daga sallar Asuba sannan bacci ya dauke shi,
Jin yanda wayar shi ke ta ƙara ne ya tayar dashi daga nauyayyen baccin da yake yi,
A hankali yake buɗe idanun shi yana lumshewa har sai da ya tabbatar da ganin shi ya dawo dai-dai sannan ya mike zaune,nan ma bai tashi kai tsaye ba saboda yasan illar dake tattare da mutum yana farkawa daga bacci yayi saurin tashi,
Sai da ya ƙara mintuna uku kafin ya mike tsaye ya nufi ban ɗaki,
Wanka yayi cikin sauri ya shirya cikin Kananan kaya da jaket na maza wanda kayan ba karamin fitowa dashi sukayi ba,sai baƙin facing cap daya saka saman lafiyayyen gyararren gashin kanshi,wanda yasha Kalolin mayuka masu matukar kamshi,
Turaren shi mai matukar sanyin kamshi ya fesa sannan ya mai da ya ajiye,
Fuskar nan nashi har wani ƙyalli yake da ɗaukar ido,yayin da kwarjinin shi yake karuwa a duk lokacin da zaka daura idanun ka a kanshi,
Ko kaɗan yau babu fara'a a fuskarshi,domin yau yan halin na kusa,
Agogon Azirfar dake ajiye gaban madubi ya ɗauka ya saka a hannun shi sannan ya fito bayan ya ɗauki makullin daya daga cikin sabbin motocin dake fake a cikin gidan a wani keɓantaccen wurin wanda in dai ba lura kayi ba da wuya ka gane a kwai wannan garejin a gidan,
Wata Musulman mota baka katuwa mai numfashi ya buɗe,wanda sai ƙyalli da daukar ido irin na niman magana yake yi,
Irin motar nan ne da manyan masu kuɗin Larabawa zaka ga suna hawa,saboda su basu son karamin mota,to irin ta ne,
Kunnawa yayi ya tayar sannan ya bar harabar gidan cikin kwarewa,da iya sarrafata,
Tunda ya shigo layin unguwar duk in da ya gefta kallon mitar ake yi,wasu har leke suke yi suga a ina zai tsaya,
Bai shigar da motar cikin gida ba dan yasan ba jimawa zai yi a ciki ba zai fito shi yasa ya faka ta a waje,
Duk suna tsaye a ƙofar gidan wasu a zaune,kasancewar a kwai ɗaurin auren da aka gama gabatarwa yanzun,
Kallon motar kawai suke yi suna jira suga wani hamshaki ne zai fito daga ciki,sai dai tsayin sakanni ba'a buɗe ba,kai babu ma wata alama da zai nuna maka na cikin motar nada niyar fitowa,
Kallon Nurudeen yayi"gaskiya duk me wannan motar ba karamin tarawa yayi ba,wata biyu kenan da akayi Lunching dinta a Saudiyya"
Ɗayan gayen dake tare dasu ne yace"ai Ibrahim ni wallahi ko wanke wannan motar aka bani na kwana daya an gama min ko mai "
Duka ya kai mashi yana dariya,
Shi dai nurudeen bai basu amsa ba,ya dai zuba ma motar ido ne kawai,domin kusan wata shida kenan tunda aka fara tallar motar ya fara tara kuɗi domin siyan ta sai dai ko rabin rabi har yanzun bai hada ba,duk da Dream Car din shi ne sai dai ya fara cire rai,dan yasan sama tayi ma yaro nisa,kai shi bai ma ɗauka a Nigeria an samu wanda ya shigo da ita ba sai yanzun da yake ganin ta a gaban shi,
Lallai ko waye mai wannan motar to ba karamin kusa bane ko dai a gwamnati ko kuma a wani masarautar,shi jira kawai yake yaga waye a cikin ta.
Sai da ya gama amsa wayar da yake yi kafin ya buɗe marfin motar ya sako kafar shi mai ɗauke da takalmi but farare sabon dizai wanda ba sai an faɗa maka ba kasan bana sawar yara bane,
Karasa fitowa yayi ya maida ƙofar motar ya kulle hannun shi riƙe da wayar shi ya doshi hanyar shiga cikin gida yayin da ya cire facing cap ɗin dake saman kanshi.
Duk da kallon Mamaki suka raka shi har ya bulle ma ganin su ba tare dashi yasan ma suna yi ba,
Basu kadai ba duk wani wanda hankalin shi ke kan fakawar wannan motar sai da yayi mamakin ganin wanda ya fito,domin sun san cewa a rayuwarshi shi mutum ne ba mai fariya ba,da wuya kaga ma yana tuka mota da kanshi,in ma zai tuka to sai dai ya shiga na matsakaita kuɗi,dan har akwai wata rana da Ibrahim ya taɓa mai gatse,akan cewar mu dai munji ance kun gaji dukiya sai dai ko kadan banga alama ba,ƙila ma faɗi ne irin na mutane,domin meshi ai baya taɓa ɓoyewa,
A lokacin girgiza kai kawai yayi ya wuce ba tare da ya ce mashi komai ba,
Da hannu yayi nuni"wannan ba Suraj bane?
Kafin su bashi amsa ne sai ga Dady ya iso in da suke"waye ya ajiye wannan motar a nan?ko anyi baƙo ne?
Girgiza kai Nurudeen yayi cikin disashewar murya yace"Suraj ne"
Shima sai da ya kara kallon motar na saƙonni kafin ya juya ya doshi cikin gida.
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*71*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*
Cikin natsuwa yake tafiya tamkar wanda baida wani damuwa a zuciyar,ya doshi shiyan Kaka,
Da Sallamah ya shiga, tana ganin shi ta shiga washe baki tana dariya wanda hakan ya saka shi murmusawa,
Da sauri Khadija ta tashi daga inda take zaune kasancewar yawancin lokuta yafi zama a nan wurin,
"Yaya ga wuri"
Bai amsa mata ba sai ma zaunawa da yayi kusa da Kaka,
"Tsohuwa barka da safiya"
"Da fatan ka tashi lafiya,?
Bai bata amsa ba sai ma cewa da yayi" Me zan samu na ci?
Kallon Mejiddarh tayi data yi zaune ta tsira mashi ido kamar taga sabon hallita,
Dauke idonta tayi a kan ta tace"ke Balki dauko ma Surajo Kunun tsamiya yana nan cikin fulas a kicin"
Da sauri ta mike ta nufi kicin din domin dauko masa,
Khadija ce ta mike tabi bayanta "bari na taimaka mata wurin dauko kulan kosai da kofi"
Ba wanda ya bata amsa har ta shige ita ma,
Karo suka ci da sauri ta karasa shiga tana jawota baya"ke kinga abinda na gani?
Hararanta tayi"ke dai Khadijah anyi Uwar gulma,yanzun har kin ga wani abu"
Dariya ta saka,sai kuma ta toshe bakinta da sauri tana zaro ido"ba ki lura da kallon da Aunty maijiddarh take masa ba?
"Wani irin kallo kenan?
Duka takai mata a kafaɗa" Irin kallon dan Allah ka kula ni "
Juya ido tayi"ina lura da komai,shima kuma yau naga kamar yan miskilancin sun motsa baki ga yanda ko amsa gaisuwar mu bai yi ba?
Kafin ta bata amsa ne suka ji muryar Kaka na fadin"wai Kunun yaki daukuwa ne?
A tare suka amsa da faɗin "gani nan zuwa"
Rike mata hannu tayi tana kashe mata ido"sai dai fa ya haɗu Balki babu karya,yau na daban ne"
Fisge hannun ta tayi tana yin gaba tare da fadin "ba kida hankali tunda so kike ya sheke mu"
Ajiye mai fulas din tayi a gaban shi sannan ta tsugunna ta tsiyaya mashi,
Ba tare da ya ce mata komai ba ya ɗauka ya fara sha a hankali,
Shigowar su Ibrahim da Nurudeen ne yasa ya dan daga kai ya masu kallo daya sannan ya dauke kai yana cigaba da kurban kunan shi,
Wanda hakan da yayi ba karamin tsayama daya daga cikin su a rai yayi ba,
"Ya jikin Habiba Surajo?an samu an mata aikin kuwa?
Jujjuya kofin dake hannun shi yake yi wanda ya kusa kammalawa" Ba ayi ba "
Cikin nuna damuwa tace"me yasa,ko an fasa aikin ne?
Ajiye kofin yayi"ba'a fasa ba za ayi amma ba yanzun ba,"
Ganin tana shirin ƙara jeho mashi wani tambayar ne yasa yace"akwai wasu gwaje_gwajen da ya kamata su kara yi mata,da zaran sun kammala za ayi"
Ibrahim ne yace "Bro gaskiya motar nan daka shigo da ita ta cije ni"
Kallon rashin fahimta yake mashi,
Dariya yayi kaɗan "ina nufin motar ya haɗu,kasan nawa naji kudinta kuwa,ai ban dauka an samu wanda ya shigo da ita Nigeria ba saboda wata biyu kenan da ya fito kuma a Saudiya aka yi Lunching din ta"
Ganin bai da niyar gama jawabin shine yasa ya mike yana faɗin "Kaka zan fita sai zuwa anjima"
"To Allah ya tsare Surajo"
"In zo ka rage min hanya"ya tambaya dan kawai ya shiga motar ya kafa tarihi a cewar shi,
Bai bashi amsa ba har sai da ya kusa barin falon sannan yace" Ba yau ba"
Dariya su Khadijah suka saka ganin yanda ya ɓata fuska,harara ya dalla masu"bakuda hankali baku san irin motar da nake magana ba ne?
"Ni kan wani irin mota ne haka da har zaka yi marmarin hawa bayan duk irin motocin dake cikin gidan nan"
Karamin tsaki yaja "bari dai na nuna maku abinda nake magana akai," Nan ya ciro waya ya bude data cikin yan mintuna yayi downloading hoton motar sannan ya mika ma Maijidda"kalli mota ki gani tamkar wani jirgin ruwa"
Amsa ta yi tana dubawa yayin da take yin kasa da hoton domin duba kudin mitar,
Ai babu shiri ta buɗe ido cikin tsananin mamaki,
"Kaka kin ga kudin motar nan kuwa? Yanzun irin motar nan Yaya Suraj ya ke dashi?
" Ita ma ya hau yau,idan har bai wuce ba kina fita kofar gida zaki ganta fake "
Fisge wayar Balki taki"ku bamu mu kashe kwarkwatan ido"
Shigowar Hajiya Saude ne ya katse su wacce ke tambayar "cin mu sun ne ake yi?
Balki ce ta mika mata wayar" Momy kalli motar da yaya Suraj yake da,kalli kuɗin motar,
Idan har yana da kudin siyan wannan motar to wani irin kuɗi kenan yake dashi "
Amsar wayar tayi tana dubawa"yanzun Suraj ne yake da irin wannan motar?
"Sosai ma kuwa"
Bashi ya kwanta ba sai bayan ya dawo daga sallar Asuba sannan bacci ya dauke shi,
Jin yanda wayar shi ke ta ƙara ne ya tayar dashi daga nauyayyen baccin da yake yi,
A hankali yake buɗe idanun shi yana lumshewa har sai da ya tabbatar da ganin shi ya dawo dai-dai sannan ya mike zaune,nan ma bai tashi kai tsaye ba saboda yasan illar dake tattare da mutum yana farkawa daga bacci yayi saurin tashi,
Sai da ya ƙara mintuna uku kafin ya mike tsaye ya nufi ban ɗaki,
Wanka yayi cikin sauri ya shirya cikin Kananan kaya da jaket na maza wanda kayan ba karamin fitowa dashi sukayi ba,sai baƙin facing cap daya saka saman lafiyayyen gyararren gashin kanshi,wanda yasha Kalolin mayuka masu matukar kamshi,
Turaren shi mai matukar sanyin kamshi ya fesa sannan ya mai da ya ajiye,
Fuskar nan nashi har wani ƙyalli yake da ɗaukar ido,yayin da kwarjinin shi yake karuwa a duk lokacin da zaka daura idanun ka a kanshi,
Ko kaɗan yau babu fara'a a fuskarshi,domin yau yan halin na kusa,
Agogon Azirfar dake ajiye gaban madubi ya ɗauka ya saka a hannun shi sannan ya fito bayan ya ɗauki makullin daya daga cikin sabbin motocin dake fake a cikin gidan a wani keɓantaccen wurin wanda in dai ba lura kayi ba da wuya ka gane a kwai wannan garejin a gidan,
Wata Musulman mota baka katuwa mai numfashi ya buɗe,wanda sai ƙyalli da daukar ido irin na niman magana yake yi,
Irin motar nan ne da manyan masu kuɗin Larabawa zaka ga suna hawa,saboda su basu son karamin mota,to irin ta ne,
Kunnawa yayi ya tayar sannan ya bar harabar gidan cikin kwarewa,da iya sarrafata,
Tunda ya shigo layin unguwar duk in da ya gefta kallon mitar ake yi,wasu har leke suke yi suga a ina zai tsaya,
Bai shigar da motar cikin gida ba dan yasan ba jimawa zai yi a ciki ba zai fito shi yasa ya faka ta a waje,
Duk suna tsaye a ƙofar gidan wasu a zaune,kasancewar a kwai ɗaurin auren da aka gama gabatarwa yanzun,
Kallon motar kawai suke yi suna jira suga wani hamshaki ne zai fito daga ciki,sai dai tsayin sakanni ba'a buɗe ba,kai babu ma wata alama da zai nuna maka na cikin motar nada niyar fitowa,
Kallon Nurudeen yayi"gaskiya duk me wannan motar ba karamin tarawa yayi ba,wata biyu kenan da akayi Lunching dinta a Saudiyya"
Ɗayan gayen dake tare dasu ne yace"ai Ibrahim ni wallahi ko wanke wannan motar aka bani na kwana daya an gama min ko mai "
Duka ya kai mashi yana dariya,
Shi dai nurudeen bai basu amsa ba,ya dai zuba ma motar ido ne kawai,domin kusan wata shida kenan tunda aka fara tallar motar ya fara tara kuɗi domin siyan ta sai dai ko rabin rabi har yanzun bai hada ba,duk da Dream Car din shi ne sai dai ya fara cire rai,dan yasan sama tayi ma yaro nisa,kai shi bai ma ɗauka a Nigeria an samu wanda ya shigo da ita ba sai yanzun da yake ganin ta a gaban shi,
Lallai ko waye mai wannan motar to ba karamin kusa bane ko dai a gwamnati ko kuma a wani masarautar,shi jira kawai yake yaga waye a cikin ta.
Sai da ya gama amsa wayar da yake yi kafin ya buɗe marfin motar ya sako kafar shi mai ɗauke da takalmi but farare sabon dizai wanda ba sai an faɗa maka ba kasan bana sawar yara bane,
Karasa fitowa yayi ya maida ƙofar motar ya kulle hannun shi riƙe da wayar shi ya doshi hanyar shiga cikin gida yayin da ya cire facing cap ɗin dake saman kanshi.
Duk da kallon Mamaki suka raka shi har ya bulle ma ganin su ba tare dashi yasan ma suna yi ba,
Basu kadai ba duk wani wanda hankalin shi ke kan fakawar wannan motar sai da yayi mamakin ganin wanda ya fito,domin sun san cewa a rayuwarshi shi mutum ne ba mai fariya ba,da wuya kaga ma yana tuka mota da kanshi,in ma zai tuka to sai dai ya shiga na matsakaita kuɗi,dan har akwai wata rana da Ibrahim ya taɓa mai gatse,akan cewar mu dai munji ance kun gaji dukiya sai dai ko kadan banga alama ba,ƙila ma faɗi ne irin na mutane,domin meshi ai baya taɓa ɓoyewa,
A lokacin girgiza kai kawai yayi ya wuce ba tare da ya ce mashi komai ba,
Da hannu yayi nuni"wannan ba Suraj bane?
Kafin su bashi amsa ne sai ga Dady ya iso in da suke"waye ya ajiye wannan motar a nan?ko anyi baƙo ne?
Girgiza kai Nurudeen yayi cikin disashewar murya yace"Suraj ne"
Shima sai da ya kara kallon motar na saƙonni kafin ya juya ya doshi cikin gida.
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*71*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*
Cikin natsuwa yake tafiya tamkar wanda baida wani damuwa a zuciyar,ya doshi shiyan Kaka,
Da Sallamah ya shiga, tana ganin shi ta shiga washe baki tana dariya wanda hakan ya saka shi murmusawa,
Da sauri Khadija ta tashi daga inda take zaune kasancewar yawancin lokuta yafi zama a nan wurin,
"Yaya ga wuri"
Bai amsa mata ba sai ma zaunawa da yayi kusa da Kaka,
"Tsohuwa barka da safiya"
"Da fatan ka tashi lafiya,?
Bai bata amsa ba sai ma cewa da yayi" Me zan samu na ci?
Kallon Mejiddarh tayi data yi zaune ta tsira mashi ido kamar taga sabon hallita,
Dauke idonta tayi a kan ta tace"ke Balki dauko ma Surajo Kunun tsamiya yana nan cikin fulas a kicin"
Da sauri ta mike ta nufi kicin din domin dauko masa,
Khadija ce ta mike tabi bayanta "bari na taimaka mata wurin dauko kulan kosai da kofi"
Ba wanda ya bata amsa har ta shige ita ma,
Karo suka ci da sauri ta karasa shiga tana jawota baya"ke kinga abinda na gani?
Hararanta tayi"ke dai Khadijah anyi Uwar gulma,yanzun har kin ga wani abu"
Dariya ta saka,sai kuma ta toshe bakinta da sauri tana zaro ido"ba ki lura da kallon da Aunty maijiddarh take masa ba?
"Wani irin kallo kenan?
Duka takai mata a kafaɗa" Irin kallon dan Allah ka kula ni "
Juya ido tayi"ina lura da komai,shima kuma yau naga kamar yan miskilancin sun motsa baki ga yanda ko amsa gaisuwar mu bai yi ba?
Kafin ta bata amsa ne suka ji muryar Kaka na fadin"wai Kunun yaki daukuwa ne?
A tare suka amsa da faɗin "gani nan zuwa"
Rike mata hannu tayi tana kashe mata ido"sai dai fa ya haɗu Balki babu karya,yau na daban ne"
Fisge hannun ta tayi tana yin gaba tare da fadin "ba kida hankali tunda so kike ya sheke mu"
Ajiye mai fulas din tayi a gaban shi sannan ta tsugunna ta tsiyaya mashi,
Ba tare da ya ce mata komai ba ya ɗauka ya fara sha a hankali,
Shigowar su Ibrahim da Nurudeen ne yasa ya dan daga kai ya masu kallo daya sannan ya dauke kai yana cigaba da kurban kunan shi,
Wanda hakan da yayi ba karamin tsayama daya daga cikin su a rai yayi ba,
"Ya jikin Habiba Surajo?an samu an mata aikin kuwa?
Jujjuya kofin dake hannun shi yake yi wanda ya kusa kammalawa" Ba ayi ba "
Cikin nuna damuwa tace"me yasa,ko an fasa aikin ne?
Ajiye kofin yayi"ba'a fasa ba za ayi amma ba yanzun ba,"
Ganin tana shirin ƙara jeho mashi wani tambayar ne yasa yace"akwai wasu gwaje_gwajen da ya kamata su kara yi mata,da zaran sun kammala za ayi"
Ibrahim ne yace "Bro gaskiya motar nan daka shigo da ita ta cije ni"
Kallon rashin fahimta yake mashi,
Dariya yayi kaɗan "ina nufin motar ya haɗu,kasan nawa naji kudinta kuwa,ai ban dauka an samu wanda ya shigo da ita Nigeria ba saboda wata biyu kenan da ya fito kuma a Saudiya aka yi Lunching din ta"
Ganin bai da niyar gama jawabin shine yasa ya mike yana faɗin "Kaka zan fita sai zuwa anjima"
"To Allah ya tsare Surajo"
"In zo ka rage min hanya"ya tambaya dan kawai ya shiga motar ya kafa tarihi a cewar shi,
Bai bashi amsa ba har sai da ya kusa barin falon sannan yace" Ba yau ba"
Dariya su Khadijah suka saka ganin yanda ya ɓata fuska,harara ya dalla masu"bakuda hankali baku san irin motar da nake magana ba ne?
"Ni kan wani irin mota ne haka da har zaka yi marmarin hawa bayan duk irin motocin dake cikin gidan nan"
Karamin tsaki yaja "bari dai na nuna maku abinda nake magana akai," Nan ya ciro waya ya bude data cikin yan mintuna yayi downloading hoton motar sannan ya mika ma Maijidda"kalli mota ki gani tamkar wani jirgin ruwa"
Amsa ta yi tana dubawa yayin da take yin kasa da hoton domin duba kudin mitar,
Ai babu shiri ta buɗe ido cikin tsananin mamaki,
"Kaka kin ga kudin motar nan kuwa? Yanzun irin motar nan Yaya Suraj ya ke dashi?
" Ita ma ya hau yau,idan har bai wuce ba kina fita kofar gida zaki ganta fake "
Fisge wayar Balki taki"ku bamu mu kashe kwarkwatan ido"
Shigowar Hajiya Saude ne ya katse su wacce ke tambayar "cin mu sun ne ake yi?
Balki ce ta mika mata wayar" Momy kalli motar da yaya Suraj yake da,kalli kuɗin motar,
Idan har yana da kudin siyan wannan motar to wani irin kuɗi kenan yake dashi "
Amsar wayar tayi tana dubawa"yanzun Suraj ne yake da irin wannan motar?
"Sosai ma kuwa"