Sashe 3
Yar Tsanar Zinari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sake baki nayi ina kallon ikon Allah,domin falon karan kanshi abin kallo ne,dan ba karamin dukiya aka kashe mashi ba,zaka iya yin mamaki ganin irin wannan haɗaɗɗen falon a cikin wannan gidan,
Ko wacce wani kofa naga ta buɗe ta shiga wanda daga dukkan alamu nanne ɗakinta,
Zama tayi a bakin gado tana sauke ajiyar zuciya,
Rinbon ɗin dake kanta ta cire tana ba suman kanta damar zubowa har gadon bayan ta,
Ɗayan wayar ta ciro daga cikin jakkan tana saka Sim card din data cire a bayan wayar ta kunna,kafin ta gama kawowa ne naga ta jawo dirowar dake gefen gado ta ciro wani kwali wanda ban gane me a ciki ba sai lokacin dana ga ta zaro karan sigari ɗaya,zaro ido nayi ina jira inga me zatayi dashi,
Ban gama mamaki ba kawai sai gani nayi ta kyasta mai wani ɗan abu karamin mai dizai wanda wuta ya fito daga cikin shi,
Sakawa tayi a baki ta mishi kyakkyawan riƙo tana zuka a hankali tare da busa hayaƙin ta baki da hanci,
Ummita ce ta shigo ɗakin,kallon ta tayi, sai dai babu wani alama na mamaki data nuna dan ganin tana shan taɓa,sai ma cewa da tayi,
"Biba yau akwai fita ne?
Kafin ta bata amsa ne wayar dake hannun ta ya shiga ƙara,sai dai bata ɗauka ba sai ma kallon Ummita da tayi" Muna da baƙi anjima,ki tabbatar kin kira Sara tazo ta gyara gidan nan dan yayi kura,ki kuma kimtsa kanki"
Gyada kai tana kallon wayar Biyu da ake ma three miss call,amma bata ɗauka ba"to Biba,bara to naje na fara gyara jiki na"
Bata bata amsa ba sai ɗaukar wayar ta da tayi,wanda tana karawa a kunne naji ta ɗayan gefen ana faɗin "haba Biba ai har kin tayarmin da hankali"
Shiru tayi taki magana sai zukan sigarin da take yi tana busar da iska
"Biba kin dawo lafiya ya aikin,da fatan an samu nasara"
"A ko wani lokaci nasara tana tare da Biba,"
Dariya yayi yana sauke ajiyar zuciya domin ba karamin daɗi yaji ba dajin wannan sanyayar muryar nata,"tabbas maganar ki haka take Biba,to yanzun yaushe zamu zo mu karɓi kayan"
"Ƙarfe goma na dare a gida na"tana gama fadar haka ta kashe wayar,
A nashi ɓangaren kuwa,rungume wayar yayi yana wani lumshe ido,Allah ya gani yana matukar kaunar Biba,duk da yasan yanada ya'ya waɗanda suka girma mata,yana da mata har biyu,kyawawa ga ilimi,
Sai dai kyan Biba na musamman ne,bai damu da Karuwancin da take yi ba,ko kuma wasu harkallolin da take gudanarwa,ko shaye-shayen da take yi,shi dai in har zata amince ta aure shi wallahi yana iya rabuwa da matan shi domin ita,yana iya mallaka mata duk abinda ya mallaka,
Sai dai kash,Biba ba su bane a gabanta,eh dole yace basu bane,domin shi kan shi da yake Minista yasan bashi kaɗai ne ke wannan haukar ba a kanta,
Ita mutum ce wacce baka gane asalen ne burin ta a rayuwa,dan haka take da wuyar fahimta,
A jiyar zuciya ya sauke yana daga wayar shi domin kiran sauran abonkan harkallolin su domin sanar dasu yau zasu haɗu da Biba a gidan ta......
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*05*
Sai da ta ƙarasa zuke sigarin da ke hannun ta sannan ta tashi ta shiga banɗaki,
Ruwan wanka ta tara tafashesshe a bahon wankan sai tururi yake,
Wani loka dake cikin bayin ta buɗe ta dauko wasu goruna sun kai kala biyar sai wasu robobi guda uku,
Wani irin sinadari ne a cikin waɗannan goruna wanda suke ruwa-ruwa,ko wanne sai da ta tsiyaya a cikin wannan ruwan,sanna ta buɗe robobin wanda gayayyaki ne kala kala a ciki,shi ma zubawa tayi,sai roban ƙarshe wanda ta dauko wani busasshen jan ganyen fulawa guda biyu ta wurga a cikin ruwan wanda nan take fulawan ya narke ruwan kuma ya koma wani irin ja mai fitar da wani irin sihirtaccen kamshi mai shiga fata,
Fita tayi daga bayin ta jawo kofar,
Kayan jikinta ta cire tas ya rage daga ita sai bireziya da pant,ta dauki wani mai a karamin gora ta shefe gaba ɗaya jikinta dashi,
Sannan ta dauki wani karamin kafet ta shimfida a zauna,gyaran kumban ƙafarta ta fara yi cikin kulawa,tana shafa masu wani dan mai a kwalba wanda sai da ta kusa minti talatin kafin ta kammala sannan ta koma banɗaki dan tuni ruwan ya huce ya kasance dumi kawai yake dashi,duk wasu tsumin kamshi data saka mashi ya gama jika,dan haka karasa cire ragowar kayan da ke jikinta tayi ta shige cikin ruwan tana nitsewa gaba ɗaya har kanta,
Ta jima sosai a bayin kafin ta fito ta shirya cikin wasu doguwar riga fara tas mara nauyi,rigar zan iya cewa ita da babu duk daya gomin kuwa rigar ta sauka har ƙasa,kuma dogon hannu gareshi,sai dai shara_shara ce yanda kasan lariya,sai dai wani dan yadi mai dan kauri wanda ya rufe daga rabin kirji zuwa haƙarƙari,amma cibiya a waje take,sai kuma daga ƙasan mara zuwa ƙasan duwawu suma a rufe suke da wannan yadin mai dan ƙauri,amma daga cinyarta har kasa ana iya gani,
Zama tayi kan kushin tana kallon tashoshin waƙoƙin turawa hankalin ta kwance,dan lokacin ma ƙarfe takwas ta wuce,
Ji tayi ana ta faman ƙwanƙwasa ƙofa,amma ko kallon wurin ba tayi ba,
Ummita ce ta fito daki da sauri ta zo ta buɗe ƙofar tana tambayar waye,
Ba tare daya kula ta ba ya shigo cikin falon yana kalle kalle,hango ta da yayi a hakimce saman kushin ne yasa da sauri ya karasa in da take zaune,
A kasa ya zauna ya kwashi ƙafafunta ya daura saman cinyarshi yana dan mammatsawa a hankali tare da shafawa,sannan cikin marairaice murya kamar zaiyi kuka yace"Biba ina kika tafi kika barni,kin saka na koma tamkar mahaukaci a garin Abuja ina nimanki,amma kin dawo ko ki nime ni"ya karasa fada yana sumbatar tafin ƙafarta,
Bata bashi amsa ba kamar yanda bata hana shi shafar ƙafarta ba,
"Biba na yi kewar ki tamkar rayuwa," Matashin saurayin ya faɗa yana tasowa tare da kara tsugunnawa sosai a gabanta yana shakar wani ni'imtaccen kamshi wanda yake ƙara tashi daga jikin ta,
Tana kallon shi ya matso da kanshi a hankali ya sumbaci lebbanta,
Nan ma bata hanashi ba,
Lumshe ido yayi yana sauke wani nauyayyen ajiyar zuciya,ƙara sumbatar bakinta yayi a karo na biyu yana daura hannun shi a saman kirjinta ya shafa,
Hannun shi ta cire daga kan kirjinta sannan ta kauda kanta daga kumbatar da yake mata,
Kamar mahaukaci haka yake ƙoƙarin hawa jikin ta,dan wannan kamshin da yake shaka ji yake kamar zai zauce,
Dakatar dashi tayi"ya isa haka Habib,ka tafi gida gobe zamu yi magana "
Girgiza kai ya shiga yi"dan Allah,dan Allah Biba ki taimaka min,wallahi a matse nake,mayi kewar ki Biba ki taimaki rayuwa ko da romancing dinki ne ki bari nayi,nayi alƙawarin kome kike so zan baki,na maki aikawari "
Mikewa tayi tsaye"kayi abinda nace ko kuma kai da ganina sai nan da sati ɗaya"
Da sauri ya juya ya bar gidan domin yasan tabbas zata iya aikata abinda tace,
Habib ɗa ne ga wani Senator,iyayen shi masu kuɗi ne sosai,shi kuma yana aiki ne a Central Bank,ba karamin kuɗi yake dashi ba,
Sun haɗu da Biba ne a wurin wani party a club,ranar tayi shaya_shayen abinda yafi karfin kanta,shine ta bishi gidan shi suka kwana a can,tun daga lokacin yake haukan binta yana mata barin kudi sai dai ko akai bata kawo shi,wani lokaci ne ma in yaci sa'a takan ɗan kula shi,
Ɗakinta ta shiga bata tsaya ko ina ba sai durowan dazu data buɗe wannan karon wani sacet din magani naga ta ciro,
Daya ta balla ta zauna tana tattaunawa kafin ta kora da ruwa,
Ko minti biyar ba ayi ba ta fara jin kanta na juyawa sakamakon kwayar data ci,
Wani Albom naga ta jawo a ƙarƙashin gado irin wanda ake saka hotuna a ciki,
Buɗe shafin farko tayi,wanda naga tana shafawa hawaye ya fara saukowa daga cikin idanun ta,
Taba ta kuma kunnawa,yayin da ta tsayar da idonta a kan hoton wanda bana iya ganin ko fuskar waye,
Ta ɗauki lokaci mai tsayi a haka kafin Ummita ta shigo "Biba sun iso tun dazu ke suke jira,
Wurge ta kuma yi da Albom din kasan gado kafin tasa hannu ta share hawayen idonta,ta ɗauki wayar ta da hannu daya hannu ɗayan kuma na riƙe da karan sigari ta doshi wani karamin hanyar dake cikin falon ta wanda ya sadata da wani madaidaicin falo hadadde in da wasu Dattijai ke zaune su huɗu suna kiranta,
Kallo daya zaka masu ka shaida cewa kuɗi sun zauna tare da hutu.
Daya daga cikin su yana dariya ya tashi ya rungume ta a jikin shi "na san zaki iya Biba, shi yasa nace ba wanda ya dace da wannan aikin sama dake Biba"
Ita ma dariya tayi tana zama a kan kafar shi bayan ya jata sun zauna saman kushin,
Shafa gemun shi tayi"kai dai faɗi gaskiya kawai dai kasan babu wanda zai iya irin wannan kasadar sai Biba shi yasa dole dai aka nime ta"
Amsar karan sigarin dake hannun ta yayi ya ajiye a saman wani karamin plate yana shafa bayanta tare da shinshinar hannunta zuwa dokin wuyar ta,
Daya daga cikin su ne wanda zuwan shi wurin na biyu kenan ya ce"Haba Alhaji Mansur,wani irin zubar da girma ne haka,wannan ai tayi sa'ar yar cikin ka,ni gaskiya bana son haka,
Kawai ta bamu abinda zata bamu mu ce"yana faɗa yana kallon inda Alhaji Abubakar ke zaune yana ta faman dariya suna zolayar Ummita wacce ita ma ke saman jikin shi dare_dare,shida Alhaji Rabi'u,
Ko wacce wani kofa naga ta buɗe ta shiga wanda daga dukkan alamu nanne ɗakinta,
Zama tayi a bakin gado tana sauke ajiyar zuciya,
Rinbon ɗin dake kanta ta cire tana ba suman kanta damar zubowa har gadon bayan ta,
Ɗayan wayar ta ciro daga cikin jakkan tana saka Sim card din data cire a bayan wayar ta kunna,kafin ta gama kawowa ne naga ta jawo dirowar dake gefen gado ta ciro wani kwali wanda ban gane me a ciki ba sai lokacin dana ga ta zaro karan sigari ɗaya,zaro ido nayi ina jira inga me zatayi dashi,
Ban gama mamaki ba kawai sai gani nayi ta kyasta mai wani ɗan abu karamin mai dizai wanda wuta ya fito daga cikin shi,
Sakawa tayi a baki ta mishi kyakkyawan riƙo tana zuka a hankali tare da busa hayaƙin ta baki da hanci,
Ummita ce ta shigo ɗakin,kallon ta tayi, sai dai babu wani alama na mamaki data nuna dan ganin tana shan taɓa,sai ma cewa da tayi,
"Biba yau akwai fita ne?
Kafin ta bata amsa ne wayar dake hannun ta ya shiga ƙara,sai dai bata ɗauka ba sai ma kallon Ummita da tayi" Muna da baƙi anjima,ki tabbatar kin kira Sara tazo ta gyara gidan nan dan yayi kura,ki kuma kimtsa kanki"
Gyada kai tana kallon wayar Biyu da ake ma three miss call,amma bata ɗauka ba"to Biba,bara to naje na fara gyara jiki na"
Bata bata amsa ba sai ɗaukar wayar ta da tayi,wanda tana karawa a kunne naji ta ɗayan gefen ana faɗin "haba Biba ai har kin tayarmin da hankali"
Shiru tayi taki magana sai zukan sigarin da take yi tana busar da iska
"Biba kin dawo lafiya ya aikin,da fatan an samu nasara"
"A ko wani lokaci nasara tana tare da Biba,"
Dariya yayi yana sauke ajiyar zuciya domin ba karamin daɗi yaji ba dajin wannan sanyayar muryar nata,"tabbas maganar ki haka take Biba,to yanzun yaushe zamu zo mu karɓi kayan"
"Ƙarfe goma na dare a gida na"tana gama fadar haka ta kashe wayar,
A nashi ɓangaren kuwa,rungume wayar yayi yana wani lumshe ido,Allah ya gani yana matukar kaunar Biba,duk da yasan yanada ya'ya waɗanda suka girma mata,yana da mata har biyu,kyawawa ga ilimi,
Sai dai kyan Biba na musamman ne,bai damu da Karuwancin da take yi ba,ko kuma wasu harkallolin da take gudanarwa,ko shaye-shayen da take yi,shi dai in har zata amince ta aure shi wallahi yana iya rabuwa da matan shi domin ita,yana iya mallaka mata duk abinda ya mallaka,
Sai dai kash,Biba ba su bane a gabanta,eh dole yace basu bane,domin shi kan shi da yake Minista yasan bashi kaɗai ne ke wannan haukar ba a kanta,
Ita mutum ce wacce baka gane asalen ne burin ta a rayuwa,dan haka take da wuyar fahimta,
A jiyar zuciya ya sauke yana daga wayar shi domin kiran sauran abonkan harkallolin su domin sanar dasu yau zasu haɗu da Biba a gidan ta......
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*05*
Sai da ta ƙarasa zuke sigarin da ke hannun ta sannan ta tashi ta shiga banɗaki,
Ruwan wanka ta tara tafashesshe a bahon wankan sai tururi yake,
Wani loka dake cikin bayin ta buɗe ta dauko wasu goruna sun kai kala biyar sai wasu robobi guda uku,
Wani irin sinadari ne a cikin waɗannan goruna wanda suke ruwa-ruwa,ko wanne sai da ta tsiyaya a cikin wannan ruwan,sanna ta buɗe robobin wanda gayayyaki ne kala kala a ciki,shi ma zubawa tayi,sai roban ƙarshe wanda ta dauko wani busasshen jan ganyen fulawa guda biyu ta wurga a cikin ruwan wanda nan take fulawan ya narke ruwan kuma ya koma wani irin ja mai fitar da wani irin sihirtaccen kamshi mai shiga fata,
Fita tayi daga bayin ta jawo kofar,
Kayan jikinta ta cire tas ya rage daga ita sai bireziya da pant,ta dauki wani mai a karamin gora ta shefe gaba ɗaya jikinta dashi,
Sannan ta dauki wani karamin kafet ta shimfida a zauna,gyaran kumban ƙafarta ta fara yi cikin kulawa,tana shafa masu wani dan mai a kwalba wanda sai da ta kusa minti talatin kafin ta kammala sannan ta koma banɗaki dan tuni ruwan ya huce ya kasance dumi kawai yake dashi,duk wasu tsumin kamshi data saka mashi ya gama jika,dan haka karasa cire ragowar kayan da ke jikinta tayi ta shige cikin ruwan tana nitsewa gaba ɗaya har kanta,
Ta jima sosai a bayin kafin ta fito ta shirya cikin wasu doguwar riga fara tas mara nauyi,rigar zan iya cewa ita da babu duk daya gomin kuwa rigar ta sauka har ƙasa,kuma dogon hannu gareshi,sai dai shara_shara ce yanda kasan lariya,sai dai wani dan yadi mai dan kauri wanda ya rufe daga rabin kirji zuwa haƙarƙari,amma cibiya a waje take,sai kuma daga ƙasan mara zuwa ƙasan duwawu suma a rufe suke da wannan yadin mai dan ƙauri,amma daga cinyarta har kasa ana iya gani,
Zama tayi kan kushin tana kallon tashoshin waƙoƙin turawa hankalin ta kwance,dan lokacin ma ƙarfe takwas ta wuce,
Ji tayi ana ta faman ƙwanƙwasa ƙofa,amma ko kallon wurin ba tayi ba,
Ummita ce ta fito daki da sauri ta zo ta buɗe ƙofar tana tambayar waye,
Ba tare daya kula ta ba ya shigo cikin falon yana kalle kalle,hango ta da yayi a hakimce saman kushin ne yasa da sauri ya karasa in da take zaune,
A kasa ya zauna ya kwashi ƙafafunta ya daura saman cinyarshi yana dan mammatsawa a hankali tare da shafawa,sannan cikin marairaice murya kamar zaiyi kuka yace"Biba ina kika tafi kika barni,kin saka na koma tamkar mahaukaci a garin Abuja ina nimanki,amma kin dawo ko ki nime ni"ya karasa fada yana sumbatar tafin ƙafarta,
Bata bashi amsa ba kamar yanda bata hana shi shafar ƙafarta ba,
"Biba na yi kewar ki tamkar rayuwa," Matashin saurayin ya faɗa yana tasowa tare da kara tsugunnawa sosai a gabanta yana shakar wani ni'imtaccen kamshi wanda yake ƙara tashi daga jikin ta,
Tana kallon shi ya matso da kanshi a hankali ya sumbaci lebbanta,
Nan ma bata hanashi ba,
Lumshe ido yayi yana sauke wani nauyayyen ajiyar zuciya,ƙara sumbatar bakinta yayi a karo na biyu yana daura hannun shi a saman kirjinta ya shafa,
Hannun shi ta cire daga kan kirjinta sannan ta kauda kanta daga kumbatar da yake mata,
Kamar mahaukaci haka yake ƙoƙarin hawa jikin ta,dan wannan kamshin da yake shaka ji yake kamar zai zauce,
Dakatar dashi tayi"ya isa haka Habib,ka tafi gida gobe zamu yi magana "
Girgiza kai ya shiga yi"dan Allah,dan Allah Biba ki taimaka min,wallahi a matse nake,mayi kewar ki Biba ki taimaki rayuwa ko da romancing dinki ne ki bari nayi,nayi alƙawarin kome kike so zan baki,na maki aikawari "
Mikewa tayi tsaye"kayi abinda nace ko kuma kai da ganina sai nan da sati ɗaya"
Da sauri ya juya ya bar gidan domin yasan tabbas zata iya aikata abinda tace,
Habib ɗa ne ga wani Senator,iyayen shi masu kuɗi ne sosai,shi kuma yana aiki ne a Central Bank,ba karamin kuɗi yake dashi ba,
Sun haɗu da Biba ne a wurin wani party a club,ranar tayi shaya_shayen abinda yafi karfin kanta,shine ta bishi gidan shi suka kwana a can,tun daga lokacin yake haukan binta yana mata barin kudi sai dai ko akai bata kawo shi,wani lokaci ne ma in yaci sa'a takan ɗan kula shi,
Ɗakinta ta shiga bata tsaya ko ina ba sai durowan dazu data buɗe wannan karon wani sacet din magani naga ta ciro,
Daya ta balla ta zauna tana tattaunawa kafin ta kora da ruwa,
Ko minti biyar ba ayi ba ta fara jin kanta na juyawa sakamakon kwayar data ci,
Wani Albom naga ta jawo a ƙarƙashin gado irin wanda ake saka hotuna a ciki,
Buɗe shafin farko tayi,wanda naga tana shafawa hawaye ya fara saukowa daga cikin idanun ta,
Taba ta kuma kunnawa,yayin da ta tsayar da idonta a kan hoton wanda bana iya ganin ko fuskar waye,
Ta ɗauki lokaci mai tsayi a haka kafin Ummita ta shigo "Biba sun iso tun dazu ke suke jira,
Wurge ta kuma yi da Albom din kasan gado kafin tasa hannu ta share hawayen idonta,ta ɗauki wayar ta da hannu daya hannu ɗayan kuma na riƙe da karan sigari ta doshi wani karamin hanyar dake cikin falon ta wanda ya sadata da wani madaidaicin falo hadadde in da wasu Dattijai ke zaune su huɗu suna kiranta,
Kallo daya zaka masu ka shaida cewa kuɗi sun zauna tare da hutu.
Daya daga cikin su yana dariya ya tashi ya rungume ta a jikin shi "na san zaki iya Biba, shi yasa nace ba wanda ya dace da wannan aikin sama dake Biba"
Ita ma dariya tayi tana zama a kan kafar shi bayan ya jata sun zauna saman kushin,
Shafa gemun shi tayi"kai dai faɗi gaskiya kawai dai kasan babu wanda zai iya irin wannan kasadar sai Biba shi yasa dole dai aka nime ta"
Amsar karan sigarin dake hannun ta yayi ya ajiye a saman wani karamin plate yana shafa bayanta tare da shinshinar hannunta zuwa dokin wuyar ta,
Daya daga cikin su ne wanda zuwan shi wurin na biyu kenan ya ce"Haba Alhaji Mansur,wani irin zubar da girma ne haka,wannan ai tayi sa'ar yar cikin ka,ni gaskiya bana son haka,
Kawai ta bamu abinda zata bamu mu ce"yana faɗa yana kallon inda Alhaji Abubakar ke zaune yana ta faman dariya suna zolayar Ummita wacce ita ma ke saman jikin shi dare_dare,shida Alhaji Rabi'u,