Sashe 43
Yar Tsanar Zinari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Girgiza kai Kaka keyi kawai,
Da sauri ya karaso inda take" dan Allah Mama kiyi haƙuri,Nasan abinda ta faɗa bai kamata ba,in sha Allah hakan ba zai ƙara faruwa ba"
"Me yasa zaka Mari uwa a gaban ya'yanta,so kake yayanka su tsana ka?wannan ba abu mai kyau bane ta aikata,sai ka bari idan kun keɓe ja mata duk abinda kaga dama amma banda duka banda Mari,domin wannan baya daya daga cikin halin kwarai,na tabbatar da idan ma da kyale ta ka yi da tana gama faɗa wucewa zata yi"
"Mama kiyi haƙuri zan dinga kiyayewa,"
"Dan Allah ku bari a gama da wanga jarabawar da ya same mu"
Komawa yayi ta zauna,
Hajiya Rahama ce ita ma ta mike "to kowa dai ya dibo da zafi bakin shi,dan haka nayi gaba" Tashi yayi ita ma ta yi wucewar ta,
Kallon Kaka ta yi,cikin kwana daya gabadaya ta zabge ta yi rama,
"Kiyi haƙuri Ammi sannan ki rage damuwa a zuciyar ki,karki bari wani ciyo ya kamaki,addu'a ita ce mafita"
Dan murmushi yake ta saki,domin ita ba mahaukaciya ɓace"In sha Allah kaka "
Nurudeen ne yace"yanzun haka na bada aikin saukar Kur'anai makarantun goma,har zuwa sanda lamarin zai yi sanyi"
"Na gode Nurudeen Allah ya maka Albarka"cewar kaka,
" Karki damu kaka,ai Suraj ai ɗan uwa na ne "
Karan Wayar Abba ne ya dakatar dasu"yauwa gashi ma sun kuma kira Allah yasa an dace sun samu shiga "
Duk da Amin suka amsa,
Gyara zama tayi,domin Allah ya gani ita kanta ta matsu ta ji halin da ake ciki.....
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*43*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*
Ɗaukar kiran yayi ya saka a amsa kuwa kamar dazu,
Bayan amsa sallamah ne yace"Ya ake ciki Sufyan ?
"Gabaɗaya wannan lamarin ya wuce da tunanin mu,domin yaron ya iso shine yake faɗa mana ai in dai a nan garin ne ba za mu taɓa samun lauyan da zai ɗauki case ɗin nan ba,domin gabaɗaya goyon bayan mutumin nan suke yi,idan kuma har wani loya musulmi yace zai karɓa ƙoƙarin koranshi suke yi daga aiki,yanzun haka shima a saboda kawai yace zai amsa wannan Case din an yi Seizing License din shi na Loya,
Yanzun gashi har karfe goma amma wallahi mutanen nan yanda kasan basu san da mu ba"
Inna'lillahi wa'inna ilaihi rajiun,shine kawai abinda suke ta maimaitawa,
"Insha Allah zamu dai ci gaba da jarabawa ko za'a dace,ku kwantar da hankalin ku,sai dai zuwa anjima duk yanda ake ciki zaku jimu"
"To shikenan"daganan sallamah suka kuma yi,
Nasiha sosai Kaka da Abba suka ma Ammi ciki harda ita sannan aka sallame su akan duk yanda ake ciki anjima za su ji,
Suna fitowa tana biye da Ammi a baya,har sun kusa isa falo tace" Ammi ina son zanje can gidan na kwaso kaya"
"Kisa Direba ya kaiki,sannan ki zauna a can dan zaman ki a nan baida wani amfani,ƙila zaman ki a can zai iya taimaka maki"tana karasa faɗa tana shigewa falon,
Me kuma take nufi da zaman ta anan bai da wani amfani,
Dan shiru tayi,to kuma gaskiya ta faɗa fa,duk da ta san abin zai yi kamar bai dame ta bane idan ta koma,amma komawar shi yafi,dan haka ba tare data shiga ciki ba ta juya ta nufi wurin ajiye motoci dan ta san anan zata samu mai kaita gida,
Tana zuwa kuwa daya daga cikin direbobin gidan ne ya kai ta har gida sannan ya dawo,
Bala ne da sauran ma'aikatan gidan suka shiga jajanta mata,tana amsawa ta shige falo,
Yau dinnan ba zata zauna ba duk wani daki na gidan nan sai ta tabbatar data bincika shi,
Anan falo ta ajiye Hijabin ta,kai tsaye dakin shi ta shiga ta fara dubawa lungu da saƙo,har ta gado,da dorowar kayan shi sai da ta matsar a tunanin ko zata samu wani ɓoyayyen daki ko ma'adana,sai dai ko fallan takarda bata samu ba a ɗakin,
Ba lallai bane ta iya maida dakin yanda yake sai dai kawai tayi iya yin ta tabar saura in ya dawo ya kyara abin shi,ƙila ma lokacin ta daɗe da barin gidan,
Ɗayan dakin dake gefen na kasa taje buɗewa,sai dai kamar daga ta ciki aka kulle dan taki buduwa,
Ta kwada yin amfani da dan karamin ƙarfe dan kwada ko zai bude amma sai da ya dauke ta kusan awa daya kafin ta iya buɗewa dan ma taki hakura,a cewar ta sai taga me a ciki,
Lafiyayyen daki ne,sai dai shima kamar wancan an rufe komai na dakin da farin kyalle wanda hakan ke nuna an jima sosai ba'a yi amfani da dakin ba,
Gabaɗaya ta yaye kyallayen tana kare ma ɗakin kallo,daga dukkan alamu dakin mace ce,
Durowar kayan ta bude nan ma kayane amma kuma na tsofaffi ne,sai dai kayan yawanci dogayen riguna ne,harda su sarƙoƙi masu matukar tsada,mai da su tayi inda ta dauki su,tana kokarin rufe wurin ne wani karamin fefa ta fado daga ƙasan akwatin sarƙoƙin,
Ɗauka tayi ta buɗe ta warware,
*Wudil,sabon layi,house no 120,Ilyasu Shehu*
Abinda ke rubuce kenan a cikin ɗan ƙaramin takardar kenan,
Ba tare da tunanin komai ba ta ɗauke takardar,ta bar ɗakin,
*Bayan Kwana biyu*
Abubuwa marasa daɗi ne kekan faruwa game da wannan lamarin,domin maganar so yake yafi karfin tunanin su,duk inda suke tunani za su samu lauya abin ya faskara,domin ko da sun samu da zaran ya amsa da kanshi zai dawo yace ya fasa abin yafi karfin shi,
Su kuma su Abbu har yanzun an hana su ganinshi,sun rasa yanda zasu yi,domin mutumin ba karamin mugun mutumi bene,duk kuma wanda ya amsa aiki kashedi ake masa da rayuwar sa ko data ahalin shi,dole ya ajiye aikin,
Sun ce kuma a cikin kwana na biyar zasu kai shi kotu a yanke mai hukunci tunda sun kasa samun Loya,
Su kansu kungiyar malamai sun so a dawo da case din Arewa,sai dai sam uban yarinyar yaki yarda dan haka addu'a kawai suke mashi,
Duk waɗannan labaran tana samu ne daga bakin Kaka idan kullun taje gaishe ta,
A wana na biyun ne kuma suka samu baki daga South African,Kanin Kaka ne tare da yaran shi uku,Babban dan shi,wanda yake wani gabjeje a kalla zai yi shekara Arba'in da biyar,sai mai bi mashi,sai kuma ƙanwar su mai ishirin da shida,
Shi kuma uban ya dan fara manyanta amma yanda kasan yaro haka yake,domin a tsuke yake cikin Kananan kaya,irin mutanin nan ne waɗanda daka gansu kasan budurwar zuciya ce dasu,
Ta gama shiri kenan tana ƙoƙarin fita sai ga Bala ya shigo da sauri har suna shirin cin karo,"kai lafiya?
"Hajiya baƙi aka yi"
Karamin tsaki taja "daga ina"
"Kanin kakar Ubangida mu ne,kuma yazo ne tare da nashi ƴaƴan"
Shiru ne ya ratsa falon na wani dan lokaci kafin tace"dama idan sun zo anan suke sauka?
"Eh to sau daya dai na taba ganin yazo nan kuma shi kadai yazo a wancan lokacin,dan a sannan Kakar Ubangida tana nan"
Falon take kare ma kallo,"yanzun ta ina zata sauke su,ita bata cika son tana zama wuri ɗaya da mutanen da bata sani ba gaka,
Ajiyar zuciya ta sauke,"da fita zan yi amma mu je "
Tare suka fito daga cikin falon ta nufi inda suke cikin takun ta nan mai jan hankali wanda ya riga ya bi mata jiki tun da jimawa ba tare ma data San tana yi ba ko a gaban waye,
Su din ma nufarta suke yi sai dai ganin ta kusa karasowa ne yasa suka dakata suna jiran isowar ta,
Tunda ta daura idanun ta a kansu zuciyar ta ke tsinkewa,domin bata yi tunanin ganin su a haka ba,manya zarata dasu har uban,sai dai shi kalar shi kamar ba Bature ba,yafi kama da yan American,sabanin yayar shi data gani a hoto wacce take Baturiya sak,
Tana isowa ta sakar masu da murmushi mai sanyi tana karasa kusa da wanda take da tabbacin shine Baban su "Welcome to Nigeria Grandpa "
Murmushi mutumin shima ya sakar mata yana buɗe mata hannu Alamun zai rungumeta,
Ita ma da yake yar duniya ce sai ta rungumeta suka gaisa,sannan ta juyo wurin mazan suma dai irin gaisuwar da suka yi kenan kafin ta masu jagora zuwa cikin falon tana rike da hannun maccen,
Nuna masu wurin zama tayi tace suyi haƙuri a gyara masu wurin da zasu zauna,
Bala ta aika yayi masu ordering abinci,
Matashiyar budurwar ce tace mata"Daughter in low ni tare dake zan zauna"
"ba damuwa tashi mu je"cikin sakin fuska tana mika mata hannu,
Kama hannun ta tayi suka yi ɗakinta ta nuna mata banɗaki ta kuma cire mata sababbin kayan wanka,
Jakkan kayanta kuma ta saka mata a gefe,
Sai da Bala ya kowa abinci sannan ta fito daga dakin da tasa ana gyara masu,ta sanar dasu an kammala suna iya shiga kowa daki daya,idan sun kammala ga abincin su nan,
Godiya suka mata,
Baban su da taji suna kira da Pa ne yace idan sun huta zuwa anjima zata kaisu wurin Maman Suraj,
Tana fitowa dakin wayar Ammi ta nima dan gara ta faɗa mata da zuwan su akan ta ganta da baƙi babu sanarwa,
Yana ta kara ba'a ɗauka har tayi kira na biyu yana ma shirin tsinkewa taji an ɗauka,
Ƙoƙarin yin sallamah take yi taji ance"wai lafiya kike damun ta da ƙira da rana tsaka"
Sai da tayi dan jim kafin tace"idan Ammi na kusa ki ba ta waya"
"Bana jin zan iya bata,tukunna ma ke wacece da zaki aike ni"
Da sauri ya karaso inda take" dan Allah Mama kiyi haƙuri,Nasan abinda ta faɗa bai kamata ba,in sha Allah hakan ba zai ƙara faruwa ba"
"Me yasa zaka Mari uwa a gaban ya'yanta,so kake yayanka su tsana ka?wannan ba abu mai kyau bane ta aikata,sai ka bari idan kun keɓe ja mata duk abinda kaga dama amma banda duka banda Mari,domin wannan baya daya daga cikin halin kwarai,na tabbatar da idan ma da kyale ta ka yi da tana gama faɗa wucewa zata yi"
"Mama kiyi haƙuri zan dinga kiyayewa,"
"Dan Allah ku bari a gama da wanga jarabawar da ya same mu"
Komawa yayi ta zauna,
Hajiya Rahama ce ita ma ta mike "to kowa dai ya dibo da zafi bakin shi,dan haka nayi gaba" Tashi yayi ita ma ta yi wucewar ta,
Kallon Kaka ta yi,cikin kwana daya gabadaya ta zabge ta yi rama,
"Kiyi haƙuri Ammi sannan ki rage damuwa a zuciyar ki,karki bari wani ciyo ya kamaki,addu'a ita ce mafita"
Dan murmushi yake ta saki,domin ita ba mahaukaciya ɓace"In sha Allah kaka "
Nurudeen ne yace"yanzun haka na bada aikin saukar Kur'anai makarantun goma,har zuwa sanda lamarin zai yi sanyi"
"Na gode Nurudeen Allah ya maka Albarka"cewar kaka,
" Karki damu kaka,ai Suraj ai ɗan uwa na ne "
Karan Wayar Abba ne ya dakatar dasu"yauwa gashi ma sun kuma kira Allah yasa an dace sun samu shiga "
Duk da Amin suka amsa,
Gyara zama tayi,domin Allah ya gani ita kanta ta matsu ta ji halin da ake ciki.....
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*43*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*
Ɗaukar kiran yayi ya saka a amsa kuwa kamar dazu,
Bayan amsa sallamah ne yace"Ya ake ciki Sufyan ?
"Gabaɗaya wannan lamarin ya wuce da tunanin mu,domin yaron ya iso shine yake faɗa mana ai in dai a nan garin ne ba za mu taɓa samun lauyan da zai ɗauki case ɗin nan ba,domin gabaɗaya goyon bayan mutumin nan suke yi,idan kuma har wani loya musulmi yace zai karɓa ƙoƙarin koranshi suke yi daga aiki,yanzun haka shima a saboda kawai yace zai amsa wannan Case din an yi Seizing License din shi na Loya,
Yanzun gashi har karfe goma amma wallahi mutanen nan yanda kasan basu san da mu ba"
Inna'lillahi wa'inna ilaihi rajiun,shine kawai abinda suke ta maimaitawa,
"Insha Allah zamu dai ci gaba da jarabawa ko za'a dace,ku kwantar da hankalin ku,sai dai zuwa anjima duk yanda ake ciki zaku jimu"
"To shikenan"daganan sallamah suka kuma yi,
Nasiha sosai Kaka da Abba suka ma Ammi ciki harda ita sannan aka sallame su akan duk yanda ake ciki anjima za su ji,
Suna fitowa tana biye da Ammi a baya,har sun kusa isa falo tace" Ammi ina son zanje can gidan na kwaso kaya"
"Kisa Direba ya kaiki,sannan ki zauna a can dan zaman ki a nan baida wani amfani,ƙila zaman ki a can zai iya taimaka maki"tana karasa faɗa tana shigewa falon,
Me kuma take nufi da zaman ta anan bai da wani amfani,
Dan shiru tayi,to kuma gaskiya ta faɗa fa,duk da ta san abin zai yi kamar bai dame ta bane idan ta koma,amma komawar shi yafi,dan haka ba tare data shiga ciki ba ta juya ta nufi wurin ajiye motoci dan ta san anan zata samu mai kaita gida,
Tana zuwa kuwa daya daga cikin direbobin gidan ne ya kai ta har gida sannan ya dawo,
Bala ne da sauran ma'aikatan gidan suka shiga jajanta mata,tana amsawa ta shige falo,
Yau dinnan ba zata zauna ba duk wani daki na gidan nan sai ta tabbatar data bincika shi,
Anan falo ta ajiye Hijabin ta,kai tsaye dakin shi ta shiga ta fara dubawa lungu da saƙo,har ta gado,da dorowar kayan shi sai da ta matsar a tunanin ko zata samu wani ɓoyayyen daki ko ma'adana,sai dai ko fallan takarda bata samu ba a ɗakin,
Ba lallai bane ta iya maida dakin yanda yake sai dai kawai tayi iya yin ta tabar saura in ya dawo ya kyara abin shi,ƙila ma lokacin ta daɗe da barin gidan,
Ɗayan dakin dake gefen na kasa taje buɗewa,sai dai kamar daga ta ciki aka kulle dan taki buduwa,
Ta kwada yin amfani da dan karamin ƙarfe dan kwada ko zai bude amma sai da ya dauke ta kusan awa daya kafin ta iya buɗewa dan ma taki hakura,a cewar ta sai taga me a ciki,
Lafiyayyen daki ne,sai dai shima kamar wancan an rufe komai na dakin da farin kyalle wanda hakan ke nuna an jima sosai ba'a yi amfani da dakin ba,
Gabaɗaya ta yaye kyallayen tana kare ma ɗakin kallo,daga dukkan alamu dakin mace ce,
Durowar kayan ta bude nan ma kayane amma kuma na tsofaffi ne,sai dai kayan yawanci dogayen riguna ne,harda su sarƙoƙi masu matukar tsada,mai da su tayi inda ta dauki su,tana kokarin rufe wurin ne wani karamin fefa ta fado daga ƙasan akwatin sarƙoƙin,
Ɗauka tayi ta buɗe ta warware,
*Wudil,sabon layi,house no 120,Ilyasu Shehu*
Abinda ke rubuce kenan a cikin ɗan ƙaramin takardar kenan,
Ba tare da tunanin komai ba ta ɗauke takardar,ta bar ɗakin,
*Bayan Kwana biyu*
Abubuwa marasa daɗi ne kekan faruwa game da wannan lamarin,domin maganar so yake yafi karfin tunanin su,duk inda suke tunani za su samu lauya abin ya faskara,domin ko da sun samu da zaran ya amsa da kanshi zai dawo yace ya fasa abin yafi karfin shi,
Su kuma su Abbu har yanzun an hana su ganinshi,sun rasa yanda zasu yi,domin mutumin ba karamin mugun mutumi bene,duk kuma wanda ya amsa aiki kashedi ake masa da rayuwar sa ko data ahalin shi,dole ya ajiye aikin,
Sun ce kuma a cikin kwana na biyar zasu kai shi kotu a yanke mai hukunci tunda sun kasa samun Loya,
Su kansu kungiyar malamai sun so a dawo da case din Arewa,sai dai sam uban yarinyar yaki yarda dan haka addu'a kawai suke mashi,
Duk waɗannan labaran tana samu ne daga bakin Kaka idan kullun taje gaishe ta,
A wana na biyun ne kuma suka samu baki daga South African,Kanin Kaka ne tare da yaran shi uku,Babban dan shi,wanda yake wani gabjeje a kalla zai yi shekara Arba'in da biyar,sai mai bi mashi,sai kuma ƙanwar su mai ishirin da shida,
Shi kuma uban ya dan fara manyanta amma yanda kasan yaro haka yake,domin a tsuke yake cikin Kananan kaya,irin mutanin nan ne waɗanda daka gansu kasan budurwar zuciya ce dasu,
Ta gama shiri kenan tana ƙoƙarin fita sai ga Bala ya shigo da sauri har suna shirin cin karo,"kai lafiya?
"Hajiya baƙi aka yi"
Karamin tsaki taja "daga ina"
"Kanin kakar Ubangida mu ne,kuma yazo ne tare da nashi ƴaƴan"
Shiru ne ya ratsa falon na wani dan lokaci kafin tace"dama idan sun zo anan suke sauka?
"Eh to sau daya dai na taba ganin yazo nan kuma shi kadai yazo a wancan lokacin,dan a sannan Kakar Ubangida tana nan"
Falon take kare ma kallo,"yanzun ta ina zata sauke su,ita bata cika son tana zama wuri ɗaya da mutanen da bata sani ba gaka,
Ajiyar zuciya ta sauke,"da fita zan yi amma mu je "
Tare suka fito daga cikin falon ta nufi inda suke cikin takun ta nan mai jan hankali wanda ya riga ya bi mata jiki tun da jimawa ba tare ma data San tana yi ba ko a gaban waye,
Su din ma nufarta suke yi sai dai ganin ta kusa karasowa ne yasa suka dakata suna jiran isowar ta,
Tunda ta daura idanun ta a kansu zuciyar ta ke tsinkewa,domin bata yi tunanin ganin su a haka ba,manya zarata dasu har uban,sai dai shi kalar shi kamar ba Bature ba,yafi kama da yan American,sabanin yayar shi data gani a hoto wacce take Baturiya sak,
Tana isowa ta sakar masu da murmushi mai sanyi tana karasa kusa da wanda take da tabbacin shine Baban su "Welcome to Nigeria Grandpa "
Murmushi mutumin shima ya sakar mata yana buɗe mata hannu Alamun zai rungumeta,
Ita ma da yake yar duniya ce sai ta rungumeta suka gaisa,sannan ta juyo wurin mazan suma dai irin gaisuwar da suka yi kenan kafin ta masu jagora zuwa cikin falon tana rike da hannun maccen,
Nuna masu wurin zama tayi tace suyi haƙuri a gyara masu wurin da zasu zauna,
Bala ta aika yayi masu ordering abinci,
Matashiyar budurwar ce tace mata"Daughter in low ni tare dake zan zauna"
"ba damuwa tashi mu je"cikin sakin fuska tana mika mata hannu,
Kama hannun ta tayi suka yi ɗakinta ta nuna mata banɗaki ta kuma cire mata sababbin kayan wanka,
Jakkan kayanta kuma ta saka mata a gefe,
Sai da Bala ya kowa abinci sannan ta fito daga dakin da tasa ana gyara masu,ta sanar dasu an kammala suna iya shiga kowa daki daya,idan sun kammala ga abincin su nan,
Godiya suka mata,
Baban su da taji suna kira da Pa ne yace idan sun huta zuwa anjima zata kaisu wurin Maman Suraj,
Tana fitowa dakin wayar Ammi ta nima dan gara ta faɗa mata da zuwan su akan ta ganta da baƙi babu sanarwa,
Yana ta kara ba'a ɗauka har tayi kira na biyu yana ma shirin tsinkewa taji an ɗauka,
Ƙoƙarin yin sallamah take yi taji ance"wai lafiya kike damun ta da ƙira da rana tsaka"
Sai da tayi dan jim kafin tace"idan Ammi na kusa ki ba ta waya"
"Bana jin zan iya bata,tukunna ma ke wacece da zaki aike ni"