Sashe 80
Yar Tsanar Zinari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wasu madaidaitan robobi ne masu kyau a ajiye a gabanta,
Nuna mata su ta shiga yi data bayan daya,
Wannan sabulun wanka ne,dashi zaki rinka yin wanka,wannan kuma man shafawa ne,sai wannan shi kuma zaki dinga cire kwaya daya kina sha ɗaya da safe daya da yamma,wannan kuma ki maida shi ruwan shanki,ba shida wani illa ko side effect,sai wannan turaren da shi kuma na tsugunnawa ne sai na jiki,a duk lokacin da zaki yi amfani dashi za'a kawo maki kaskon,dan Allah ki dage ki yi yanda nace,wanda baki gane ba zaki ga komai a rubuce "ta faɗa tana maida su cikin jakkan tare da mika mata,
Amsa tayi" Na gode sosai Ammi"
"Ki yi ƙoƙari ki shiga ki gaida Kaka"
"To" Ta fada tana tashi,
Daki ta kai kayan ta ajiye sannan ta ɗauki ƙaramin hijabi ta saka sannan ta fita,
A hankali take takawa dan ji take kamar iska zai dauke ta saboda rashin nauyin jiki,
Tana dab da shiga shi yana taji an riƙo mata hannu,
Zabura tayi tana dan matsawa baya kaɗan dan ta dan tsorata,
"Oh Sorry na baki tsoro "
Kallon shi take yi tare da kokarin janye hannun ta,sai dai yaƙi saki, "me haka Nurudeen sake min hannu"
Ajiyar zuciya ya sauke"Thank God baki manta suna na ba"
"Ka sake ni bana son haka,idan wani ya ganmu fa"
"Ai nafi son ma a ganmu kin ga sai a saka wannan hoton mijin naki ya sake ki ni kuma na aure ki"
Daga bayan su suka yi an ce"sakar mata hannu"
Duk juyawa suka yi,ganin wanda yayi maganar ne yasa da sauri ya sakar mata hannu,
Ba tare data ƙara kallon su ba ta saka kai ta shige,
Ita gabaɗaya daga shi Nurudeen din har Shamsuddeen,tun lokacin da shi Shamsuddeen din ya bada shaidar karya a gaban su kaka a kan ita da Suraj ta ji ya fita ranta,ɗan girman da take ganin shi dashi duk ta zube,
Da fara'a Kaka ta tare ta "Habiba ya jikin naki"
Zama tayi kusa da ita"na ji sauki Kaka sai kewar ki da nake yi"
Dariya tayi "ke dai faɗi gaskiya,ko dai kewar mijin ki kike yi"
Nan take ta bata fuska tana shirin yin magana kenan suka haɗa ido Maijiddarh dake zaune,
Nan take ta canja salo zuwa yanayin shagwaba "ban cin ya tafi ya barni da kewar shi,ni fushi nake dashi"
Dariya kaka ta saka"ke da ba kida lafiya ina zai dauke ki yai ta yawo dake"wayar ta dake gefe ne ya shiga ƙara,ɗauka tayi tana miƙa ma ta"dubamin wake kira,dan ban fito da Glass ba,
Ganin sunan me kira kaɗai sai da yasa zuciyar ta girgiza"Suraj ne"
"Yauwa dan Halak ke nan,to ɗauki wayar"
Girgiza kai tayi"A'a ai ke ya kira,ni kin ga ma bari naje amma anjima zan dawo "
Karɓa tayi tana karawa a kunne tana dariya,
Daga can ɓangaren yake tambayar "kaka dariyar me kike yi"
"Ni da matar ka mana,wai fushi take da kai"
Dan murmushi ta saki "me tace na mata?
" Ka kira ta ka tambaye ta"
Dariya yayi "ke dai na baki wannan damar ki lallasar min ita"
"Ja'iri ya jikin Nana A'isha"
"Da sauƙi,gata ku gaisa"ya faɗa yana karama Kakar shi wayar a kunne,
_________kwance take saman gado tana rusar kuka,tunda ta dawo shiyan kaka yanzun kusan mintuna talatin kenan tana abu daya,babu abinda yake kara tada mata hankali shine ganin yanda Biba ta zama jaruma akan idanun kowa,
Jin shigowar Momy bai sa ta tsagaita daga kukan da take yi ba,
Zama tayi a bakin gadon tana dagota "zauna muyi magana"
Kokarin komawa kwance take yi"ni dai ki kyale ni,babu wani maganar da zamu yi da ke"
Wannan karon cikin jin haushi ta ce"idan baki saurare ni ba ta yaya zamu samu mafita? Ƙara dagota zaune tayi,
"Yanzun shi Yusuf ya kuke ciki akan maganar shi?
Jan majina tayi tana sheshsheka"idan na kira wayar shi baya ɗauka,karshe ma sai turomin saƙo yayi cewar ni ba iri ajin shi bace,saboda ya lura ni ban waye ba ban San Me duniya ke ciki ba,"
"Tsinanne,shi har ya isa yace haka akanki,ki kyale shi shi yake da asara"
Kara fashewa tayi da kuka"ni yanzun shi kenan haka zan zauna ban yi aure ba,shi kenan nayi Two Zero,gashi Suraj yayi min nisa ko ganin shi bana samun damar yi,har Gara da,wallahi Momy kin cuce ni duk ke kika lalata komai "
Tama rasa me zata ce mata,wani shawara ya kamata ta bata wanda zuciyar ta zai yi sanyi,tun ba yanzun ba ta san cewar ta kwafsa da ya,sai dai bata son ta nuna gazawarta a gaban yar ta,"kin ga kiyi haƙuri bari zan kira Atika zamu samu mafita"a haka ta samu ta shawo kanta da kyar ta yi shiru.
*Bayan sati ɗaya*
A cikin kwanaki bakwai idan ka ga Biba kallo daya zaka mata ka shaida tabbas ta dawo haiyacinta,ta kuma koma asalin Biban ta,
Domin duk wani rama da kodewa da tayi sai da ta ciko,
Ammi kullun cikin bata haɗin danyen madara da na namar kaza take,gashi man da ta bata ya taimaka wurin goge mata fatar jiki,dan har wani tsantsi take yi,cikin turarukan da take sawa tayi har da gashi, ita karan kanta wani lokaci idan ta kalli kanta a madubi tana jinjina ma kayan tare da mamakin in da Ammi ta samo su,dan wani irin fitinannan kanshi ke fita a jinta wanda hatta fitsari idan tayi shi ji take a ciki,har mamaki matsewarta take yi,dan ko kaɗan yatsar ta bai iya wuce kofar wurin,ga wani irin ruwa sake fita,wani lokaci har tsoro abin ke bata yanda yake fita,ita karan kanta ta san ta samu canji da yawa a jikin ta,farin ta ya karu fiye da da,har wani kashe ido take da ƙyalli na musamman,lallai bata san da wani baki ya kamata ta gode ma Ammi ba,babu in da take zuwa sai gaida Kaka sai kuma zaman istigfari wanda a yanzun yawancin lokuta zaka ganta da ƙaramin charbi irin mai batir din nan tana dannawa.
Ammi ce ta buɗe ƙofar ta shigo "har yanzun baki kammala shiryawa ba,kin san saura yan mintuna jirginmu ya tashi"
Juyowa tayi fuskarta dauke da murmushi "na kammala Ammi yanzun takalmi kawai zan saka"
"To ki yi sauri dai dan ke kadai muke jira"ta ƙarasa faɗa tana fita,
"To"
Ita da Ammi ne kawai zasu tafi,dan Amira zata zauna ne a wurin Goggon yara,dan haka Shamsuddeen shi ya kai su har Airport bayan sunyi sallamah da su Kaka,
Ko lokacin da jirgi ke lulawa sararin samaniya lumshe ido tayi tana jero addu'a,kwata-kwata bana jin yin wannan tafiyar,ba dan komai ba sai don bata son haɗuwa dashi,ita da ma ace za'abi nata da Ammi ta barta anan idan har aka gama shari'ar sai su dawo su mai da ita gida,sam bata shirya tarbon wulakanci ba irin nashi,ta tabbatar idan har sun haɗu sai yayi abinda zai ɓata mata rai sannan hankalin shi yake kwanciya,
Ganin tunanin yana ƙoƙarin yi mata yawa ne yasa ta maida hankalin ta wurin jan charbin da take yi,daga haka har bacci ya kwashe ta,
Sai da jirgin su ya sauka sannan Ammi ta tayar da ita suka fito,wani irin sanyi ake yi mai matukar shiga jiki da ratsa kashi,Glass din dake cikin jakkanta ta ciro ta saka a idon ta,wanda ba karamin kyau da ƙara fito da ita yayi ba,dama gashi riga da Siket ne na Atamfa a jikin ta mai kalan ja,sai After dress data saka fara tas mai tsansi shara_shara mara nauyi,sai karamin jakka mai dogon tsarka wanda ake sakalawa a kafaɗa dan ƙarami wanda baici ya ɗauki waya biyu ba,sai ta fito yanda kasan ƴar tsanar zinari,
Ammi ce a gaba ita tana biye da ita a baya jaye da dan madaidaicin Aƙwati,
Sam bai lura da ita ba sai da ya rungume Ammi yana murmushin farin ciki "welcome Ammi"
"Thank you My Dear"
Cikin yanayin shagwaba wanda ba ta san ya iya ba ya shafa cikin shi"Ammi yunwa nake ji,nayi kewar girkin ki,"
"Nikam babu abinda zan kara girka maka tunda ga matarka nan ta maka"
Yana shirin kara yin magana ne idanun shi suka sauka akan ta,duk da akwai Glass mai duhu a idanun ta hakan bai hana shi ganin kwayar idanun ta data cire a kanshi tana ƙara kauda kai,
Gefen lips din shi ya dan ciza yana shafa kai tare da kara kallon ta daga sama har kasa cikin kallon nan nashi na gefen ido,
"Ni dai muge sanyi nake ji"
Maida hankali yayi kan Ammi yana rike hannun ta"muje to"
Tana biye dasu a baya har wurin parking mota inda ya buɗe ma Ammi gidan baya ta shiga,ya mai da kofar ya kulle,da makulli yayi amfani ya danna,nan take but din motar ya buɗe,saka akwatin tayi ta kulle sannan ta zagaya ta buɗe gidan baya kusa da Ammi ta zauna ba tare data kalli koda in da yake ba,tayi alkawarin har su bar garin ba zata taɓa shiga har Karshi ba,
Da kallon mamaki yake binta dashi a ran shi,wanda ko kaɗan bai nuna ba a fili,wato shi zata nuna ma miskilanci,ai kuwa sai ta san dame yi take yi,
Buɗe mazaunin direba yayi ya zauna,yana tayar da motar.......
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*81*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*
Nuna mata su ta shiga yi data bayan daya,
Wannan sabulun wanka ne,dashi zaki rinka yin wanka,wannan kuma man shafawa ne,sai wannan shi kuma zaki dinga cire kwaya daya kina sha ɗaya da safe daya da yamma,wannan kuma ki maida shi ruwan shanki,ba shida wani illa ko side effect,sai wannan turaren da shi kuma na tsugunnawa ne sai na jiki,a duk lokacin da zaki yi amfani dashi za'a kawo maki kaskon,dan Allah ki dage ki yi yanda nace,wanda baki gane ba zaki ga komai a rubuce "ta faɗa tana maida su cikin jakkan tare da mika mata,
Amsa tayi" Na gode sosai Ammi"
"Ki yi ƙoƙari ki shiga ki gaida Kaka"
"To" Ta fada tana tashi,
Daki ta kai kayan ta ajiye sannan ta ɗauki ƙaramin hijabi ta saka sannan ta fita,
A hankali take takawa dan ji take kamar iska zai dauke ta saboda rashin nauyin jiki,
Tana dab da shiga shi yana taji an riƙo mata hannu,
Zabura tayi tana dan matsawa baya kaɗan dan ta dan tsorata,
"Oh Sorry na baki tsoro "
Kallon shi take yi tare da kokarin janye hannun ta,sai dai yaƙi saki, "me haka Nurudeen sake min hannu"
Ajiyar zuciya ya sauke"Thank God baki manta suna na ba"
"Ka sake ni bana son haka,idan wani ya ganmu fa"
"Ai nafi son ma a ganmu kin ga sai a saka wannan hoton mijin naki ya sake ki ni kuma na aure ki"
Daga bayan su suka yi an ce"sakar mata hannu"
Duk juyawa suka yi,ganin wanda yayi maganar ne yasa da sauri ya sakar mata hannu,
Ba tare data ƙara kallon su ba ta saka kai ta shige,
Ita gabaɗaya daga shi Nurudeen din har Shamsuddeen,tun lokacin da shi Shamsuddeen din ya bada shaidar karya a gaban su kaka a kan ita da Suraj ta ji ya fita ranta,ɗan girman da take ganin shi dashi duk ta zube,
Da fara'a Kaka ta tare ta "Habiba ya jikin naki"
Zama tayi kusa da ita"na ji sauki Kaka sai kewar ki da nake yi"
Dariya tayi "ke dai faɗi gaskiya,ko dai kewar mijin ki kike yi"
Nan take ta bata fuska tana shirin yin magana kenan suka haɗa ido Maijiddarh dake zaune,
Nan take ta canja salo zuwa yanayin shagwaba "ban cin ya tafi ya barni da kewar shi,ni fushi nake dashi"
Dariya kaka ta saka"ke da ba kida lafiya ina zai dauke ki yai ta yawo dake"wayar ta dake gefe ne ya shiga ƙara,ɗauka tayi tana miƙa ma ta"dubamin wake kira,dan ban fito da Glass ba,
Ganin sunan me kira kaɗai sai da yasa zuciyar ta girgiza"Suraj ne"
"Yauwa dan Halak ke nan,to ɗauki wayar"
Girgiza kai tayi"A'a ai ke ya kira,ni kin ga ma bari naje amma anjima zan dawo "
Karɓa tayi tana karawa a kunne tana dariya,
Daga can ɓangaren yake tambayar "kaka dariyar me kike yi"
"Ni da matar ka mana,wai fushi take da kai"
Dan murmushi ta saki "me tace na mata?
" Ka kira ta ka tambaye ta"
Dariya yayi "ke dai na baki wannan damar ki lallasar min ita"
"Ja'iri ya jikin Nana A'isha"
"Da sauƙi,gata ku gaisa"ya faɗa yana karama Kakar shi wayar a kunne,
_________kwance take saman gado tana rusar kuka,tunda ta dawo shiyan kaka yanzun kusan mintuna talatin kenan tana abu daya,babu abinda yake kara tada mata hankali shine ganin yanda Biba ta zama jaruma akan idanun kowa,
Jin shigowar Momy bai sa ta tsagaita daga kukan da take yi ba,
Zama tayi a bakin gadon tana dagota "zauna muyi magana"
Kokarin komawa kwance take yi"ni dai ki kyale ni,babu wani maganar da zamu yi da ke"
Wannan karon cikin jin haushi ta ce"idan baki saurare ni ba ta yaya zamu samu mafita? Ƙara dagota zaune tayi,
"Yanzun shi Yusuf ya kuke ciki akan maganar shi?
Jan majina tayi tana sheshsheka"idan na kira wayar shi baya ɗauka,karshe ma sai turomin saƙo yayi cewar ni ba iri ajin shi bace,saboda ya lura ni ban waye ba ban San Me duniya ke ciki ba,"
"Tsinanne,shi har ya isa yace haka akanki,ki kyale shi shi yake da asara"
Kara fashewa tayi da kuka"ni yanzun shi kenan haka zan zauna ban yi aure ba,shi kenan nayi Two Zero,gashi Suraj yayi min nisa ko ganin shi bana samun damar yi,har Gara da,wallahi Momy kin cuce ni duk ke kika lalata komai "
Tama rasa me zata ce mata,wani shawara ya kamata ta bata wanda zuciyar ta zai yi sanyi,tun ba yanzun ba ta san cewar ta kwafsa da ya,sai dai bata son ta nuna gazawarta a gaban yar ta,"kin ga kiyi haƙuri bari zan kira Atika zamu samu mafita"a haka ta samu ta shawo kanta da kyar ta yi shiru.
*Bayan sati ɗaya*
A cikin kwanaki bakwai idan ka ga Biba kallo daya zaka mata ka shaida tabbas ta dawo haiyacinta,ta kuma koma asalin Biban ta,
Domin duk wani rama da kodewa da tayi sai da ta ciko,
Ammi kullun cikin bata haɗin danyen madara da na namar kaza take,gashi man da ta bata ya taimaka wurin goge mata fatar jiki,dan har wani tsantsi take yi,cikin turarukan da take sawa tayi har da gashi, ita karan kanta wani lokaci idan ta kalli kanta a madubi tana jinjina ma kayan tare da mamakin in da Ammi ta samo su,dan wani irin fitinannan kanshi ke fita a jinta wanda hatta fitsari idan tayi shi ji take a ciki,har mamaki matsewarta take yi,dan ko kaɗan yatsar ta bai iya wuce kofar wurin,ga wani irin ruwa sake fita,wani lokaci har tsoro abin ke bata yanda yake fita,ita karan kanta ta san ta samu canji da yawa a jikin ta,farin ta ya karu fiye da da,har wani kashe ido take da ƙyalli na musamman,lallai bata san da wani baki ya kamata ta gode ma Ammi ba,babu in da take zuwa sai gaida Kaka sai kuma zaman istigfari wanda a yanzun yawancin lokuta zaka ganta da ƙaramin charbi irin mai batir din nan tana dannawa.
Ammi ce ta buɗe ƙofar ta shigo "har yanzun baki kammala shiryawa ba,kin san saura yan mintuna jirginmu ya tashi"
Juyowa tayi fuskarta dauke da murmushi "na kammala Ammi yanzun takalmi kawai zan saka"
"To ki yi sauri dai dan ke kadai muke jira"ta ƙarasa faɗa tana fita,
"To"
Ita da Ammi ne kawai zasu tafi,dan Amira zata zauna ne a wurin Goggon yara,dan haka Shamsuddeen shi ya kai su har Airport bayan sunyi sallamah da su Kaka,
Ko lokacin da jirgi ke lulawa sararin samaniya lumshe ido tayi tana jero addu'a,kwata-kwata bana jin yin wannan tafiyar,ba dan komai ba sai don bata son haɗuwa dashi,ita da ma ace za'abi nata da Ammi ta barta anan idan har aka gama shari'ar sai su dawo su mai da ita gida,sam bata shirya tarbon wulakanci ba irin nashi,ta tabbatar idan har sun haɗu sai yayi abinda zai ɓata mata rai sannan hankalin shi yake kwanciya,
Ganin tunanin yana ƙoƙarin yi mata yawa ne yasa ta maida hankalin ta wurin jan charbin da take yi,daga haka har bacci ya kwashe ta,
Sai da jirgin su ya sauka sannan Ammi ta tayar da ita suka fito,wani irin sanyi ake yi mai matukar shiga jiki da ratsa kashi,Glass din dake cikin jakkanta ta ciro ta saka a idon ta,wanda ba karamin kyau da ƙara fito da ita yayi ba,dama gashi riga da Siket ne na Atamfa a jikin ta mai kalan ja,sai After dress data saka fara tas mai tsansi shara_shara mara nauyi,sai karamin jakka mai dogon tsarka wanda ake sakalawa a kafaɗa dan ƙarami wanda baici ya ɗauki waya biyu ba,sai ta fito yanda kasan ƴar tsanar zinari,
Ammi ce a gaba ita tana biye da ita a baya jaye da dan madaidaicin Aƙwati,
Sam bai lura da ita ba sai da ya rungume Ammi yana murmushin farin ciki "welcome Ammi"
"Thank you My Dear"
Cikin yanayin shagwaba wanda ba ta san ya iya ba ya shafa cikin shi"Ammi yunwa nake ji,nayi kewar girkin ki,"
"Nikam babu abinda zan kara girka maka tunda ga matarka nan ta maka"
Yana shirin kara yin magana ne idanun shi suka sauka akan ta,duk da akwai Glass mai duhu a idanun ta hakan bai hana shi ganin kwayar idanun ta data cire a kanshi tana ƙara kauda kai,
Gefen lips din shi ya dan ciza yana shafa kai tare da kara kallon ta daga sama har kasa cikin kallon nan nashi na gefen ido,
"Ni dai muge sanyi nake ji"
Maida hankali yayi kan Ammi yana rike hannun ta"muje to"
Tana biye dasu a baya har wurin parking mota inda ya buɗe ma Ammi gidan baya ta shiga,ya mai da kofar ya kulle,da makulli yayi amfani ya danna,nan take but din motar ya buɗe,saka akwatin tayi ta kulle sannan ta zagaya ta buɗe gidan baya kusa da Ammi ta zauna ba tare data kalli koda in da yake ba,tayi alkawarin har su bar garin ba zata taɓa shiga har Karshi ba,
Da kallon mamaki yake binta dashi a ran shi,wanda ko kaɗan bai nuna ba a fili,wato shi zata nuna ma miskilanci,ai kuwa sai ta san dame yi take yi,
Buɗe mazaunin direba yayi ya zauna,yana tayar da motar.......
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*81*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*