← Book details Yar Tsanar Zinari Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 53 OF 96

Sashe 53

Yar Tsanar Zinari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Dan fuskar damuwa ita ma ta nuna"Dady sai dai ku taya mu da addu'a kawai,sai dai abinda Allah tayi"

"Haka ne Addu'a kuwa munanan muna taya ku dashi kullun" Cewar Abbu,

Hango shi zaune tayi a saman wani ɓENCI hannun shi tsarkafe da Ankwa sai masu tsaron shi dake tsaye suna hira suma dan wurin cike yake da jami'an tsaro,

"La gama Suraj din can"

"Ai ba zasu barki ki karasa in da yake ba,dan mun yi kokarin haka ko gaisawa muyi dashi amma sun hana" Cewar Pa,

"Bari naje na gwada ai ni lauyar shi ce"
Bata jira amsar suba ta nufe in da suke,

Suna kallon yanda take Challenging da Masu tsaron shi daga karshe suka ga ta karasa in da yake zaune yana kallon su ta zauna fuskarta dauke da murmushi,

"Barka da Safiya Malam Suraj"

Kim amsa mata yayi,
Bata fuska tayi cikin shagwaba tace"ba zaka amsa ba?

"Ki fara yin sallamah tukun na"

"Ohh na manta tare da Ustazu nake,Assalamu alaika"

Amsawa yayi yana kauda kai daga kallon ta,
"You look Happy"

Dariya ta yi wanda ke ƙara baiyana farin cikin ta"sosai ma domin yau zaka fito"

"Kina da tabbaci a kan haka kenan?

" Hundred and ten percent "

Ganin bai ce komai ba ne yasa tace"to ka juyo mana,ni na fison idan ina magana ana kallo na"

Har yanzun din ma kin kallon nata yayi,
Ji yayi ta shiga jan hannun shi "ni dai ka juyo,ni dai sai ka kalle ni"

Ganin tana shirin ja mai magana ne yasa ya juyo yana daura idanun shi a kanta,
Murmushi ta saki"yauwa ko kaifa,to mu koma maganar mu na jiya tunda ina saka ran komai ya kare anan"

Ganin kamar bai gane me take nufi bane yasa tace"jiya baka tambaye ni me nake bukatar ba"

Dantse Lip dinshi yayi da hokora,wanda ganin abinda yayi ne yasa ta shiga kwasan dariya tana nunashi,shi kuma sai bata fuska yake yi,sai da tayi mai isar ta sannan ta dafa shi"kaga relax,i am not ganna kiss you"

Har yanzun bai cire haƙoran ba"da gaske nake yi,kaga bari ma na fada maka abinda nake so"

Juyowa yayi yana sake Lip dinshi a hankali ya mai da hankalin shi kanta,
Wannan karon a kwai natsuwa a tare da ita wanda hakan ke nuna muhimmancin abinda take son faɗa,
*Idan har naci nasara yau ɗin nan zaka rubuta min takardar saki* ?Ta faɗa tana dagowa suna kallon juya cikin idanu..

🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂

Story & Writing
By
JIDDARH UMAR

🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/

*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~

*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*

*53*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*

Kamar ba zai ce komai ba dan har ta fara cire rai ga amsar shi,
Sai ta ji yace"me yasa kika zaɓi wannan?

Ajiyar zuciya mai ɗan ƙarfi ta sake yayin da nan take wani irin damuwa mai tattare da kunci ya lulluɓe kyakkyawar fuskarta mai dauke da dariya "Ada ina son nayi wani irin tafiya ne da babu waiwaye a cikin ta,sai dai kuma duk nisan da nayi sai gashi na tsince kai na a baya,ina nufin a mafarin tafiyar wanda hakan ke nuna dole sai dai na sake sabuwar farawa,
Ban damu ba ada,amma kuma yanzun na rasa kwarin gwiwa tun mutuwar Ummita,
Na tabbatar a kwai abinda ke jana baya,shi yasa na yanke hukun komawa baya na fuskaci rayuwata dana baro,wacce nake jin tsoro,"dago kai tayi ta kalle shi "a hanya muka haɗu da kai ina kan wannan tafiyar,shi yasa nake son na rabu da kai a wannan hanyar,bana son na tafi da nauyin ka ba tare daka sauke min shi ba,zan koma gida,zan koma wurin iyayena"
Dukar da kai tayi tana share hawayen daya ɗigo daga idanun ta"ka yi hakuri komai na wancan auren Karya ne"

Ya buɗe baki da shirin yin magana kenan sai ga sako daga masinjan kotu wai su shigo lokacin shari'ar su yayi,

Mai da abinda ke zuciyar shi yayi har zuwa sanda zasu fito,

Ita ma mikewa tayi"idan mun fito ma karasa magana,dan bazan koma Kano tare da ku ba"

Bai bata amsa ba suka fara yin gaba da sojojin kafin ta bi su a baya,
Wannan karon ma kamar wancan lokacin ne dan sai da akayi gaisuwa da kuma gabatarwa,

Lauyan wanda suka shigar da kara ne ya tashi ya fara magana "ya mai shari'a ina rokon Kotu idan har wannan karon Barrister Ummu Salma ba ta kawo kwakkwaran hujja ba ina rokon Kotu data yanke ma Suraj hukunci kisa kamar yanda yama Jesica,wanda hakan zai zama izina ga masu hali irin nashi da kuma shi kanshi,na gode ya mai shari'a" Ya fada yana zama irin na takama alamun zamu ga yanda zaki yi,

Mikewa tayi tsaye ita ma"kamar yanda ɗan uwana Barrister ya faɗa ni kaina ba zan so na bata ma kotu lokaci ba,kuma ina rokon kotu duk wanda yake da hannu a cikin wannan shari'ar kotu ta yi gaggawar kamashi ta mai hukunci,sannan abu na karshe shine ina son gabatar ma kotu da wannan ɗan ƙaramin Video nawa kashin na kuma gabatar da wani shaida "

Ɗayan Alkalin ne yace"Kotu ta baki dama"

Masinja ne ta amsa ya haɗa a babban kayan kallon dake cikin Kotun wanda nan take video Manager da mutanen da ba'a gane ko su waye ba suna magana har irin kudin da aka bashi,da sanda aka shigar da gawar dakin daya sauka,har karshen video,

Kowa jikin shi yayi sanyi da ganin wannan video,

"Ya mai shari'a ina rokon kotu ta Bani dama na gabatar da shaidata na biyu"

"Kotu ta baki dama"

Nan ma gabatar masu da Jusif tayi,in da ta shiga yi mashi tambayoyi yana amsawa har ta kammala,

Barrister ne ya tashi yace"ya mai shari'a in ba damuwa ni ma akwai wasu yan tambayoyin da nake son nama Jusif "
Nan ma kotu ta bashi dama,
Sai dai duk irin tambayoyin da take ma Josif domin ya rudar dashi yaki bashi dama,dan ya kwantar da hankali sosai yana amsa mashi kamar yanda ita ta faɗa mashi hakan na iya faruwa,

"Ko zaka iya faɗa ma koto ta yaya kaga sanda suke magana har kaji ka kuma gani?

" Kamar yamda na faɗa Abinci aka kira kicin akai shi ne aka ce na ɗauka na kai, shi yasa naji abinda suke faɗa "

"Kenan haka na nufin Labe ka yi masu?

" Eh to kana iya saka shi a matsayin haka,domin kan ba zan musa ba idan ka ce Labe ne,dan na Labe na dauki su Video domin na yi amfani dashi na samu kuɗin da zan yi bikin birne kanwata,to sai gashi wanda aka ma abin shi ya taimaka min wanda har yanzun ni da mahaifiyata muna cin taimakon,shi yasa ban yi manager barazana da video ba"

"Amma kasan kotu zata iya hukunta ka akan abinda kayi,sannan ba kaji a ranka kaci amanar yarenka da ƴan uwanka ka zabi wasu"

Dariya yayi kaɗan "Amana fa kace, karka manta na faɗa maka uzurina amma a cikin su ba wanda ya iya taimaka min ko yaji tausayi na har ta dashi manager da nake ma aiki,har vashi na roka su Bani sai a dinga cirewa acikin Albashi na amma suka hana ni,yan uwana sai zagi na suke yi,shi kuma wanda ka kira bare ba tare daya sanni ba ko ya damu kabila ta ko addini na ya taimakamin da kuɗaɗe masu yawa, lta yaya ina da abinda zai taimaka mashi ba zan taimaka ba,ni ban damu da hukuncin da za'a min,in dai har zai fita to zan jure"

Mikewa tayi"ya mai shari'a Barrister yana ƙoƙarin sauka kan layi,domin babu in da aka ba da dama akan a hukunta mutum domin yayi Labe,tunda ba'a kamashi da laifin yima Manager barazana ba,ina rokon kotu ta watsar da wannan kalaman na Barrister ta"

"Barrister ka kiyaye" Alkali ya faɗa,

"Na gode ya mai shari'a" Ya faɗa yana komawa ya zauna,domin cikin ikon Allah duk wani dubara nashi ya kucce,

"Sakamakon hujjoji da muka haɗa daga likitoci wanda ke nuna babu shatin hannun Suraj a jikin gawar,da kuma hujjojin da Lauyar shi ta gabatar,wannan Kotun ta wanke Suraj Abdul basir daka zargin da take mai na kisan kai,ta kuma bada dama da a kamo Manager Hotel domin a fara sabuwar shari'a a kanshi" Nan take mutumin ya buga wannan karamin sandar nashi mai fitar da dan sauti,

Duk in da masoyan Young Ustadz suke a fadin duniya masu kallon abinda ke faruwa ta online godiya suka shiga yima Allah daya fito masu da matashin malamin su lafiya,
Yayin da ta gefe ɗaya kuma hankalin wasu a mugun tashe yake fiye da tunani,dan wannan shi ake kira da rashe ya juya da mujiya ko kuma suce Shari'a saɓanin hankali.

Nan take Sojojin suka shiga kwance mashi Ankwa,suna mai ba shi haƙuri,yayin da yana fitowa yan jarida suka lulluɓe shi suna mashi tambayoyi,

Ita kuma ta ɗayan ƙofar ta fito dan ba zata iya da wannan cin koson da akayi mai ba idan sun koma Hotel ya huta sa karasa magana,

Tana fitowa lokacin taga su kuma sun shiga wani bakin mota katuwa,kamar kuma faɗa suke yi ranshi a ɓace,

Tana kallo har matukin motar yaja motar wanda bata sanshi ba,wani tunani ne yazo ranta,to me ke faruwa ai kamata yayi ace taga tsananin farin ciki a fuskar su ba tashin hankali ba da faɗa kamar zasu yi danbe abinda bata taba gani ba,to ko kuma sace su za'a yi,
Kai koma menene gara ta bi bayan su,

Dan haka cikin sauri ta karasa wurin motar Allah yasa Direba na wurin yana jiranta sai gashi ta iso,nuna mashi motar dake kokarin barin harabar Kotun tayi"Yi sauri kabi wannan motar"

"To Hajiya"
Chapter 53 · 0% Book details