Sashe 66
Yar Tsanar Zinari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sam bata jin daɗin rayuwarta,wanda da wannan damar ne ƙawarta Suba tayi amfani ta fara koya mata harkar shaye-shaye,tun daga shan Sigari har zuwa tauna Kwaya,in da Allah ya taimaka dai shine basu shan giya,
Kuma har yau idan har ta kira Mama ta fada mata halin da take ciki sai dai ta ce taci gaba da addu'a,
Ranar da suka kammala makarantar su aka basu takardun kammala karatu,in da ta samu kyautuka masu tari yawa kasancewar ta First Class,
Ba zata taɓa mantawa da wannan ranar ba a rayuwar ta,
Abinda ya faru kuwa a lokacin shine Yaya Abdulrahman baida lafiya sosai har yakai ga an saka masa bututun shaƙar numfashi,wannan dalilin ya hana daga gida babu wanda yazo mata, duk da ba daɗi sai dai bata ji haushin su,
Abinda ya ɓata mata rai shine rashin halarta Yusuf wurin har aka gama ta dawo gida,
Kiran number Mama tayi tana tambayar ta mai jiki,
"Da sauƙi ta amsa mata"
"Mama ki gaishe shi idan ya farka"
"Zai ji"
Dan shiru suka yi na sakanni,kafin tace "Mama,dan Allah ko zaki ma Yusuf magana da kanki ko zai yarda muga likita tunda cikin satin nan zamu dawo,"
"Salma ke ma kisan ban cika son shiga harkar mijin ki ba,ki bari idan kun dawo koma dai menene sai mu yi magana"
"Dan Allah Mama,ni dai nafi son kawai ki mai magana mu ga likita anan"
Numfashi ta sauke"to kai mashi wayar"
Dariya ta saka"na gode Mama"
Koda ta shiga dakin shi yana wanka,"Mama bari zan kira ki zuwa anjima domin yana wanka yanzun"
Da to ta amsa tana kashe wayar,
Ita kuma zama tyi anan bakin gado tana tunanin yanda zasu kare da Mama,Allah dai yasa ya amince,ai kuwa da ta ji daɗi,
Hannunta ne taje ajiyewa shine ya sauka a kan wayar shi dake ajiye,
Murmushi tayi tana juyo da fuskar wayar"shi kenan bai da aiki sai kallo a waya,ji yanda ya kife waya salon mutum ya zauna a sama sekrim ya fashe y..........
Sauran maganar nata ya makale ne sakamakon wani irin mugun gani da tayi a rayuwar ta wanda har yau yake mata gizo a kwakwalwarta,har a bada bata fatan tuna abinda ta gani a wannan wayar,
Domin kuwa Video ne hannun ta ya danna ya shiga play,
Fuskar Baba ne a bayyane yana tsaye haihuwar uwar shi tare da Yusuf da ke kwance yana mika mashi hannu alamun yazo gare shi,
Yanda kasan mata da miji,sumbatar juna suke yi suna shafa jikin juna,yayin da lokacin daya Baba ya shiga aikata Madigo da Yusuf ta baya,suna masu kururuwan jin daɗi,
Haka ma video na gaba,wanda sai da tayi playing uku duk su biyu ne a daki mabanbanta suna aikata Luwaɗi,
Daga zaunen da take ne ta ji idanun ta na ƙoƙarin rufewa,jin alamun zai fito ne yasa da sauri ta ajiye wayar tana fita daga dakin a daddafe saboda duhun da take gani,
Da kyar ta iya kai kanta ɗakin ta zauna a kasa ba tare da ma ta san cewar a kasar take ba,
Tunda take a rayuwar ta bata tsammanin duka su biyu zasu iya aikata haka ba,
Mijin aurenta da mahaifinta,
Duk yanda taso ta ƙaryata kanta kasawa tayi,haka kuma duk yanda taso ta gasgata kanta nan ma kasawa tayi,
Tsabar tashin hankalin da ta shiga ko kiran Mama bata iya ɗauka ba,a ranar tai ma kanta buking din jirgin Nijeriya wanda gobe zai tashi ƙarfe tara na safe,
Ranar duk iya sata irin na barci kasa ɗaukarta yayi,domin idanunta kuwa kafin wayewar gari sun kumbura,haka kuma a lokacin da za'a auna jinin ta to zai iya kaiwa ɗari biyu, ji take zuciyarta ya mata wani irin nauyi har numfashinta bai iya fita da kyau,
Sai dai bata damu ba, da halin da take ciki dan haka ko ta kanshi bata bi ba,ƙarfe takwas na safe ya mata ne a airport,ita bata ma kaunar ta ganshi domin hankalin ta tashi zai ƙara yi,nimar wanda zai karyata mata lamarin take yi,dan haka tana buƙatar Mama,tana son tayi magana da ita, dan baza taɓa iya ɓoye mata wannan lamarin mai girma ba.
Ƙarfe tara jirginsu ya shilla a sararin samaniya.
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*66*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*
Jirgin su na sauka,Adaidaita ta tare ya kawota har cikin unguwar su,
A baki Get tace ya tsaya sannan ta ciro kuɗi ta bashi,ko tsayawa karɓar canji ba tayi ba ta buɗe Get ta shige,
Megadi na ganinta ya taso cikin rawar jiki da murna zai tare ta,sai dai ko takanshi bata iya yi ba sai ma sake mashi aƙwati da tayi ta karasa cikin gida tana kwalla kiran sunan Mama,
Daya daga cikin masu aikin gidan ne take sanar da ita ba kowa a gidan domin duk suna Asibiti wurin Abdulrahman,
Ajiyar zuciya ta sauke mai ƙarfi da tana ƙoƙarin danne duk wani damuwa dake ranta,sai dai wannan lamarin ba irin wanda zata iya jurewa ba na,Oh shiyasa wato bai da ra'ayi akan mata ko,
Dakin Mama ta shiga ta watsa ruwa sannan ta canja kaya,sai dai a kwana ɗayan nan kawai idan ka ga irin ramar da tayi zaka yi tunanin ko tayi shekara ne tana ciyo,
Ta dauko mayafi tana ƙoƙarin fitowa ta tafi Asibitin sai ga Mama ta shigo,
Tsayawa tayi baki buɗe tana mata kallon mamaki"ke ce kuwa da gaske"
Nan take ta ji komai ya ƙara dawo mata saboda,raunin da take kokarin ɓoyewa ne ya baiyana,
Da sauri Mama ta rungume ta tana shafa bayan ta "ina Yusuf din yake?
" Na baro shi a can London"
"Kika taho nan ke kaɗai?ko dai faɗa kuka yi ne?
Girgiza kai tayi cikin tsananin kuka tace" Mama!na ga Baba da Yusuf a waya"
Kasa karasawa tayi sai yanke jiki da tayi ta faɗi,dan nan take numfashin ta ya ɗauke,
Tashin hankali wanda ba'a saka masa rana,domin ihu Mama ta fara tana kira sunan ta,abinda ya kuma bata tsoro shine ganin jini na fita daga kasa ta,
Kasancewar Mama mace mai jiki yasa ta dauke ta da kanta ta saka a mota,direba ne yaja suka tafi Asibiti,inda anan ne aka karbe ta aka shigar da ita dakin taimakon gaggawa,
Sai bayan awa daya da rabi likita ya fito,
Anan yake sanar da Mama cewar sai dai suyi haƙuri domin cikin dake jikinta dan sati takwas ya fita,sannan sun mata wankin ciki,yanzun haka tana dakin hutu suna iya zuwa su ganta,
Kuka Mama ta fara tana riƙe hannun Baba wanda isowar shi kenan ya samu likita na wannan bayanin,
Lallashinta ya fara yi "idan har kina kuka haka ita kuma me ya kama tayi kenan,ya isa haka zo mushiga mu duba ta"
Tare suka shiga dakin da take kwance ita kaɗai,idanun ta a buɗe suke yayin da take kallon sama,
Jin an buɗe ƙofa ne yasa ta maida kallon ta kan ƙofa,ganin shine yasa ta lumshe ido tana ƙoƙarin koran abinda ke zuwa mata a cikin ƙwaƙwalwa,
Da sauri suka karasa inda take,rike hannun ta yayi"Salma kina lafiya?ya jikin naki?yanzun me yake maki ciyo?
A hankali ta zame hannun ta a cikin nashi,"Mama ina Yusuf "
Ajiyar zuciya ta sauke"karki zamu yana hanya,sun riga sunyi magana da Baban ku,ya shaida mashi kina nan"
"Me likita yace" Ta tambaya yayin da maganarta ke fita a hankali,
Kallon juna suka yi sai dai sun kasa faɗa mata,ba tare data ce masu komai ba ta juya baya yayin da take jin hawaye masu zafi na ƙara wanke mata fuska,
Ganin haka ne yasa suka mike suka fita tare da jawo mata ƙofa dan ta samu ta huta,
Ganin sun fita ne yasa ta fashe da kuka sosai ko zata ɗan ji sanyi,ita a rayuwar ta bata San wani irin so take ma Yusuf ba,wannan abun da ta gani koda ace na karya ne yaci ace ta tsane shi,amma ta kasa,sai ji ma da tayi tana son ganin shi,ita ta san wannan shine babban jarabawar ta soyayyar Yusuf,
Ta jima tana kuka kafin barci mai nauyi ya ɗauke ta,
Ƙarfe hudu na yamma aka sallame su suka dawo gida,dan Mama ce ta tsaya da ita sai Yaya Abdulmajid,
Da taimakon Mama ta zauna a kan gado,tana ya mutse fuska,dan har yanzun tana jin murdawar ciki,
Har Mama zata fita ta kira sunan ta,"Mama"
Juyowa tayi, nuna mata kusa da ita tayi alamun ta zauna,
Dawowa tayi ta zauna kusa da ita,
"Mama,kinsan me na gani a wayar Yusuf?
Girgiza mata kai tayi,
" Video Baba na gani tare da Yusuf suna aikata barna,dukkanin su babu kaya ajikin su Mama,Luwaɗi suke aikatawa "share hawayen daya zubo mata tayi" Na kasa yarda,Baba ba zai taɓa aikata haka ba ko Mama?abu ne da Allah ya ya tsine ma masu yi,kuma duk mai yi Allah zai haɗa sa da mutanen Annabi Lut,aci gaba da azabtar dasu har ranar tashin kiyama,Mama saboda Luwaɗi Ubangiji kan iya juya kasa ya kife ta,Nasan Baba ba zai yi haka ba,balle da Mijina "
Rungumeta tayi yayin da taji wani irin tashin hankali na karyo mata,abinda take mata gudu kenan a wancan lokacin amma ita bata fahimtaba,
Dago fuskarta tayi suna fuskantar juna"kina jina ba?
Jinjina kai tayi tana ƙoƙarin rike kukan dake ƙoƙarin kucce mata,
"Kina son mijinki har yanzun?
" Mama na kasa daina son Yusuf,duk da baya kyauta ma rayuwata na kasa tsanar shi,gani nake idan har babu shi ba zan iya rayuwa ba"
"Bansan wani irin so kike mashi ba,in da ace zaki iya hakura dashi da sai nace ki hakura dashi Allah ya zaɓa maki wanda ya fi shi"
Girgiza kai tayi"ba zan iya ba Mama"
Kuma har yau idan har ta kira Mama ta fada mata halin da take ciki sai dai ta ce taci gaba da addu'a,
Ranar da suka kammala makarantar su aka basu takardun kammala karatu,in da ta samu kyautuka masu tari yawa kasancewar ta First Class,
Ba zata taɓa mantawa da wannan ranar ba a rayuwar ta,
Abinda ya faru kuwa a lokacin shine Yaya Abdulrahman baida lafiya sosai har yakai ga an saka masa bututun shaƙar numfashi,wannan dalilin ya hana daga gida babu wanda yazo mata, duk da ba daɗi sai dai bata ji haushin su,
Abinda ya ɓata mata rai shine rashin halarta Yusuf wurin har aka gama ta dawo gida,
Kiran number Mama tayi tana tambayar ta mai jiki,
"Da sauƙi ta amsa mata"
"Mama ki gaishe shi idan ya farka"
"Zai ji"
Dan shiru suka yi na sakanni,kafin tace "Mama,dan Allah ko zaki ma Yusuf magana da kanki ko zai yarda muga likita tunda cikin satin nan zamu dawo,"
"Salma ke ma kisan ban cika son shiga harkar mijin ki ba,ki bari idan kun dawo koma dai menene sai mu yi magana"
"Dan Allah Mama,ni dai nafi son kawai ki mai magana mu ga likita anan"
Numfashi ta sauke"to kai mashi wayar"
Dariya ta saka"na gode Mama"
Koda ta shiga dakin shi yana wanka,"Mama bari zan kira ki zuwa anjima domin yana wanka yanzun"
Da to ta amsa tana kashe wayar,
Ita kuma zama tyi anan bakin gado tana tunanin yanda zasu kare da Mama,Allah dai yasa ya amince,ai kuwa da ta ji daɗi,
Hannunta ne taje ajiyewa shine ya sauka a kan wayar shi dake ajiye,
Murmushi tayi tana juyo da fuskar wayar"shi kenan bai da aiki sai kallo a waya,ji yanda ya kife waya salon mutum ya zauna a sama sekrim ya fashe y..........
Sauran maganar nata ya makale ne sakamakon wani irin mugun gani da tayi a rayuwar ta wanda har yau yake mata gizo a kwakwalwarta,har a bada bata fatan tuna abinda ta gani a wannan wayar,
Domin kuwa Video ne hannun ta ya danna ya shiga play,
Fuskar Baba ne a bayyane yana tsaye haihuwar uwar shi tare da Yusuf da ke kwance yana mika mashi hannu alamun yazo gare shi,
Yanda kasan mata da miji,sumbatar juna suke yi suna shafa jikin juna,yayin da lokacin daya Baba ya shiga aikata Madigo da Yusuf ta baya,suna masu kururuwan jin daɗi,
Haka ma video na gaba,wanda sai da tayi playing uku duk su biyu ne a daki mabanbanta suna aikata Luwaɗi,
Daga zaunen da take ne ta ji idanun ta na ƙoƙarin rufewa,jin alamun zai fito ne yasa da sauri ta ajiye wayar tana fita daga dakin a daddafe saboda duhun da take gani,
Da kyar ta iya kai kanta ɗakin ta zauna a kasa ba tare da ma ta san cewar a kasar take ba,
Tunda take a rayuwar ta bata tsammanin duka su biyu zasu iya aikata haka ba,
Mijin aurenta da mahaifinta,
Duk yanda taso ta ƙaryata kanta kasawa tayi,haka kuma duk yanda taso ta gasgata kanta nan ma kasawa tayi,
Tsabar tashin hankalin da ta shiga ko kiran Mama bata iya ɗauka ba,a ranar tai ma kanta buking din jirgin Nijeriya wanda gobe zai tashi ƙarfe tara na safe,
Ranar duk iya sata irin na barci kasa ɗaukarta yayi,domin idanunta kuwa kafin wayewar gari sun kumbura,haka kuma a lokacin da za'a auna jinin ta to zai iya kaiwa ɗari biyu, ji take zuciyarta ya mata wani irin nauyi har numfashinta bai iya fita da kyau,
Sai dai bata damu ba, da halin da take ciki dan haka ko ta kanshi bata bi ba,ƙarfe takwas na safe ya mata ne a airport,ita bata ma kaunar ta ganshi domin hankalin ta tashi zai ƙara yi,nimar wanda zai karyata mata lamarin take yi,dan haka tana buƙatar Mama,tana son tayi magana da ita, dan baza taɓa iya ɓoye mata wannan lamarin mai girma ba.
Ƙarfe tara jirginsu ya shilla a sararin samaniya.
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*66*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*
Jirgin su na sauka,Adaidaita ta tare ya kawota har cikin unguwar su,
A baki Get tace ya tsaya sannan ta ciro kuɗi ta bashi,ko tsayawa karɓar canji ba tayi ba ta buɗe Get ta shige,
Megadi na ganinta ya taso cikin rawar jiki da murna zai tare ta,sai dai ko takanshi bata iya yi ba sai ma sake mashi aƙwati da tayi ta karasa cikin gida tana kwalla kiran sunan Mama,
Daya daga cikin masu aikin gidan ne take sanar da ita ba kowa a gidan domin duk suna Asibiti wurin Abdulrahman,
Ajiyar zuciya ta sauke mai ƙarfi da tana ƙoƙarin danne duk wani damuwa dake ranta,sai dai wannan lamarin ba irin wanda zata iya jurewa ba na,Oh shiyasa wato bai da ra'ayi akan mata ko,
Dakin Mama ta shiga ta watsa ruwa sannan ta canja kaya,sai dai a kwana ɗayan nan kawai idan ka ga irin ramar da tayi zaka yi tunanin ko tayi shekara ne tana ciyo,
Ta dauko mayafi tana ƙoƙarin fitowa ta tafi Asibitin sai ga Mama ta shigo,
Tsayawa tayi baki buɗe tana mata kallon mamaki"ke ce kuwa da gaske"
Nan take ta ji komai ya ƙara dawo mata saboda,raunin da take kokarin ɓoyewa ne ya baiyana,
Da sauri Mama ta rungume ta tana shafa bayan ta "ina Yusuf din yake?
" Na baro shi a can London"
"Kika taho nan ke kaɗai?ko dai faɗa kuka yi ne?
Girgiza kai tayi cikin tsananin kuka tace" Mama!na ga Baba da Yusuf a waya"
Kasa karasawa tayi sai yanke jiki da tayi ta faɗi,dan nan take numfashin ta ya ɗauke,
Tashin hankali wanda ba'a saka masa rana,domin ihu Mama ta fara tana kira sunan ta,abinda ya kuma bata tsoro shine ganin jini na fita daga kasa ta,
Kasancewar Mama mace mai jiki yasa ta dauke ta da kanta ta saka a mota,direba ne yaja suka tafi Asibiti,inda anan ne aka karbe ta aka shigar da ita dakin taimakon gaggawa,
Sai bayan awa daya da rabi likita ya fito,
Anan yake sanar da Mama cewar sai dai suyi haƙuri domin cikin dake jikinta dan sati takwas ya fita,sannan sun mata wankin ciki,yanzun haka tana dakin hutu suna iya zuwa su ganta,
Kuka Mama ta fara tana riƙe hannun Baba wanda isowar shi kenan ya samu likita na wannan bayanin,
Lallashinta ya fara yi "idan har kina kuka haka ita kuma me ya kama tayi kenan,ya isa haka zo mushiga mu duba ta"
Tare suka shiga dakin da take kwance ita kaɗai,idanun ta a buɗe suke yayin da take kallon sama,
Jin an buɗe ƙofa ne yasa ta maida kallon ta kan ƙofa,ganin shine yasa ta lumshe ido tana ƙoƙarin koran abinda ke zuwa mata a cikin ƙwaƙwalwa,
Da sauri suka karasa inda take,rike hannun ta yayi"Salma kina lafiya?ya jikin naki?yanzun me yake maki ciyo?
A hankali ta zame hannun ta a cikin nashi,"Mama ina Yusuf "
Ajiyar zuciya ta sauke"karki zamu yana hanya,sun riga sunyi magana da Baban ku,ya shaida mashi kina nan"
"Me likita yace" Ta tambaya yayin da maganarta ke fita a hankali,
Kallon juna suka yi sai dai sun kasa faɗa mata,ba tare data ce masu komai ba ta juya baya yayin da take jin hawaye masu zafi na ƙara wanke mata fuska,
Ganin haka ne yasa suka mike suka fita tare da jawo mata ƙofa dan ta samu ta huta,
Ganin sun fita ne yasa ta fashe da kuka sosai ko zata ɗan ji sanyi,ita a rayuwar ta bata San wani irin so take ma Yusuf ba,wannan abun da ta gani koda ace na karya ne yaci ace ta tsane shi,amma ta kasa,sai ji ma da tayi tana son ganin shi,ita ta san wannan shine babban jarabawar ta soyayyar Yusuf,
Ta jima tana kuka kafin barci mai nauyi ya ɗauke ta,
Ƙarfe hudu na yamma aka sallame su suka dawo gida,dan Mama ce ta tsaya da ita sai Yaya Abdulmajid,
Da taimakon Mama ta zauna a kan gado,tana ya mutse fuska,dan har yanzun tana jin murdawar ciki,
Har Mama zata fita ta kira sunan ta,"Mama"
Juyowa tayi, nuna mata kusa da ita tayi alamun ta zauna,
Dawowa tayi ta zauna kusa da ita,
"Mama,kinsan me na gani a wayar Yusuf?
Girgiza mata kai tayi,
" Video Baba na gani tare da Yusuf suna aikata barna,dukkanin su babu kaya ajikin su Mama,Luwaɗi suke aikatawa "share hawayen daya zubo mata tayi" Na kasa yarda,Baba ba zai taɓa aikata haka ba ko Mama?abu ne da Allah ya ya tsine ma masu yi,kuma duk mai yi Allah zai haɗa sa da mutanen Annabi Lut,aci gaba da azabtar dasu har ranar tashin kiyama,Mama saboda Luwaɗi Ubangiji kan iya juya kasa ya kife ta,Nasan Baba ba zai yi haka ba,balle da Mijina "
Rungumeta tayi yayin da taji wani irin tashin hankali na karyo mata,abinda take mata gudu kenan a wancan lokacin amma ita bata fahimtaba,
Dago fuskarta tayi suna fuskantar juna"kina jina ba?
Jinjina kai tayi tana ƙoƙarin rike kukan dake ƙoƙarin kucce mata,
"Kina son mijinki har yanzun?
" Mama na kasa daina son Yusuf,duk da baya kyauta ma rayuwata na kasa tsanar shi,gani nake idan har babu shi ba zan iya rayuwa ba"
"Bansan wani irin so kike mashi ba,in da ace zaki iya hakura dashi da sai nace ki hakura dashi Allah ya zaɓa maki wanda ya fi shi"
Girgiza kai tayi"ba zan iya ba Mama"