Sashe 11
Yar Tsanar Zinari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Nuna mata ɗakinta Amira,sai ki nuna mata kicin ta daura girkin dare,Sinasir da miyan ganye zata yi,sai ki bata shinkafar da nasa kika jika dazu"
"TO Ammi"
"Idan kin kammala nuna mata ki zo ki tafi islamiya kafin yayanki ya shigo"
Nan ma amsa mata tayi,
Tunda taji ance tayi Sinasir taji wani zufa na karyo mata,ita da batama taba jin sunan abinci haka ba,bata ma sanshi ba,shine za'a ce taje tayi,
Duk wani surutu da Amira ke yi ba fahimtar ta take ba,har ta nuna mata ɗakinta wanda karamin gado ne kawai a dakin sai sif da kuma bayi a ciki,
"Yauwa ki ajiye jakkanki kizo in nuna maki kicin dan zan tafi ne,idan kin kammala sai ki zo ki kyara dakin.
Kara fita sukayi ta kaita har babban kicin dinsu ta kuma nuna mata in da kayan abinci suke da komai da komai har da Firig din da suke ajiye nama daban na saka abinsha da ban,
Anan ta barta tsaye ta wuce,
Komawa ɗaki tayi ta ɗauki waya ta kira number A'I,wacce sai da taimata kira uku kafin ta ɗauka so disgusting,jin tana tambayar waye ne,dan ba makaranta tayi ba,cikin jin haushi tace "Biba ce"
"Ohh ya aka yi?
" Sun ce nayi Sinasir,ni kuma ban san yanda ake ba"
Cikin daga murya tace"ni bana jinki ki daga murya kin san wayar ki sai a hankali "
Kara maimaita mata abinda ta ce tayi,
"Oh,shinkafar da aka baki jikakke zaki wanke sosai sai ki zuba a Blender ki duba acikin firig in akwai nono mai kyau sai ki zuba kaɗan a cikin shinkafar sai ki niƙa,idan ya yi sai ki juye a kwano ki rufe shi dakyau sai ki ajiye a wuri mai dumi,ko kuma ki rufe da Flannel zuwa mintuna talatin,daga nan sai ki hau suya"nan ta sanar da ita yanda zata soya,miya kuma tace ta duba a cikin jakkanta zata ga littafin girki idan ta duba akwai wanda kalolin miya ne kadai aciki.
Da taimakon A'i dana takardan nan ta samu tayi Sinasir da miya,kuma ya fita sosai saboda bata cika wuta ba kamar yanda A'I ta faɗa mata.
Koda ta kammala har an fara shiga sallah Magrib,dan haka dakinta ta shiga tayi wanka sannan ta canja kaya tayi sallah,tana idarwa ta koma kicin ta wanke kayan da ta bata ta kuma goge duk inda ta bata,
Samun kanta tayi da son dafa shayi irin wanda ta ɗauki lokaci mai tsayi a rayuwarta bata dafa irin shiba,wato shayin da mahaifinta ke matukar so,kullun ita ke dafa mashi a wannan lokacin.
Dauko tukunya tayi ta dauraye ta goge,sannan ta daura a gas,sai da ya bushe sannan ta zuba ruwa madaidaici a kai,kayan marmari ta dauko ta yanka shi kanana_kanana sai dai banda kankana da gwanda,ta zuba a ciki,sannan ta kawo kayan kamshi ta zuba,hade da wasu ganyayyakin shayi masu kanshi data gani a store,ta rage wuta sosai dan haka a hankali yake dahuwa,
Kulolin abincin data zuba na mutanen gidan ta dauka ta kai in da suke cin abinci,sauran kuma guda biyu ta bar shi a anan ɗan bata san ko na waye ba ne.
Sai da aka idar da sallar Isha'i kafin ta juyo shayin ta tace ta zuba a fulas kananu guda biyu,
Shayin kawai ta diba ta shige dakin ta,
Ammin ce ta fito rike da wani ƙarfe irin wanda masu ciyo a kafa suke amfani dashi,
Kicin ta fara shiga ta dudduba domin tabbatar da tsaftar ta,babu komai na datti domin komai a kyare yake saf,
Dawowa falo tayi nan ma ta buɗe kulolin abincin ta duba,ba laifi tayi ƙoƙari,ganin fulas ne yasa ta buɗe wanda wani irin kanshi mai matukar daɗi ya ɗaki hancin ta,kofi ta jawo ta zuba kaɗan,kalan shayin ruwan zuma ne farar saƙa,kaiwa bakinta tayi ta kurbi kaɗan tana lumshe ido,domin kamshin fruit ne ya haɗu da kayan ƙanshi sai ya bada wani kamshin na musamman,gashi kuma da zaƙi dai dai mitsali, in kana bukatar suger kana iya karawa,
Jinjina kai tayi tana sakin murmushi,
Tana kwance tana jujjuya karamin wayar nan a hannun ta,sai ji tayi ana kwankwasa mata kofa ta ji an yi,tashi tayi ta fara buɗe ƙofar,Amira ce ta gani tsaye,"Ammi na kira"komawa tayi ta dauki karamin hijabin ta iya guiwa ta fito falo,
Tire Amira ta miko mata wanda yake ɗauke da kuloli sai fulas daya a kai"wannan ki kaima Kaka,ni zan kai ma Yaya nashi"
Amsa tayi domin ta gane shiyan,
Kasan cewar gidan akwai haske wuta ta ko'ina yasa bata damu da duhun da garin yayi ba,
Sai da takai ƙofar falon sannan tayi sallamah,amsawa aka yi,
Dan haka jin an amsa ne yasa ta shigo kai tsaye,
Maza ta gani zaune wadanda zata iya kira da manyan samari,biyu suna daddana waya yayin da daya kuma suke surutu da Kaka sai dariya suke,
Kallo daya taimasu ta kauda kai tana gaida su,sai dai ba wanda ya amsa mata,wanda ba karamin haushi hakan ya bata ba,wai yau ita Biba take magana har ayi kaman ba a san da ita ba,
Karasawa tayi wurin kaka cikin girmamawa tace"kaka ina zan ajiye maki abinci "
"Ƴar Albarka ajiye anan,jiki kicin gashi can ki dauko min kofi,"
"To" Ta faɗa tana mikewa tabi hanyar da kaka ta nuna mata,
Tana sako kai cikin kicin din shi kuma yana fitowa hannun shi riƙe da kofi mai dauke da ruwan zafi a ciki,
Cikin rashin sani suka ci karo wanda kofin ruwan zafin ya faɗi ƙasa yayin da ruwan ya zubar mata a hannu,shi kuma ya zubar mai a ƙafa,
Wani irin zafi taji ya sauko tun daga cikin ƙwaƙwalwar ta har yatsun hannun ta,dan haka kafin ma ya ankara dawa yaci karo har ta buɗe baki ta shiga kwara ihu tana yarfe hannu tare da fitowa falo da gudu rike da hunnun tana ihu.
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*13*
*Wannan Littafina mai suna a sama na kuɗi ne,tare da JAURO,idan kina son daya 300,dari uku,guda biyu kuma da Yar Tsanar Zinari tare da Jauro,dari biyar 500,ko wani daya dari uku*
*Hauwa Umar,Zenith Bank, 2284905309*
*ko katin waya na MTN,tare da turo shedar biya ta 08141644865*
Jin ihu ne yasa duk suka maida hankalin su ta ƙofar kicin ɗin,
Ganin yanda ta fito a gigice ne yasa Kaka mikewa tana salati tare da kiran sunan"Biba,Biba"amma ina gaba ɗaya ma hankalin ta baya wurin su domin ni man hanya fita kawai take daga Falon domin ta samu ruwan sanyi ta zuba a hannun,dan ko kaɗan bata shiri da ruwan zafi,
Nafisa ca data fito ɗaki da sauri kaka tace"Nafisa riƙo ta muji me ya faru"
Da sauri ta riƙe mata hannu "sannan Biba,zo ki zauna a nan" Ta faɗa tana zaunar da ita in da Kaka ta nuna mata,
Yarfe hannu kawai take tana hawaye"waiyo hannu na,ki bani ruwa"
Kaka ce tace"miko ruwa "
Da sauri ta bude firig ta dauko goran ruwan sanyi ta buɗe sannan ta mika mata,
Tana ƙoƙarin zubawa ne Kaka ta riƙe goran ruwan"karki zuba ruwan sanyi,muga wurin"ta faɗa tana jujjuya hannun wanda tuni wurin yayi ja,
"Nafisa ɗauko kwano a banɗaki"
Jin takun tafiya a hankali ne yasa suka maida idon su kanshi,shima a hankali yake ɗan dingisa ƙafa in da ruwan zafin ya zubar mai,
Maida kallon ta kan Biba tayi "wai me ya faru ne?
Cikin muryar kuka ta nuna shi da ɗayan hannun " Wannan ne ya kona ne da ruwan zafi,"
Ƙara kallon shi suka yi,shi kuma sai ɓata fuska da yayi ya nime wuri ya zauna,
Ajiyar zuciya kaka ta sauke"Nurudeen zo dan Allah ka duba mata wannan hannun gashi har yayi ja"
Bai ci musu ba,domin kuwa tunda ta fito kicin din idon shi ke kanta har zamanta ƙare mata kallo yake tun daga kan ɗan yatsar ƙafarta har zuwa fuskarta wanda ɗan kukan da tayi yayi ja,
Tasowa yayi ya zauna a gefenta,"kawo hannun mu gani "
Ba tare da tunanin komai ba ta daura tafin hannun ta saman nashi,
Kallon yatsun hannun nata yake wanda suke zaro_zaro,gasu farare tas,ɗan shafa tafin hannun yayi yayin da yaji wani laushi da tsantsi a hannun nata,kai ko fatan ta abin kallo ne,"Sorry "ya faɗa a hankali,
Buɗe first aid box,da Nafisa ta kawo yayi yana ciro wani kwalin cream wanda naga an rubuta Ketoconazole a jikin shi,buɗewa yayi ya ciro sannan ya ɗauki cotton Bud's guda daya ya tatsa Cream din a jiki sannan ya shiga shafamata a hankali yana kallon yanda take dan matse ido,
Koda ya kammala shafamata cream ɗin bai sake mata hannu ba,sai kallon hannu yake domin ba karamin jan hankalin yake ba.
Sai sannu kaka ke mata,
Haɗa ido suka yi dashi dake zaune ya wani hakimce yana shan abu a kofi,
Harara ta zuba mai,tana ɗauke kai,domin ba karamin haushe ya bata ba,ko sannu bai ce mata ba,
Ganin abunda ta mai me yasa ya kauda kai yana jinjina rashin kunyar ta,
Dariya Ibrahim yayi yana ajiye wayar hannun shi"ƴan mata ya kike hararar mana Young Ustadz"domin ya ga abinda ta yi,"Kaka ina kika samo yarinya mai kyau haka?
"Tubarkarla,mai taimakama Ammi ce,dazu ta zo,gashi Sorajo na ƙoƙarin kona yar mutane"
Jin yanda yake shafamata tafin hannu ne yasa ta zare hannun ta a cikin nashi tana kallon shi,
Murmushi ya sakar mata,
Ibrahim ne ya katse su"ni dai tamin Kaka,me sunan ta"
Ɓata fuska tayi"ni fa bana son shashanci,"
Mikewa yayi tsaye "Tsohuwa sai da safe"
"Ba zaka ce mata sannu ba,bancin ka kona ta da ruwan zafi"
Bai bata amsa ba yasa kai ya fita,
Cikin jin haushi tace "ku tashi ku tafi na sallame ku"
Mikewa suka yi suma cewa "tunda laifin wani ya shafe mu sai da safe"
Sakawa tayi Nafisa ta rakata har shiyan su sannan ta dawo,dan ita a nan shiyan kaka take kwana,
"TO Ammi"
"Idan kin kammala nuna mata ki zo ki tafi islamiya kafin yayanki ya shigo"
Nan ma amsa mata tayi,
Tunda taji ance tayi Sinasir taji wani zufa na karyo mata,ita da batama taba jin sunan abinci haka ba,bata ma sanshi ba,shine za'a ce taje tayi,
Duk wani surutu da Amira ke yi ba fahimtar ta take ba,har ta nuna mata ɗakinta wanda karamin gado ne kawai a dakin sai sif da kuma bayi a ciki,
"Yauwa ki ajiye jakkanki kizo in nuna maki kicin dan zan tafi ne,idan kin kammala sai ki zo ki kyara dakin.
Kara fita sukayi ta kaita har babban kicin dinsu ta kuma nuna mata in da kayan abinci suke da komai da komai har da Firig din da suke ajiye nama daban na saka abinsha da ban,
Anan ta barta tsaye ta wuce,
Komawa ɗaki tayi ta ɗauki waya ta kira number A'I,wacce sai da taimata kira uku kafin ta ɗauka so disgusting,jin tana tambayar waye ne,dan ba makaranta tayi ba,cikin jin haushi tace "Biba ce"
"Ohh ya aka yi?
" Sun ce nayi Sinasir,ni kuma ban san yanda ake ba"
Cikin daga murya tace"ni bana jinki ki daga murya kin san wayar ki sai a hankali "
Kara maimaita mata abinda ta ce tayi,
"Oh,shinkafar da aka baki jikakke zaki wanke sosai sai ki zuba a Blender ki duba acikin firig in akwai nono mai kyau sai ki zuba kaɗan a cikin shinkafar sai ki niƙa,idan ya yi sai ki juye a kwano ki rufe shi dakyau sai ki ajiye a wuri mai dumi,ko kuma ki rufe da Flannel zuwa mintuna talatin,daga nan sai ki hau suya"nan ta sanar da ita yanda zata soya,miya kuma tace ta duba a cikin jakkanta zata ga littafin girki idan ta duba akwai wanda kalolin miya ne kadai aciki.
Da taimakon A'i dana takardan nan ta samu tayi Sinasir da miya,kuma ya fita sosai saboda bata cika wuta ba kamar yanda A'I ta faɗa mata.
Koda ta kammala har an fara shiga sallah Magrib,dan haka dakinta ta shiga tayi wanka sannan ta canja kaya tayi sallah,tana idarwa ta koma kicin ta wanke kayan da ta bata ta kuma goge duk inda ta bata,
Samun kanta tayi da son dafa shayi irin wanda ta ɗauki lokaci mai tsayi a rayuwarta bata dafa irin shiba,wato shayin da mahaifinta ke matukar so,kullun ita ke dafa mashi a wannan lokacin.
Dauko tukunya tayi ta dauraye ta goge,sannan ta daura a gas,sai da ya bushe sannan ta zuba ruwa madaidaici a kai,kayan marmari ta dauko ta yanka shi kanana_kanana sai dai banda kankana da gwanda,ta zuba a ciki,sannan ta kawo kayan kamshi ta zuba,hade da wasu ganyayyakin shayi masu kanshi data gani a store,ta rage wuta sosai dan haka a hankali yake dahuwa,
Kulolin abincin data zuba na mutanen gidan ta dauka ta kai in da suke cin abinci,sauran kuma guda biyu ta bar shi a anan ɗan bata san ko na waye ba ne.
Sai da aka idar da sallar Isha'i kafin ta juyo shayin ta tace ta zuba a fulas kananu guda biyu,
Shayin kawai ta diba ta shige dakin ta,
Ammin ce ta fito rike da wani ƙarfe irin wanda masu ciyo a kafa suke amfani dashi,
Kicin ta fara shiga ta dudduba domin tabbatar da tsaftar ta,babu komai na datti domin komai a kyare yake saf,
Dawowa falo tayi nan ma ta buɗe kulolin abincin ta duba,ba laifi tayi ƙoƙari,ganin fulas ne yasa ta buɗe wanda wani irin kanshi mai matukar daɗi ya ɗaki hancin ta,kofi ta jawo ta zuba kaɗan,kalan shayin ruwan zuma ne farar saƙa,kaiwa bakinta tayi ta kurbi kaɗan tana lumshe ido,domin kamshin fruit ne ya haɗu da kayan ƙanshi sai ya bada wani kamshin na musamman,gashi kuma da zaƙi dai dai mitsali, in kana bukatar suger kana iya karawa,
Jinjina kai tayi tana sakin murmushi,
Tana kwance tana jujjuya karamin wayar nan a hannun ta,sai ji tayi ana kwankwasa mata kofa ta ji an yi,tashi tayi ta fara buɗe ƙofar,Amira ce ta gani tsaye,"Ammi na kira"komawa tayi ta dauki karamin hijabin ta iya guiwa ta fito falo,
Tire Amira ta miko mata wanda yake ɗauke da kuloli sai fulas daya a kai"wannan ki kaima Kaka,ni zan kai ma Yaya nashi"
Amsa tayi domin ta gane shiyan,
Kasan cewar gidan akwai haske wuta ta ko'ina yasa bata damu da duhun da garin yayi ba,
Sai da takai ƙofar falon sannan tayi sallamah,amsawa aka yi,
Dan haka jin an amsa ne yasa ta shigo kai tsaye,
Maza ta gani zaune wadanda zata iya kira da manyan samari,biyu suna daddana waya yayin da daya kuma suke surutu da Kaka sai dariya suke,
Kallo daya taimasu ta kauda kai tana gaida su,sai dai ba wanda ya amsa mata,wanda ba karamin haushi hakan ya bata ba,wai yau ita Biba take magana har ayi kaman ba a san da ita ba,
Karasawa tayi wurin kaka cikin girmamawa tace"kaka ina zan ajiye maki abinci "
"Ƴar Albarka ajiye anan,jiki kicin gashi can ki dauko min kofi,"
"To" Ta faɗa tana mikewa tabi hanyar da kaka ta nuna mata,
Tana sako kai cikin kicin din shi kuma yana fitowa hannun shi riƙe da kofi mai dauke da ruwan zafi a ciki,
Cikin rashin sani suka ci karo wanda kofin ruwan zafin ya faɗi ƙasa yayin da ruwan ya zubar mata a hannu,shi kuma ya zubar mai a ƙafa,
Wani irin zafi taji ya sauko tun daga cikin ƙwaƙwalwar ta har yatsun hannun ta,dan haka kafin ma ya ankara dawa yaci karo har ta buɗe baki ta shiga kwara ihu tana yarfe hannu tare da fitowa falo da gudu rike da hunnun tana ihu.
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*13*
*Wannan Littafina mai suna a sama na kuɗi ne,tare da JAURO,idan kina son daya 300,dari uku,guda biyu kuma da Yar Tsanar Zinari tare da Jauro,dari biyar 500,ko wani daya dari uku*
*Hauwa Umar,Zenith Bank, 2284905309*
*ko katin waya na MTN,tare da turo shedar biya ta 08141644865*
Jin ihu ne yasa duk suka maida hankalin su ta ƙofar kicin ɗin,
Ganin yanda ta fito a gigice ne yasa Kaka mikewa tana salati tare da kiran sunan"Biba,Biba"amma ina gaba ɗaya ma hankalin ta baya wurin su domin ni man hanya fita kawai take daga Falon domin ta samu ruwan sanyi ta zuba a hannun,dan ko kaɗan bata shiri da ruwan zafi,
Nafisa ca data fito ɗaki da sauri kaka tace"Nafisa riƙo ta muji me ya faru"
Da sauri ta riƙe mata hannu "sannan Biba,zo ki zauna a nan" Ta faɗa tana zaunar da ita in da Kaka ta nuna mata,
Yarfe hannu kawai take tana hawaye"waiyo hannu na,ki bani ruwa"
Kaka ce tace"miko ruwa "
Da sauri ta bude firig ta dauko goran ruwan sanyi ta buɗe sannan ta mika mata,
Tana ƙoƙarin zubawa ne Kaka ta riƙe goran ruwan"karki zuba ruwan sanyi,muga wurin"ta faɗa tana jujjuya hannun wanda tuni wurin yayi ja,
"Nafisa ɗauko kwano a banɗaki"
Jin takun tafiya a hankali ne yasa suka maida idon su kanshi,shima a hankali yake ɗan dingisa ƙafa in da ruwan zafin ya zubar mai,
Maida kallon ta kan Biba tayi "wai me ya faru ne?
Cikin muryar kuka ta nuna shi da ɗayan hannun " Wannan ne ya kona ne da ruwan zafi,"
Ƙara kallon shi suka yi,shi kuma sai ɓata fuska da yayi ya nime wuri ya zauna,
Ajiyar zuciya kaka ta sauke"Nurudeen zo dan Allah ka duba mata wannan hannun gashi har yayi ja"
Bai ci musu ba,domin kuwa tunda ta fito kicin din idon shi ke kanta har zamanta ƙare mata kallo yake tun daga kan ɗan yatsar ƙafarta har zuwa fuskarta wanda ɗan kukan da tayi yayi ja,
Tasowa yayi ya zauna a gefenta,"kawo hannun mu gani "
Ba tare da tunanin komai ba ta daura tafin hannun ta saman nashi,
Kallon yatsun hannun nata yake wanda suke zaro_zaro,gasu farare tas,ɗan shafa tafin hannun yayi yayin da yaji wani laushi da tsantsi a hannun nata,kai ko fatan ta abin kallo ne,"Sorry "ya faɗa a hankali,
Buɗe first aid box,da Nafisa ta kawo yayi yana ciro wani kwalin cream wanda naga an rubuta Ketoconazole a jikin shi,buɗewa yayi ya ciro sannan ya ɗauki cotton Bud's guda daya ya tatsa Cream din a jiki sannan ya shiga shafamata a hankali yana kallon yanda take dan matse ido,
Koda ya kammala shafamata cream ɗin bai sake mata hannu ba,sai kallon hannu yake domin ba karamin jan hankalin yake ba.
Sai sannu kaka ke mata,
Haɗa ido suka yi dashi dake zaune ya wani hakimce yana shan abu a kofi,
Harara ta zuba mai,tana ɗauke kai,domin ba karamin haushe ya bata ba,ko sannu bai ce mata ba,
Ganin abunda ta mai me yasa ya kauda kai yana jinjina rashin kunyar ta,
Dariya Ibrahim yayi yana ajiye wayar hannun shi"ƴan mata ya kike hararar mana Young Ustadz"domin ya ga abinda ta yi,"Kaka ina kika samo yarinya mai kyau haka?
"Tubarkarla,mai taimakama Ammi ce,dazu ta zo,gashi Sorajo na ƙoƙarin kona yar mutane"
Jin yanda yake shafamata tafin hannu ne yasa ta zare hannun ta a cikin nashi tana kallon shi,
Murmushi ya sakar mata,
Ibrahim ne ya katse su"ni dai tamin Kaka,me sunan ta"
Ɓata fuska tayi"ni fa bana son shashanci,"
Mikewa yayi tsaye "Tsohuwa sai da safe"
"Ba zaka ce mata sannu ba,bancin ka kona ta da ruwan zafi"
Bai bata amsa ba yasa kai ya fita,
Cikin jin haushi tace "ku tashi ku tafi na sallame ku"
Mikewa suka yi suma cewa "tunda laifin wani ya shafe mu sai da safe"
Sakawa tayi Nafisa ta rakata har shiyan su sannan ta dawo,dan ita a nan shiyan kaka take kwana,