Sashe 28
Yar Tsanar Zinari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dago idanun shi yayi wanda har yanzun suke a birkice" Na'am "ya amsa da muryar shi da bata fita sosai,
" Ya muka yi da kai a game da bikin ka da Maijiddarh?
Shiru yayi yana kallon ta yana son ya fahimci inda maganar ta ya dosa"na ce na Amince"
"Me yasa tun farko da kaji kana ra'ayin mace baka faɗa amaka aure ba?
Wannan karon kam ya rasa ida zaren maganar ya dosa,dan haka shiru yayi bai ce mata komai ba,tunda bai san me take nufi ba,
Kuka ta fashe dashi" Na dauke ka tamkar jika na,harma na fifita ka akan sauran,na nuna maka soyayya har na dauki jika ta ina ƙoƙarin baka a matsayin matar auren ka,ba tare dana duba laifin dana ganka kana aikatawa ba,amma shine ba zaka iya riƙe kanka har nan da kwana uku ba sai ka nuna asalin halin naka"
Tofa gabaɗaya maganar kaka ya ɗaure ma kowa kai a wannan wurin face wadanda dama suka san da shirin,
Abbu ne yace"me kike nufi da kasa riƙe kai Mama,da kuma wani hali na shi?
Cikin kuka ta nunashi da hannun ta"gashi nan ku tambaye shi me yake aikatawa a ɓoye da yar mutane"
Duk maida kallon su kanshi suka yi,suna jiran jin karin baya ni,sai dai kanshi a kasa yake domin ji yake kamar kanshi na juyawa,yau me ke shirin faruwa dashi,
Ammi da tuni ta fara hawaye tace "Suraj kai muke saurare ka faɗa mana Komai"
"Ai ba zai iya faɗa ba amma ku duba abinda ya ke aikatawa kenan" Ta fada tana watso wasu hotunan a tsakiyar falon,
Gabaɗaya hankalin duk wanda ke cikin falon tashi yayi,domin kuwa tabbas shi ne ba wani ba,nan take kaji salati ya shiga tashi ta ko ina,
Tunda ya daga kai ka kalli hotunan saudaya ya maida kai ya dukar,tabbas yanzun kam yasan meke shirin faruwa dashi,
Kukan Ammi ne ya karaɗe falon sosai yayin da cikin gunjin kuka ta nufi shi,rike hannun shi tayi ta duka a gaban shi "Suraj!dan Allah ka ce min ba kai bane wannan,kaci musu,ka ce ba kai bane" Ta fada cikin matsanancin kuka da tashin hankali,
Dady ne yace "dama ita tsintacciyar mage bata mage,Allah mun gode maka daka nuna mana wannan sirrin nashi kafin haɗa zuri'a dashi,dan haka na janye baka aure yata,ba zan iya haɗa zuri'a da kai ba"
Ammi ce ta riƙe hannun Abbu wanda yake zaune yama kasa cewa komai "dan Allah Sufyan kama ɗan Uwan ka bayani,wannan ba halin ɗan mu bane,wannan ba halin Suraj bane"
Sai dai ga mamakin ta sai zame hannun shi yayi daga cikin nata"ɗan ki dai,domin kowa yasan cewa Suraj ba ɗa na bane,ƴaƴa na biyu ne daga Shamsuddeen sai Amira,wanda ina da tabbacin Shamsuddeen ba zai taba aikata hakan ba saboda ya haɗa jini da ni,banga laifin wadanda suke cewa basu karɓar dan wani a matsayin nasu ba,saboda karya bata ma nasu tarbiya,ƙila dai ta ɓangaren ubanshi ya dauko irin wannan halin"
"Ai matsalar Auren mace mai ɗa kenan,yanzun ga irin ta nan,ka jawo shi a jiki tamkar naka,amma ji abin kunyar da yazo yake aikatawa,mun gode ma Allah da abun ya tsaya a kan masu aiki bai kai ga ya'yan mu mata ba" Cewar Goggo,
Kukan Ammi ne ke kara ƙaruwa"Kufa malamai ne,masana Addini,me yasa kuke faɗin haka,me yasa ba za a ji ta bakin shi ba"
"Ammi sai dai kawai in baki son ki yarda da abinda ke gabanki na zahiri,amma ni kai na na sha ganin shi ba sau daya ba,ba sau biyu ba"
"Amma me yasa baka taɓa sanar da ni ba Shamsuddeen,me yasa?
" Saboda koda na faɗa maki ba yarda zaki yi ba Ammi,kamar dai yanzun ma da ga shaida a gabanki amma baki son ki gasgata "
"Ai ku ne baku sani ba,amma ni ba abinda ban sani ba,ko yawon tafiye-tafiye da yake yi na karyan yana zuwa wa'azi ai tare yake zuwa da ƴan matan shi,wasu kuma a can yake samu suna hutawar su" Cewar Ibrahim,
"Haɗa jini da Bayahude mutum hatsari ne,komai daren daɗewa sai ya nuna maka halin su na Akuyanci,ni banga laifinshi ba tunda Kakar shi bayahudiya ce wa yasan abinda ta aikata lokacin yarinta,kuma shi dama ƙazanta ai jini yake bi"Hajiya Rahama ta faɗa,
Jin maganganun su yake har tsakiyar kanshi,suna mai amsa kuwa,ko wace kallama daya da zasu faɗa ji yake yana shiga cikin jikin shi ya bula zuciyar shi ya shige,zafi yake ji,raɗaɗi yake ji sosai,ji yake kamar yace su tsaya ya huta,su tsaya ya sauke numfashi daya tsayamai a kirji kafin su cigaba,sai dai ya kasa koda ɗaga kai ya kalle su,domin mutanen da yayi rayuwa dasu,ya yarda dasu,yake zaune dasu tamkar ahalin shi sune suke fadar munanan kalamar akanshi,harda wanda yake kira da dan uwa kuma yaya,Shamsuddeen,da kuma wanda ya ɗauka a matsayin Kani,Ibrahim,
Yana sauraran yanda Ammin shi ke kuka,duk kuma saboda shi.
Maijiddarh wacce tunda taji batun fasa aurenta take kuka ta matso wurin kaka,cikin kuka tace"Kaka kema kinsan ina son shi,ba zan iya rayuwa ba idan bashi,dan Allah kar ki bari a fasa wannan auren ina son shi a haka"
Jawota Aunty Atika keyi"kina da hankali kuwa,ba ki ganin abinda ke gaban ki,"ta faɗa tana nuna mata hotunan da har yanzun suke watse a tsakar falon"a haka zaki aure shi,mutum irin shi sam bai dace da zuri'ar wannan gidan ba,kuma koda kin aure shi ba fasa halin shi zai yi ba,dan haka ki dawo hankali ki"
Aunty Hajjo ce tana mikewa ta kai mata Lafiyayyen mari a fuskar ta.........
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*30*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*
Aunty Hajjo ce tana mikewa ta kai mata lafiyayyen mari a fuskarta,
Duk mai da kallo kansu suka yi,sai dai shi uban gaiyar ko inda suke bai kalla ba,sai ma lumshe idanun shi da yayi gabaɗaya,
Nuna ta tayi da ɗan yatsa"ai wannan ita ce babbar munafukar,kuma mai laifin,ta yaya ta aikata abu irin haka sannan ta zauna ba tare da tace komai ba"
Dafe kumatunta tayi da taji yana mata raɗaɗi dan wallahi har gara marin da ya mata dazu akan wannan na Aunty Hajjo dan katon hannu gare ta,
Tattara hotunan tayi ta watso mata shi a jikinta,"tunda shi dan gidan Yahudawa yaki mana bayani ke sai ki mana bayani akan waɗannan "
Hajiya Saude ce tace"kika sani ko tursasa ta yayi?
Daukar hotunan take cikin tsananin mamaki wanda ya kasa boyuwa,kallon wanda ke hannun ta yi"wannan lokacin da muka je Asibiti ne"
Da sauri Ibrahim yace"ba dai zubar da ciki ba"
Duk da halin da take ciki hakan bai hana ta hararanshi ba"tir,tir Allah ya kiyaye duk iskanci na ban taba zubar da ciki ba"
Salati yawancin mutanen falon suka saka yayin da Kaka da Ammi suke ci gaba da kuka,
"Kenan dama kun daɗe kuna iskanci?wannan karon Shamsuddeen ne ya mata tambayar,
Dago kai tayi ta kalle shi,sannan ta maida kallon ta kanshi,idanun shi a lumshe suke,sai dai fuskar nan nashi yayi ja,
Wannan ne karo na farko da taji ya bala'in bata tausayi,domin duk maganar da suke faɗi da aibantashin da suke yi bai ce masu komai ba,bai kuma ƙarya tasu ba,Ashe shi ba Asalin jikan kaka bane,kuma ba ɗan Abbu bane,to me yasa zasu mai irin wannan fahimtar lokaci ɗaya haka,
"Ke muke saurare" Ya kara faɗa,
"Ban taɓa Iskanci da shi ba,asalima babu wani abu ɗaya taba shiga tsakani na dashi sai yau,wannan hoton da kuke gani lokacin da suka raka ni Asibiti ne shida Amira duba Mama ta da bata da lafiya"
"To ya akayi ya rungume ki a hoton"
Shiru tayi kamar mai nazari,tabbas ma nazarin take yi,domin a ranar da abin ya faru taci kwaya bata cikin hankalin ta"ba zan iya tunawa ba"
"Magana ta tabbata kenan,a kwai dai abinda ya kaimu" Nuna ɗayan hoton yayi "wannan ma kamar na yau ne?
" Eh tabbas na yau ne,sai dai ba laifin sa bane,ni ce da kaina na sumbace shi ba tare da son ranshi ba"
Duka Aunty Atika takai mata"sannu manafuka uwar Karuwai,wato kare shi zaki yi,ta yaya zaki sumbace shi ba da son ranshi ba,kalli fa harda rike mata ƙwanƙwaso"
Janye ta Hajiya Rahama tayi"rufamin Asiri kar ki haɗa kashi da ita,domin irin su ba'a faɗa dasu sai su shafa maka zufan su na tsiya "
"Abu ɗaya kawai nasan zan masa na karshe a matsayina na wanda yake amsa sunan mahaifin shi,shine aura masa wannan yarinyar a yau ta yanda zai zama ishara a gare shi"cewar Abu Sufyan
Tunda aka fara maganar nan wannan ne karo na farko daya buɗe baki yayi magana" Kayi haƙuri Abbu amma ban yarda da wannan auren ba"
Salati Goggo ta saka"kai kaji min ɗan duniya,bayan ka gama ɓata masu yarinya shine zaka ce ba zaka aure ta ba,ai kuwa baka isa ba"
"Ai dama irin su haka suke,anci moriyar ganga za'a yada koren ta"
A zabure ita ma tace"wallahi ban amince ba,ni ba zan aure shi ba,"
Buge mata baki Aunty Atika tayi"munafuka yi mana shiru"
Kallon Ammi Kaka tayi"idanun ɗan ki ya buɗe sosai yanzun,har tsoron yi masa magana nake yi,dan haka ina ga ƙila ke ki nada sauran daraja a idanun shi ki masa magana ko zai amince"
Kafin tace komai sai ji suka yi yace "na amince"
Ihu ta saka "wallahi ban amince ba,ni dai ba na son shi tafiya ta ma zan yi yanzun" Ta faɗa tana ƙoƙarin mikewa,
Aunty Hajjo ta jawota kiiiii ta cillata dakin kaka ta kulle ƙofa "tunda har kwadayin ku yaja maku to sai dai ku karasa da juna"
"So nake a ɗaura auren daganan zuwa sallar Magariba,zuwa lokacin Iyayen yarinyar sun iso an masu bayani nasan idan sun ji komai ba zasu ki yarda ba"
" Ya muka yi da kai a game da bikin ka da Maijiddarh?
Shiru yayi yana kallon ta yana son ya fahimci inda maganar ta ya dosa"na ce na Amince"
"Me yasa tun farko da kaji kana ra'ayin mace baka faɗa amaka aure ba?
Wannan karon kam ya rasa ida zaren maganar ya dosa,dan haka shiru yayi bai ce mata komai ba,tunda bai san me take nufi ba,
Kuka ta fashe dashi" Na dauke ka tamkar jika na,harma na fifita ka akan sauran,na nuna maka soyayya har na dauki jika ta ina ƙoƙarin baka a matsayin matar auren ka,ba tare dana duba laifin dana ganka kana aikatawa ba,amma shine ba zaka iya riƙe kanka har nan da kwana uku ba sai ka nuna asalin halin naka"
Tofa gabaɗaya maganar kaka ya ɗaure ma kowa kai a wannan wurin face wadanda dama suka san da shirin,
Abbu ne yace"me kike nufi da kasa riƙe kai Mama,da kuma wani hali na shi?
Cikin kuka ta nunashi da hannun ta"gashi nan ku tambaye shi me yake aikatawa a ɓoye da yar mutane"
Duk maida kallon su kanshi suka yi,suna jiran jin karin baya ni,sai dai kanshi a kasa yake domin ji yake kamar kanshi na juyawa,yau me ke shirin faruwa dashi,
Ammi da tuni ta fara hawaye tace "Suraj kai muke saurare ka faɗa mana Komai"
"Ai ba zai iya faɗa ba amma ku duba abinda ya ke aikatawa kenan" Ta fada tana watso wasu hotunan a tsakiyar falon,
Gabaɗaya hankalin duk wanda ke cikin falon tashi yayi,domin kuwa tabbas shi ne ba wani ba,nan take kaji salati ya shiga tashi ta ko ina,
Tunda ya daga kai ka kalli hotunan saudaya ya maida kai ya dukar,tabbas yanzun kam yasan meke shirin faruwa dashi,
Kukan Ammi ne ya karaɗe falon sosai yayin da cikin gunjin kuka ta nufi shi,rike hannun shi tayi ta duka a gaban shi "Suraj!dan Allah ka ce min ba kai bane wannan,kaci musu,ka ce ba kai bane" Ta fada cikin matsanancin kuka da tashin hankali,
Dady ne yace "dama ita tsintacciyar mage bata mage,Allah mun gode maka daka nuna mana wannan sirrin nashi kafin haɗa zuri'a dashi,dan haka na janye baka aure yata,ba zan iya haɗa zuri'a da kai ba"
Ammi ce ta riƙe hannun Abbu wanda yake zaune yama kasa cewa komai "dan Allah Sufyan kama ɗan Uwan ka bayani,wannan ba halin ɗan mu bane,wannan ba halin Suraj bane"
Sai dai ga mamakin ta sai zame hannun shi yayi daga cikin nata"ɗan ki dai,domin kowa yasan cewa Suraj ba ɗa na bane,ƴaƴa na biyu ne daga Shamsuddeen sai Amira,wanda ina da tabbacin Shamsuddeen ba zai taba aikata hakan ba saboda ya haɗa jini da ni,banga laifin wadanda suke cewa basu karɓar dan wani a matsayin nasu ba,saboda karya bata ma nasu tarbiya,ƙila dai ta ɓangaren ubanshi ya dauko irin wannan halin"
"Ai matsalar Auren mace mai ɗa kenan,yanzun ga irin ta nan,ka jawo shi a jiki tamkar naka,amma ji abin kunyar da yazo yake aikatawa,mun gode ma Allah da abun ya tsaya a kan masu aiki bai kai ga ya'yan mu mata ba" Cewar Goggo,
Kukan Ammi ne ke kara ƙaruwa"Kufa malamai ne,masana Addini,me yasa kuke faɗin haka,me yasa ba za a ji ta bakin shi ba"
"Ammi sai dai kawai in baki son ki yarda da abinda ke gabanki na zahiri,amma ni kai na na sha ganin shi ba sau daya ba,ba sau biyu ba"
"Amma me yasa baka taɓa sanar da ni ba Shamsuddeen,me yasa?
" Saboda koda na faɗa maki ba yarda zaki yi ba Ammi,kamar dai yanzun ma da ga shaida a gabanki amma baki son ki gasgata "
"Ai ku ne baku sani ba,amma ni ba abinda ban sani ba,ko yawon tafiye-tafiye da yake yi na karyan yana zuwa wa'azi ai tare yake zuwa da ƴan matan shi,wasu kuma a can yake samu suna hutawar su" Cewar Ibrahim,
"Haɗa jini da Bayahude mutum hatsari ne,komai daren daɗewa sai ya nuna maka halin su na Akuyanci,ni banga laifinshi ba tunda Kakar shi bayahudiya ce wa yasan abinda ta aikata lokacin yarinta,kuma shi dama ƙazanta ai jini yake bi"Hajiya Rahama ta faɗa,
Jin maganganun su yake har tsakiyar kanshi,suna mai amsa kuwa,ko wace kallama daya da zasu faɗa ji yake yana shiga cikin jikin shi ya bula zuciyar shi ya shige,zafi yake ji,raɗaɗi yake ji sosai,ji yake kamar yace su tsaya ya huta,su tsaya ya sauke numfashi daya tsayamai a kirji kafin su cigaba,sai dai ya kasa koda ɗaga kai ya kalle su,domin mutanen da yayi rayuwa dasu,ya yarda dasu,yake zaune dasu tamkar ahalin shi sune suke fadar munanan kalamar akanshi,harda wanda yake kira da dan uwa kuma yaya,Shamsuddeen,da kuma wanda ya ɗauka a matsayin Kani,Ibrahim,
Yana sauraran yanda Ammin shi ke kuka,duk kuma saboda shi.
Maijiddarh wacce tunda taji batun fasa aurenta take kuka ta matso wurin kaka,cikin kuka tace"Kaka kema kinsan ina son shi,ba zan iya rayuwa ba idan bashi,dan Allah kar ki bari a fasa wannan auren ina son shi a haka"
Jawota Aunty Atika keyi"kina da hankali kuwa,ba ki ganin abinda ke gaban ki,"ta faɗa tana nuna mata hotunan da har yanzun suke watse a tsakar falon"a haka zaki aure shi,mutum irin shi sam bai dace da zuri'ar wannan gidan ba,kuma koda kin aure shi ba fasa halin shi zai yi ba,dan haka ki dawo hankali ki"
Aunty Hajjo ce tana mikewa ta kai mata Lafiyayyen mari a fuskar ta.........
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*30*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*
Aunty Hajjo ce tana mikewa ta kai mata lafiyayyen mari a fuskarta,
Duk mai da kallo kansu suka yi,sai dai shi uban gaiyar ko inda suke bai kalla ba,sai ma lumshe idanun shi da yayi gabaɗaya,
Nuna ta tayi da ɗan yatsa"ai wannan ita ce babbar munafukar,kuma mai laifin,ta yaya ta aikata abu irin haka sannan ta zauna ba tare da tace komai ba"
Dafe kumatunta tayi da taji yana mata raɗaɗi dan wallahi har gara marin da ya mata dazu akan wannan na Aunty Hajjo dan katon hannu gare ta,
Tattara hotunan tayi ta watso mata shi a jikinta,"tunda shi dan gidan Yahudawa yaki mana bayani ke sai ki mana bayani akan waɗannan "
Hajiya Saude ce tace"kika sani ko tursasa ta yayi?
Daukar hotunan take cikin tsananin mamaki wanda ya kasa boyuwa,kallon wanda ke hannun ta yi"wannan lokacin da muka je Asibiti ne"
Da sauri Ibrahim yace"ba dai zubar da ciki ba"
Duk da halin da take ciki hakan bai hana ta hararanshi ba"tir,tir Allah ya kiyaye duk iskanci na ban taba zubar da ciki ba"
Salati yawancin mutanen falon suka saka yayin da Kaka da Ammi suke ci gaba da kuka,
"Kenan dama kun daɗe kuna iskanci?wannan karon Shamsuddeen ne ya mata tambayar,
Dago kai tayi ta kalle shi,sannan ta maida kallon ta kanshi,idanun shi a lumshe suke,sai dai fuskar nan nashi yayi ja,
Wannan ne karo na farko da taji ya bala'in bata tausayi,domin duk maganar da suke faɗi da aibantashin da suke yi bai ce masu komai ba,bai kuma ƙarya tasu ba,Ashe shi ba Asalin jikan kaka bane,kuma ba ɗan Abbu bane,to me yasa zasu mai irin wannan fahimtar lokaci ɗaya haka,
"Ke muke saurare" Ya kara faɗa,
"Ban taɓa Iskanci da shi ba,asalima babu wani abu ɗaya taba shiga tsakani na dashi sai yau,wannan hoton da kuke gani lokacin da suka raka ni Asibiti ne shida Amira duba Mama ta da bata da lafiya"
"To ya akayi ya rungume ki a hoton"
Shiru tayi kamar mai nazari,tabbas ma nazarin take yi,domin a ranar da abin ya faru taci kwaya bata cikin hankalin ta"ba zan iya tunawa ba"
"Magana ta tabbata kenan,a kwai dai abinda ya kaimu" Nuna ɗayan hoton yayi "wannan ma kamar na yau ne?
" Eh tabbas na yau ne,sai dai ba laifin sa bane,ni ce da kaina na sumbace shi ba tare da son ranshi ba"
Duka Aunty Atika takai mata"sannu manafuka uwar Karuwai,wato kare shi zaki yi,ta yaya zaki sumbace shi ba da son ranshi ba,kalli fa harda rike mata ƙwanƙwaso"
Janye ta Hajiya Rahama tayi"rufamin Asiri kar ki haɗa kashi da ita,domin irin su ba'a faɗa dasu sai su shafa maka zufan su na tsiya "
"Abu ɗaya kawai nasan zan masa na karshe a matsayina na wanda yake amsa sunan mahaifin shi,shine aura masa wannan yarinyar a yau ta yanda zai zama ishara a gare shi"cewar Abu Sufyan
Tunda aka fara maganar nan wannan ne karo na farko daya buɗe baki yayi magana" Kayi haƙuri Abbu amma ban yarda da wannan auren ba"
Salati Goggo ta saka"kai kaji min ɗan duniya,bayan ka gama ɓata masu yarinya shine zaka ce ba zaka aure ta ba,ai kuwa baka isa ba"
"Ai dama irin su haka suke,anci moriyar ganga za'a yada koren ta"
A zabure ita ma tace"wallahi ban amince ba,ni ba zan aure shi ba,"
Buge mata baki Aunty Atika tayi"munafuka yi mana shiru"
Kallon Ammi Kaka tayi"idanun ɗan ki ya buɗe sosai yanzun,har tsoron yi masa magana nake yi,dan haka ina ga ƙila ke ki nada sauran daraja a idanun shi ki masa magana ko zai amince"
Kafin tace komai sai ji suka yi yace "na amince"
Ihu ta saka "wallahi ban amince ba,ni dai ba na son shi tafiya ta ma zan yi yanzun" Ta faɗa tana ƙoƙarin mikewa,
Aunty Hajjo ta jawota kiiiii ta cillata dakin kaka ta kulle ƙofa "tunda har kwadayin ku yaja maku to sai dai ku karasa da juna"
"So nake a ɗaura auren daganan zuwa sallar Magariba,zuwa lokacin Iyayen yarinyar sun iso an masu bayani nasan idan sun ji komai ba zasu ki yarda ba"