← Book details Yar Tsanar Zinari Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 52 OF 96

Sashe 52

Yar Tsanar Zinari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"To yanzun ma da kike maganar Auren waye zai Daura mata aure bayan Ubannin ta basu nan"

"Ai Mustapha na nan shima Ubanta ne dan haka yana da damar da zai Daura mata aure"

Kaka ce ta katse su dan su Ammi ko baki basu saka masu ba balle ta fassara su wani iri,ita da Goggon yara ne kawai take yi,

"Waye mijin da zata aura?

Murmushin shakiyanci tayi" Yauwa Kaka tambayar daya kamata tun farko sumin kenan amma sun tsaya suna Challenging di na"

"Ki faɗa min abinda na tambaye ki"

"Sunan shi Yusuf,shi din shahararren ɗan kasuwa ne,yawancin kasuwancin shi a kasar waje yake yi"

"Iyayen shi fa?

" Mutanin Niger state ne"

"Menene Nasabar shi dana iyayen shi?

" Wai ni kaka duk wannan tambayoyin na menene "

"Idan ba kida duka amsar waɗannan tambayoyin to ki nimosu kafin ki zo min da batun aure domin ko ke kafin ki shigo cikin zuri'a ta sai da na tabbatar Nasan ko su waye iyayen ki da kakanin ki,dan haka bana son wata magana tashi ki fitar min a falo"

Cikin jin haushi ta tashi ta bar falon yayin da ta bar kowa da saƙar zuci.

____________*LEGOS*

Suna kammala waya da su Ammi hawa kan gado kayi ta kwanta dan tana buƙatar hutu,
Ranar yini tayi tana barci sallah da cin abinci kadai ke tayar da ita,dan ita kanta ta san idan har bata huta ba tana iya rasa hankalin ta,

*Washegari da safe*

Karfe takwas yayi mata ne a Gidan yarin domin daganan so take ta koma Hotel ɗin nan akwai binciken da zata yi a karo na karshe,

Kamar ko wani lokaci yauma haka ne yana zaune yana jiran shigowarta,

Sai da ta mai sallamah sannan ta zauna, jan kujera tayi ta zauna sannan ta buɗe jakka ta ciro takardar ta tura mashi a gaban shi "gashi ka saka hannu"

Ja yayi gaban shi ya saka hannu"idan har na fita me kike buƙata?

Shiru tayi tana kallon shi na wani lokaci,wato ma tambayar da zai mata kenan,nan take wani tunani ya zo mata,ai kuwa zata yi maganin shi,kare ma fuskar shi kallon take yi kafin ta tsayar da idanun ta akan lips din shi"kome nake bukata zaka Bani?

"In dai bai tsaba ma shari'a ba"

Murmushi ta sake tana ture jakkan ta gefe ta mike tsaye,
A hankali take takowa har ta iso in da yake zaune,
Jan kujeran da yake zaune tayi baya sannan ta zauna a saman cinyar shi ba tare da fargaban komai ba a zahiri,
Kyara zamanta tayi da kyau a saman cinyan shi,"Kace kome nake buƙata ?

Ƙoƙarin kauda kai yake yi tasa ɗan yatsan hannun ta tadawo da fuskar shi ta yanda suke fuskanta juna,
Tun daga saman goshinshi ta shiga zagayewa da ɗan yatsar hannun ta har ta gangaro izuwa cikakken giran shi,idanun shi masu matukar jan hankali,

Lumshe ido yayi yana jin yanda take yawo da yatsanta saman fuskar shi,
Gangarowa ta kuma yi saman lip dinshi inda nan ma sai da ta ɓata sakanni tana zagayeshi kafin yaji saukar nata bakin saman nashi,

Kara lumshe nashi idanun yayi,
Bata damu da yanayin da zai shiga ba ko yake ciki,ita dai abinda tayi niyar yi mai shi take kokarin aikatawa,

Dan haka kama Lip dinshi na sama tayi ta shiga tsotsa a hankali tana mai kokarin kamo harshen shi,
Bai hana ta ba sai ma dama da ya bata,
Sai da ta gamsu dan kanta sannan ta sake masa baki wanda saura kaɗan ta ciye masa shi,
Haɗe goshin su wuri ɗaya tayi ta yanda suke iya shakar numfashin juna,

Dago kai tayi ta tsura ma fuskar shi ido na wasu sakanni,duk da idanun shi a lumshe suke baka isa ka fassara a wani irin yanayi yake ciki ba,
Ta dai san duk wannan Kiss din data mai ko sau daya bai yi respond ba,bai kuma hana ta ba,

Kamar wacce aka tsikara haka ta mike ta dauki jakkan ta ba tare data ƙara kallon inda yake ba ta bar wurin.......

*Jiddarh ce* 🦚

*Yanzun aka fara*
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂

Story & Writing
By
JIDDARH UMAR

🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/

*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~

*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*

*52*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*

Tana fita daga wurin mota ta shiga ta zauna a gidan baya"muje "

"To Hajiya" Ya fada yana tayarda motar,
Ya riga ya san inda zasu je dan ta riga ta sanar dashi tun kafin su fito dan haka kai tsaye Hotel din suka nufa wanda yake da tazara sosai da in da suka baro,karin abin takaici shine yawan Goslow da hanyar,
A tafiyar da zaka yi mintuna talatin sai ka bata kusan awanni biyu zuwa uku,

Abinda ya bata haushi ya kuma ɓata mata rai shine bayan irin wannan dogon tafiyar da suka sha sai gashi masu gadin bakin Get din shiga wurin sun hana su shiga,
Ba irin rokon da bata masu ba har ta I.D card dinta ta nuna masu amma suka ki yarda wai umurni ne na Ogan su,
Ta kira Number wancan Inyamurin shi kuma bata shiga wanda daga dukkan alamu blocking din ta yayi,

Ko kusa da bakin Get din sun hana su tsayawa,dole dan nisa da Hotel din suka samu wuri suka yi parkin mota,

Fitowa tayi daga cikin motar ta jingina da jikin motar ta dafe kai,
Tunani take ta ina zata fara,komai ƙoƙari yake ya kwace mata,gashi gobe ne za'a koma kotu sai dai har yanzun komai baya iya samu ba,
Ta tabbatar ko yaya ne idan har bata samu wani abun da zata kai ba suna iya yanke mashi hukuncin da suka ga dama wanda bata fatan haka,

Ji yayi daga gefen ta ance "Hi"

Dagowa tayi ta kalli mutumin shima zubin Yarbawa gare shi,
Mai da mai da "Hi" Din shi tayi kafin tace"me kake buƙata "dan a yanda ya tsaya mata daga dukkan alamu akwai magana a bakin shi,

Kalle_kallen gefen shi yake" Zamu iya shiga motar ki muyi magana,domin ba na son a gammu tare ni ma'aikacin wannan Hotel din ne "ya faɗa yana nuna mata I.D din shi,

Cikin sauri ta buɗe mashi gidan baya" Shiga "
Sannan ta zagaya ta shiga"ya kamata mu ɗanyi nisa da nan kaɗan "

Jin abinda tace ne yasa Direban dake jiran umurninta ya tayar da motar ya bar layin dasu.

Yana parka motar a wani ɗan hanya ya fita a motar ya bar masu wuri,

"Ma,Suna na Josif, ni ma'aikaci ne a wannan Hotel ɗin,tun wannan ranar da kika fara zuwa wurin Manager mu na ganki,naso na maki magana amma ban samu dama ba kuma ina jin tsoron a ganni dake dan amma gargaɗi sosai akan ki,sai dai kuma yau ma na ga an hana ki shiga shi yasa nace bari nayi amfani da wannan damar domin ba zan taba manta taimakon da wanda kike karewa yayi min ba,a lokacin da kowa ya juya min baya na rasa yanda zan yi,shine ya taimake ni ba tare daya duba yare na ko Addini na ba wanda gashi har ta sanadin haka na buɗe ma Mama na shago ta na sayar da kaya a ƙofar gida tana samun kuɗin abinci ba tare data jira ni ba ko taci bashi,"

Ita dai sauraren shi take yi tana kuma mamakin wani taimako ne ya mai haka,

"Ranar da abin ya faru ina kicin ina aiki sai gashi Manager ya kira akai mai abinci shida baƙi a Ofishin shi,
Ko da na shiga kai abincin suna ta cikin dakin hutawar shi dake cikin Ofishin,har zan juya naji daya daga cikin su yana daɗin Tunda mun samu ya fita daga dakin ya kamata ka saka a hanzarta a shigar da Gawar yarinyar dakin shi ta yanda komai zai yi dai daidai,
Jin wannan maganar ne yasa da sauri na ciro wayata na shiga wurin kwasar Video da daukar murya na labe ina ta kwasar su har suka kammala tsara shirin su,
Jin za'a fito ne yasa da sauri na fita,
Sai dai ban koma wurin aiki na ba na labe a ta bayan kofar baya da naji ta nan za'a shigo da gawar,
Sai da na tabbatar na kwashe komai sannan na wuce,sai dai a lokacin ban cewa ɗakin shi aka saka gawar ba,kuma ni ma dalilin da yasa na ɗauka saboda ina son idan na koma gida na kira Manager na masa barazana da wannan Video na samu kudin bikin binne kanwata data mutu,
Ana cikin haka sai ga kiran Mom din mu tana faɗi min irin munanan kalaman mutane ƙauyen mu a kanmu,wanda sai da nayi kuka,
A wannan lokacin ne Allah ya haɗa mu da shi yaji kukan da nake yi shine ya tambaye ni akan meke damuna,dana faɗa mashi nan take ya amsa account din na ya turamin dubu dari da hamsin,
Shi yasa da na ga abinda ya faru dashi ban tura ma Manager Video ba na ajiye domin na san zai taimake shi wurin fitowa"ya faɗa yana mika mata Memory,

Tsabar farin ciki ji tayi kamar ta rungume mutumin sai godiya take tayi mai kafin ya fita yayi wucewar shi,

Direban ne ya shigo motar"ina zamu Hajiya?

"Gida" Ta bashi amsa fuskarta dauke da murmushi.

Ranar haka tayi ni cikin tsananin farin ciki domin ta san Allah ne ya kawo mata sauƙi har in da take,jira kawai take gode tayi a shiga kotu.

____________*Washegari*

Ƙarfe tara na safe tayi mata ne a cikin kotu dan ma tun ƙarfe bakwai suka fito,to amma saboda yanayi na cikowar abin hawa shi yasa basu iso da wuri ba,

Ko da ta isa a haraban babban Kotun ta samu su Pa da Abbu sai Dady,
Cikin girmamawa ta gaishe su,suka amsa,

Dady ne yace"ƴa ta da fatan an samu wani abun,dan gaba ɗaya hankalin mu a tashe yake yau bamusan yanda shari'ar zata kasance ba"
Chapter 52 · 0% Book details