Sashe 90
Yar Tsanar Zinari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kallon mamaki yake mata,da jin irin kalaman dake fitowa daga bakin ta,yanzun har shi Suraj zata faɗa ma haka,har shi zata kalli idon shi tace saboda jikinta yake tare da ita,tana kuma mashi kallon daya daga cikin mutanen da suka amfana da jikin ta,
Ba tare da yace komai ba ya sauka daga saman gadon ya nufi ban ɗaki,ya jima sosai a ciki dan har ta gaji da jiranshi ta zuba abinci ta ci bai fito ba,
Yana fitowa kuma bai kalli in da take ba ya fita,babu jimawa kuna sai ga shi ya shigo da leda babban a hannu,ajiyewa yayi saman gado,fuskarshi a cunkushe take yanda baka isa ka shaida yanayin da yake ciki ba,sai dai idanun shi da suka yi wani iri,
"Ga kaya nan ki saka,idan kin kammala ki same ni a falo,zan mai da ke gida"
"Na gode"
"Umm" Ya fada yana barin ɗakin.......
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*89*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*
Tana kammala shiryawa ta fito,a falon ta same shi yana amsa waya,zama tayi a gefen shi har ya kammala,
Juyowa yayi fuskar shi dauke da dan murmushi "muje ko?
Jinjina nashi kai tayi tana mikewa,
Tare suka jero hannun shi na zube cikin aljihun wandon shi,
Idan ka kallesu yanda suke taku a hankali yanda kasan wata da zara,sun bala'in dacewa da juna,
" Akwai in da ke miki ciyo ne?
Kallon shi tayj"Umm um,naji sauki yanzun sosai "
Ajiyar zuciya ya sauke "that is good"
Buɗe mata gidan gaba yayi ta shiga sannan ya zagaya ya zauna a mazaunin direba,
A hankali yake tuka motar ba tare da gudu ko garaje ba,"Kasan gidan mu ne?
Ba tare da ya kalli in da take ba yace "um"
Jin haka yasa ta ja bakinta tayi shiru,dan ta fahimce ƴan miskilancin suna kusa,
Cikin kankanin lokaci sai gasu a bakin Get din gidan su,mai gadi na ganin shi ya buɗe masu Get suka shiga,
Tare suka fito sai dai ita gaba tayi ganin ya tsaya da Yaya Abdulmajid suna gaisawa,
Tana shiga falo Turus ta tsaya ganin mutanen da bata taba tsammanin gani ba,wato yan Group din Yar Tsanar Zinari Fans group,
Da gudu ta karasa ta rungume Ummunas tana fashewa da kuka,ita ma rungume ta tayi tana shafa bayan ta,cikin taushin murya ta shiga lallashin ta tana mata nasiha "ni ba zan hana ki kuka ba,domin duk wanda kaji yace yi ma mamaci kuka babu kyau to bai rasa wani mukusanci nashi bane,abinda kawai ba a so shine yin na fitar kima,kiyi haƙuri wannan wata jarabawa ce data same ki,kuma muna maki fatan zaki cinye ta"
Dagowa tayi daga jikin ta tana share hawaye,"Addu'ar ki shi suka fi bukatar a yanzun"cewar Ummuhaidar,
"Gaskiya ne komai yayi zafi addu'a ne magani,ki duba ki ga dukkan mu saboda ke muka zo nan" Cewar Bareerah Umar,
"kalli ga Salma,ga DeejAysh,ga Ummu husna,kin ga harda Rx_Aryamn tana nan,duk da aiyukan da suke dashi haka suka ajiye domin ke saboda suzo su sanyaya zuciyar ki,"
Murmushi mai dauke da hawaye ne suka sauko mata,"Ummunas banga Salmancy da A.I Bauchi da Fatety ba,ko dai basu samu zuwa bane?
"Sun zo,ina ga suna waje suna magana da Suraj ne dan sunce shima ya cancanci gaisuwa"
Sallamar da suka ji ya saka su juyawa,fara'ar fuskokin su ne ya karu ganin tawagar Kungiyar Moonlight writers,wato kungiyar su na Marubuta tare da yan fans group dinsu,
Queen Nasma ce a gaba,domin ita ce shugaba kuma jagoran wannan kungiyar mai Albarka,wanda ya hada manya kuma haziƙan marubata,
Cikin girmamawa da mutunta juna aka shiga gaisawa tare da musayar ta'aziyya,
Ko gama zama ba su yiba sai ga sallamar yan Fans group din FAKIRI yayin da shugaban su Khadijah Umar ta jagorance ce,tare suke da Fans din Sardauna,Allah sarki ƴan Amana,
Wannan zuwan nasu ba karamin farin ciki da daɗi ya mata ba,domin mutane ne da suka zo daga mabanbanta yanki a fadin kasar,har ma da wajen kasar,kuma duk saboda ita suka zo,gaskiya in bata gode ma Allah ba bata san Me zata yi ba,
Aunty Fati Uwar Abulkhairi ita ta fara lura da babu Uwar mijin ta,dan haka mikewa tayi tana dan lekawa tare da fadin"wai jama'a ina Jiddarh Umar?
Daga bakin kofa suka ji ta amsa da "gani nan"
Masha Allah kake jin yana fitowa daga bakin mutane,domin sanye take cikin leshi dinkin doguwar riga na bubu wanda ba karamin kyau ya mata ba,gata dama doguwa mai dogon gashi har gadon baya,ga dogon hanci har baki,ido farare tamkar madara,dan ko Biba da take mace sai da ta juya ta kara kallon ta tsabar kyau yanda kasan ba a duniyar mutane ba,kamar dai a duniyar Novel (ni ma na ɗana,ehe basu Biba kadai suke da kyau ba😜)
Cikin tsananin farin ciki ta kara so ta rungume Biba tare da mata gaisuwar rasuwa,sannan cikin girmamawa ta gaida shugaban kungiyoyi da manyan su,
Abinci lafiyayye Biba ta saka aka kawo masu,cikin har da su farfesun kaji da kayan shaye-shaye kala_kala,
Dukkan su kowa yana ji da kanshi domin mutane ne masu aji da class,
Nikam ganin basu da niyar taba komai ne yasa na juya na kalli Maman Abu,"Sirika idan zaki ci Bismillah idan kuma zaki tsaya yanga ni dai na yi nan"kafin su ankara sai ganin Jiddarh Umar suka yi ta zauna tare da takwashe kafa tashiga buɗe plate,duk wanda ya mata shi take jawowa gaban ta,
Ganin da gaske ci take hankali kwance ya saka masu sha'awar ci suma suka fara ci,
Queen ce ta danja gefen mayafin ta "Jiddarh"
Juyowa nayi"umm "domin ba zan iya amsawa ba saboda baki na cike yake da namar kaza,
" Me haka,dan Allah karki bada ƴan Moonligh mana"
'Gaskiya sai dai kiyi haƙuri Queen,ba zan iya ma kai na bakin ciki ba,haka kawai kana kallon abu kana son ci sai ka tsaye kana hadiye miyau saboda wani abu wai shi aji,gaskiya ni dai in kan abinci ne ba ni da aji,domin duk in da naje aka ba ni in har yamin zan ci ne,babu ruwa na ehe "
"Dama nasan you ar very Stoburn"
Tura baki nayi na ci gaba da kwasan girki na,
Rx_Aryamn ce tace"Jiddarh ki bar naman nan haka,kin san ba lafiyar kirji gare ki ba,kuma likita ya hana ki cin soyayyen abu,salon ki ci yanzun an jima ki kama nishi da faɗin zaki mutu"
"Ai sai dai ki yi hakuri likita,domin rayuwa bashi yuwa sai da soyayyen abu,ta yaya za'ayi in gani in kyale,gaskiya ci zan yi idan ciyo ya taso a sha magana asha wahala,idan an warke a ɗaura daga in da aka tsaya"
"To karma dai ki nime ni anjima idan abun naki ya motsa"
Sahibar Moonlight ce ta katse mu ta hanyar fadin "jiddarh naji ance ke yar Kano ce?
" A'a ni ba yar Kano ba ce,ni yar Niger state ce"
"Niger?
" Ni fa bance Niger ba,ina nufin Niger State a garin Minna "
"Wow abun mamaki,wai dama a Minna a kwai marubuta?
" Akwai mana,ban san me yasa mutane wani bi suke raina baiwar da Allah yama dan adam ba,sau da yawa sai kiga mutane suna fadin ai gabaɗaya marubuta a Kano suke,alhalin basu san a garin da suke ma akwai ba,dan haka nake Alfaharin kasancewata yar Niger state "
Murmushi ne dauke a fuskar su "gaskiya ne Jiddarh,yanzun dai tunda kin gama ya kamata a kira mana Ammi da Aunty Hulaira mu masu gaisuwa,daganan sai mu fita mu ma Suraj shima gaisuwa"
"Haka ne" Duk suka amsa,
Ammi ma ta ji dadin zuwan su sosai dan malama Amina Jibrin ta group din Fakiri ita ta bayar da Addu'a sosai tare da wa'azi mai ratsa jiki,
A waje ma gaisuwa suka ma Suraj da su Ya Abdulmalik,har bakin Get Biba ta raka su kafin ta dawo,
Ganin ta wuce ne Salmancy ta kalle mu"ni kuwa sai nake ganin kamar a kwai damuwa a idanun Suraj,ko baku lura da haka ba?
"Ke dai Salmancy Allah ya shirye ki,baki iya gani ki yi shiru" Cewar Bareera Umar,
"Allah da gaske nake ji"
Girgiza kai Ummunas tayi,bata dai ce masu komai ba ita da Ummuhaidar,
"DeejAysh baku gani ba?
Busar da iska tayi ta baki" Ta ya za'ayi in gani bayan hankalina yana kan kallon baiwar kyan da Allah ya mashi"
"Kuka sani ko damuwar mutuwar ce har yanzun a ran shi" Cewar fatity,
"To me zai hana mu tambaye Jiddarh Umar"
"Dadi na dake kanki na ja Salma" Ummuhusna ta fada,
Jawo ni baya suka yi "faɗa mana meke damun Young Ustaz ne haka?
Kallon su take ita ma kamar yanda suka zuba mata ido,dan har dariya sun so bata" To ta yaya zan sani,kawai dai ku jira ku gani koma dai meke damun shi ai da kanshi zai faɗa ko,ni ta yaya ma za'a yi in sani"
"Saboda ke ce Alkalin wasan"
Gira daya na daga,"a naku ganin ba,ni kuma a nawa bangaren hannu na shine Alkalin wasan,domin ban isa yanke hukunci ba sai lokacin da nake kan buga wasan,ma'ana sai lokacin dana dauki waya,dan haka mu jira mu gani,Allah sarki gaskiya Biba ta ban tausayi "
Karamin tsaki sis Khadijah taja"ai ke kika sani,ni kunga tafiya ta ga Baban Hamnat can ya zo daukata "
Sallamah suka mata ta wuce,
A takaice dai da dai_daiya matan auren mazajen su ke ta zuwa suna ɗaukar su har ya rage daga ni sai Fatity,
Ganin yanda ta yi shiru be yasa na dafa ta"ya dai mutuniyar"
"Jiddarh aure zan yi"
Ba karamin dariya maganar ta ya ba ni ba,ai kuwa sai da na dara"me yasa sai yanzun?
Kafin ta ba ni amsa ne sai ga kiran Sultan di na ya shigo waya,dan haka ba tare dana saurare ta ba na daga mata hannu ina daukau wayar tare da shigewa cikin Adaidaita sahun dana tare,
Murmushi tayi itama tana ɗaga min hannu........
Ba tare da yace komai ba ya sauka daga saman gadon ya nufi ban ɗaki,ya jima sosai a ciki dan har ta gaji da jiranshi ta zuba abinci ta ci bai fito ba,
Yana fitowa kuma bai kalli in da take ba ya fita,babu jimawa kuna sai ga shi ya shigo da leda babban a hannu,ajiyewa yayi saman gado,fuskarshi a cunkushe take yanda baka isa ka shaida yanayin da yake ciki ba,sai dai idanun shi da suka yi wani iri,
"Ga kaya nan ki saka,idan kin kammala ki same ni a falo,zan mai da ke gida"
"Na gode"
"Umm" Ya fada yana barin ɗakin.......
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*89*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*
Tana kammala shiryawa ta fito,a falon ta same shi yana amsa waya,zama tayi a gefen shi har ya kammala,
Juyowa yayi fuskar shi dauke da dan murmushi "muje ko?
Jinjina nashi kai tayi tana mikewa,
Tare suka jero hannun shi na zube cikin aljihun wandon shi,
Idan ka kallesu yanda suke taku a hankali yanda kasan wata da zara,sun bala'in dacewa da juna,
" Akwai in da ke miki ciyo ne?
Kallon shi tayj"Umm um,naji sauki yanzun sosai "
Ajiyar zuciya ya sauke "that is good"
Buɗe mata gidan gaba yayi ta shiga sannan ya zagaya ya zauna a mazaunin direba,
A hankali yake tuka motar ba tare da gudu ko garaje ba,"Kasan gidan mu ne?
Ba tare da ya kalli in da take ba yace "um"
Jin haka yasa ta ja bakinta tayi shiru,dan ta fahimce ƴan miskilancin suna kusa,
Cikin kankanin lokaci sai gasu a bakin Get din gidan su,mai gadi na ganin shi ya buɗe masu Get suka shiga,
Tare suka fito sai dai ita gaba tayi ganin ya tsaya da Yaya Abdulmajid suna gaisawa,
Tana shiga falo Turus ta tsaya ganin mutanen da bata taba tsammanin gani ba,wato yan Group din Yar Tsanar Zinari Fans group,
Da gudu ta karasa ta rungume Ummunas tana fashewa da kuka,ita ma rungume ta tayi tana shafa bayan ta,cikin taushin murya ta shiga lallashin ta tana mata nasiha "ni ba zan hana ki kuka ba,domin duk wanda kaji yace yi ma mamaci kuka babu kyau to bai rasa wani mukusanci nashi bane,abinda kawai ba a so shine yin na fitar kima,kiyi haƙuri wannan wata jarabawa ce data same ki,kuma muna maki fatan zaki cinye ta"
Dagowa tayi daga jikin ta tana share hawaye,"Addu'ar ki shi suka fi bukatar a yanzun"cewar Ummuhaidar,
"Gaskiya ne komai yayi zafi addu'a ne magani,ki duba ki ga dukkan mu saboda ke muka zo nan" Cewar Bareerah Umar,
"kalli ga Salma,ga DeejAysh,ga Ummu husna,kin ga harda Rx_Aryamn tana nan,duk da aiyukan da suke dashi haka suka ajiye domin ke saboda suzo su sanyaya zuciyar ki,"
Murmushi mai dauke da hawaye ne suka sauko mata,"Ummunas banga Salmancy da A.I Bauchi da Fatety ba,ko dai basu samu zuwa bane?
"Sun zo,ina ga suna waje suna magana da Suraj ne dan sunce shima ya cancanci gaisuwa"
Sallamar da suka ji ya saka su juyawa,fara'ar fuskokin su ne ya karu ganin tawagar Kungiyar Moonlight writers,wato kungiyar su na Marubuta tare da yan fans group dinsu,
Queen Nasma ce a gaba,domin ita ce shugaba kuma jagoran wannan kungiyar mai Albarka,wanda ya hada manya kuma haziƙan marubata,
Cikin girmamawa da mutunta juna aka shiga gaisawa tare da musayar ta'aziyya,
Ko gama zama ba su yiba sai ga sallamar yan Fans group din FAKIRI yayin da shugaban su Khadijah Umar ta jagorance ce,tare suke da Fans din Sardauna,Allah sarki ƴan Amana,
Wannan zuwan nasu ba karamin farin ciki da daɗi ya mata ba,domin mutane ne da suka zo daga mabanbanta yanki a fadin kasar,har ma da wajen kasar,kuma duk saboda ita suka zo,gaskiya in bata gode ma Allah ba bata san Me zata yi ba,
Aunty Fati Uwar Abulkhairi ita ta fara lura da babu Uwar mijin ta,dan haka mikewa tayi tana dan lekawa tare da fadin"wai jama'a ina Jiddarh Umar?
Daga bakin kofa suka ji ta amsa da "gani nan"
Masha Allah kake jin yana fitowa daga bakin mutane,domin sanye take cikin leshi dinkin doguwar riga na bubu wanda ba karamin kyau ya mata ba,gata dama doguwa mai dogon gashi har gadon baya,ga dogon hanci har baki,ido farare tamkar madara,dan ko Biba da take mace sai da ta juya ta kara kallon ta tsabar kyau yanda kasan ba a duniyar mutane ba,kamar dai a duniyar Novel (ni ma na ɗana,ehe basu Biba kadai suke da kyau ba😜)
Cikin tsananin farin ciki ta kara so ta rungume Biba tare da mata gaisuwar rasuwa,sannan cikin girmamawa ta gaida shugaban kungiyoyi da manyan su,
Abinci lafiyayye Biba ta saka aka kawo masu,cikin har da su farfesun kaji da kayan shaye-shaye kala_kala,
Dukkan su kowa yana ji da kanshi domin mutane ne masu aji da class,
Nikam ganin basu da niyar taba komai ne yasa na juya na kalli Maman Abu,"Sirika idan zaki ci Bismillah idan kuma zaki tsaya yanga ni dai na yi nan"kafin su ankara sai ganin Jiddarh Umar suka yi ta zauna tare da takwashe kafa tashiga buɗe plate,duk wanda ya mata shi take jawowa gaban ta,
Ganin da gaske ci take hankali kwance ya saka masu sha'awar ci suma suka fara ci,
Queen ce ta danja gefen mayafin ta "Jiddarh"
Juyowa nayi"umm "domin ba zan iya amsawa ba saboda baki na cike yake da namar kaza,
" Me haka,dan Allah karki bada ƴan Moonligh mana"
'Gaskiya sai dai kiyi haƙuri Queen,ba zan iya ma kai na bakin ciki ba,haka kawai kana kallon abu kana son ci sai ka tsaye kana hadiye miyau saboda wani abu wai shi aji,gaskiya ni dai in kan abinci ne ba ni da aji,domin duk in da naje aka ba ni in har yamin zan ci ne,babu ruwa na ehe "
"Dama nasan you ar very Stoburn"
Tura baki nayi na ci gaba da kwasan girki na,
Rx_Aryamn ce tace"Jiddarh ki bar naman nan haka,kin san ba lafiyar kirji gare ki ba,kuma likita ya hana ki cin soyayyen abu,salon ki ci yanzun an jima ki kama nishi da faɗin zaki mutu"
"Ai sai dai ki yi hakuri likita,domin rayuwa bashi yuwa sai da soyayyen abu,ta yaya za'ayi in gani in kyale,gaskiya ci zan yi idan ciyo ya taso a sha magana asha wahala,idan an warke a ɗaura daga in da aka tsaya"
"To karma dai ki nime ni anjima idan abun naki ya motsa"
Sahibar Moonlight ce ta katse mu ta hanyar fadin "jiddarh naji ance ke yar Kano ce?
" A'a ni ba yar Kano ba ce,ni yar Niger state ce"
"Niger?
" Ni fa bance Niger ba,ina nufin Niger State a garin Minna "
"Wow abun mamaki,wai dama a Minna a kwai marubuta?
" Akwai mana,ban san me yasa mutane wani bi suke raina baiwar da Allah yama dan adam ba,sau da yawa sai kiga mutane suna fadin ai gabaɗaya marubuta a Kano suke,alhalin basu san a garin da suke ma akwai ba,dan haka nake Alfaharin kasancewata yar Niger state "
Murmushi ne dauke a fuskar su "gaskiya ne Jiddarh,yanzun dai tunda kin gama ya kamata a kira mana Ammi da Aunty Hulaira mu masu gaisuwa,daganan sai mu fita mu ma Suraj shima gaisuwa"
"Haka ne" Duk suka amsa,
Ammi ma ta ji dadin zuwan su sosai dan malama Amina Jibrin ta group din Fakiri ita ta bayar da Addu'a sosai tare da wa'azi mai ratsa jiki,
A waje ma gaisuwa suka ma Suraj da su Ya Abdulmalik,har bakin Get Biba ta raka su kafin ta dawo,
Ganin ta wuce ne Salmancy ta kalle mu"ni kuwa sai nake ganin kamar a kwai damuwa a idanun Suraj,ko baku lura da haka ba?
"Ke dai Salmancy Allah ya shirye ki,baki iya gani ki yi shiru" Cewar Bareera Umar,
"Allah da gaske nake ji"
Girgiza kai Ummunas tayi,bata dai ce masu komai ba ita da Ummuhaidar,
"DeejAysh baku gani ba?
Busar da iska tayi ta baki" Ta ya za'ayi in gani bayan hankalina yana kan kallon baiwar kyan da Allah ya mashi"
"Kuka sani ko damuwar mutuwar ce har yanzun a ran shi" Cewar fatity,
"To me zai hana mu tambaye Jiddarh Umar"
"Dadi na dake kanki na ja Salma" Ummuhusna ta fada,
Jawo ni baya suka yi "faɗa mana meke damun Young Ustaz ne haka?
Kallon su take ita ma kamar yanda suka zuba mata ido,dan har dariya sun so bata" To ta yaya zan sani,kawai dai ku jira ku gani koma dai meke damun shi ai da kanshi zai faɗa ko,ni ta yaya ma za'a yi in sani"
"Saboda ke ce Alkalin wasan"
Gira daya na daga,"a naku ganin ba,ni kuma a nawa bangaren hannu na shine Alkalin wasan,domin ban isa yanke hukunci ba sai lokacin da nake kan buga wasan,ma'ana sai lokacin dana dauki waya,dan haka mu jira mu gani,Allah sarki gaskiya Biba ta ban tausayi "
Karamin tsaki sis Khadijah taja"ai ke kika sani,ni kunga tafiya ta ga Baban Hamnat can ya zo daukata "
Sallamah suka mata ta wuce,
A takaice dai da dai_daiya matan auren mazajen su ke ta zuwa suna ɗaukar su har ya rage daga ni sai Fatity,
Ganin yanda ta yi shiru be yasa na dafa ta"ya dai mutuniyar"
"Jiddarh aure zan yi"
Ba karamin dariya maganar ta ya ba ni ba,ai kuwa sai da na dara"me yasa sai yanzun?
Kafin ta ba ni amsa ne sai ga kiran Sultan di na ya shigo waya,dan haka ba tare dana saurare ta ba na daga mata hannu ina daukau wayar tare da shigewa cikin Adaidaita sahun dana tare,
Murmushi tayi itama tana ɗaga min hannu........