Sashe 79
Yar Tsanar Zinari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da zasu tafi ta rako su har bakin falo,duk da sun so tayi zamanta saboda ƙafar ta,
Sawa tayi Nafisa ta kai su shiyan Ammi,
Nan ma sai da akai masu iso sannan suka shiga,ita sai lokacin ma ta san cewar Salma na gidan,
Basu wani jima a shiyan ba suka tashi zasu tafi,bayan Ammi ta masu Alkawarin zuwa har gida idan Suraj ya kammala abinda yake yi zasu taho tare da Biba,
"Bari na kira naku ita kuyi sallamah"
"A'a Ammi ki bar ta domin wani rigimar zata saka"
"To shikenan" Ita ma ta rakasu bayan Alkhairin data masu sosai ga kuma na Kaka da suka samu shima,gaskiya hankalin su ya kwanta sosai da mutanen.
Bayan tafiyar su ne Ammi ta nufi kofar dakin ta,ƙwanƙwasawa ta shiga yi a hankali tana kiran sunan ta,
Jin muryar Ammi ne yasa dole ta taso tazo ta buɗe ƙofar tana kauda kanta gefe,dan bata son Ammi taga waɗannan kumburarrun idanun,
Murmushi tayi tana karasa shiga tare da zama a gefen gado,nuna mata kusa da ita tayi"zo ki zauna"
A hankali take takowa kanta a kasa dan Allah ya gani tana girmama matar kuma kunyar ta take ji,
A maimakon zama saman gadon in da ta nuna mata sai zaunawa tayi a kasa kusa da ƙafafunta,cikin sanyin murya tace"Ammi ina wuni"
"Lafiya qlau Salma ya jikin naki"
"Da sauƙi" Ta faɗa tana share hawayen da yaki tsayawa,
"Har yanzun kukan ne?
Ita dai shiru tayi bata bata amsa ba,
Hannun ta tari ko cikin nata,cikin kwantar da murya irin na wanda ake rarrashi ta shiga yi mata nasiha mai ratsa jiki,akan Kaddara da kuma yarda da ita" Kaddara wata aba ce da Ubangiji ke Daura ma bawa domin ya gwada karfin imanin shi,Salma duk wani bawa mai imani da zaki gani a ɗoron duniya tabbas yana fuskantar tashi ƙaddarar,wani za'a jarabce shine ta hanyar Ya'yan shi,wasu ta Matan shi,wasu kuma ta yan uwa ko ya'yan yan'uwa ko kuma miji,
Duka dame zamu kira shi?kaddara wanda muke fatan mu cinye ta hanya mai kyau,
Ke Allah ya jarabce kine ta hanyoyi uku,na faro mijin ki,na biyu mahaifinki,na uku kuma mahaifiyar ki,amma sai gashi a lokacin daya kin manta da Allah da ya jarabce ki yana sane dake ba kuma ya manta dake bane,kin zabi hanyar saba mashi,a maimakon komawa gare shi,kin manta cewar duk in da kika je kika dawo dole wurin shi zaki koma in da yake jiran ki a madaka domin amsa tambayoyi,kin yi zina,me zaki ce masa akan haka Salma,idan da ace a wancan ranar kin mutu ba tare da kin tuba ba me zaki ce masa Salma?
Lallai Allah yana son ki da rahama da har ya nufe ki da tashi ba tare da kin samu wani nakaso ba,wannan na nuna wata dama ce da Ubangiji ya kara baki domin ganin kin share wannan kuskuren da kika aikata,shin me zaki yi game da haka?
Ina mai baki shawara da ki yi gaggawar watsar da komai ki fuskanci rayuwarki,ki kuma ga Allah ki nime yafiyar shi,domin shi gwanine a fagen yafiya,ki dage da yin istigfari ina ganin hakan zai fi idan har kika karɓi kaddara ki da hannu biyu"
Tunda Ammi ta fara magana take kuka tana kuma auna kuraruran ta da lafukanta,
Rungume Ammin tayi tana ci gaba da kuka"tabbas na aikata laifi mai tarin yawa wanda na aikata cikin sani ba cikin rashin sani ba,domin rufewar ido dana zuciya,ina ganin tamkar babu wani wanda yake cikin kuncin rayuwa sama dani,shin kina ganin idan na nime yafiyar Allah zai yafe min?
"Me zai hana,ai shi Allah mai yin gafara ne,dan haka zai gafarta maki,ke dai kawai ki tsarkake zuciyar ki,ki kuma tabbatar ba zaki ƙara komama zunu banki ba"
"Nayi Alkawari Ammi,in sha Allah daga yau na cire komai a raina,sai dai kuma VIP,ba lallai bane ya barni,sannan Suraj....
Yatsa ta saka mata a baki," Karki damu da wannan domin Suraj zai ji da komai"
"Ta yaya aka yi kuka san da batun VIP Ammi,naga shima Suraj yawancin abubuwa baya mamaki a kansu,sannan dama kin san da aikin da ya kawo ni gidan nan tun farko me yasa kika amshe ni?sannan ya akayi kika sani?
Murmushi mai ciyo a saki,wanda iyakar shi fatan bakin ta,
" Abu ne da aka fara shekaru goma sha ɗaya data wuce,har i zuwa yau,kin ga mu ba abin mamaki bane a gare mu,har balle kamar yanda suke tunanin sun san ko wani motsi na mu,to muma kusan haka ne,duk da ba duka ba,
Tun kafin zuwan ki wannan gidan nasan da batun turo ki,a lokacin da suke niman har yar shigo dake cikin gidan a lokaci na basu hanya ta hanyar zubar da man gyada na zame har samu targade a kafa,ta hakan ne suka samu damar shigo dake,
Sun saka kina masu aiki cikin duhu ba tare da sun san ta gefe ɗaya muna muna amfani dake ba,nasan ba zaki manta wanda ya kiraki yake shaida maki ki yi maza ki bar Legas ki koma Abuja domin rayuwar Ummita na a cikin hatsari,tabbas shima yaron mijin ki ne,wanda yake bibiyar dum wani motsi nasu har ma da naki,
Sannan shi karan kanshi wanda yake saka ki aiki da sunan VIP,da kuma mutanen dake zagaye dashi dukansu yanzun a tafin hannun mu suke,Domin yanzun Kaka ta farka,dama ita ce cikon shaidar mu,kuma ta tashi,"
Tunda Ammi ta fara magana ta kafe ta da ido,cikin tsananin mamaki,wato a cikin wannan wasan dai ita ce katin wasan da kowa ke bugawa yanda yaga dama ba tare da sanin ta ba,"da yaushe ta tashi"
"Ranar da za'a maki aiki,yanzun haka mijin ki na can"
Lumshe ido tayi ta buɗe "baki bani amsar yanda akayi kija sanni ba,har kome dan gane dani,ina son sanin komai"
"Zaki sani sai dai ba yanzun ba,amma na maki Alƙawarin zan warware maki komai a gaban mahaifiyar ki,a lokacin da muka haɗu,sannan nan da kwana Takwas da za'a shiga ƙoto domin Kaka ta shigar da kara a yanzun haka,amma a London za'a yi shari'ar domin a can komai ya faro"
"Amma an kama su ne?
" Ummm to wannan dai yana hannun mijin ki,sai yanda ya tsara,amma a nasu bangaren basu san yasan komai ba"
"Ammi please waye VIP" Ta tambaya tana tsare ta da ido,
Girgiza mata kai tayi"bana ce ba,amma mu jira har zuwa lokacin da za'a shiga kotu,da idanun ki zaki ga ko ma waye,dan idan na faɗa maki ba lallai ki iya yarda ba"
Tana shirin ƙara jeho mata wani tambayar ta Daura mata yatsa a baki"shiiii no more question,sannan da zaran kome ya kare zamu mai da ke gida,sai dai ina son in zaki koma ki koma cikin mutunci da kyawun gani,dan haka zuwa anjima zamu fara kyaran jikin ki"tana gama fadar haka ta tashi ta fita tana kara jawo mata ƙofa,
Gabaɗaya zuciyarta bata mata daɗi,wato a wannan wasan ita ce a tsakiya,kuma a duhu,amfani dukan su biyu suka yi da ita wurin cin ma burin su harda Suraj,wato tun farko yasan komai,gashi sanadin wannan wasan nasu Ummita ta rasa rayuwar ta har abada,ita ma kuma Allah ne yayi da sauran shan ruwan ta a duniya,da yanzun kuma ba wannan labarin ake yi ba,ita ce babbar mai asara a cikin su,domin ta baro gidan su da komai nata,ta kuma zabe hanyar da take ganin zai fi mata sauki bata san rami take tura kanta ba,
Amma babu komai ko yanzun ta koyi darasi a kan wannan aikin,dan haka zata bi shawarar Ammi ta koma ga Allah da niman tuba,sannan da an gama wannan shari'ar zata koma gida taci gaba da rayuwar ta cikin yannin ta da iyayenta,zata manta da komai ta fara gina sabuwar rayuwar ta,
Da wannan tunanin ta tsayar da zuciyar ta wuri ɗaya.......
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*80*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*
Da Sallamah ta shigo dakin hannun ta rike da tiren kuloli,ajiyewa tayi a gefe ba tare data ce mata komai ba,ita ma din dai tana zaune ne a in da Ammi ta barta tun dazu,
Ganin har tana shirin fita bata dago ta kalle ta ba yasa ta ɗan dakata"ya jikin naki?
Kara kauda kai tayi tana kwantar dashi saman gado "da sauki"
"Allah ƙara lafiya" Ta faɗa tana fita,ita a da bata son Biba ko kadan tunda ta aure yayan ta,kuma ba tada ilimi,sai gashi cikin lokaci ƙanƙani ta shayar dasu mamaki,ashe da gaskiyar hausawa da suke cewa duk yanda kake ganin mutum karka taba raina shi saboda baka San irin baiwar da Allah ya mai ba.
Bata maci abincin ba sai da tayi barci ta tashi,sannan ta watsa ruwa,ganin lokacin sallah la'asar yayi ne yasa ta dauro Alwallah tayi sallah,ko da ta idar zaman yin istigfari tayi,har kusan ƙarfe biyar da wani abu,sannan ta shafa addu'a ta tashi,dan sau biyu Ammi na aikowa a leko ko ta gama,sai da ta ci abinci sannan ta fita,ganin bata falo ne yasa ta nufe dakin ta,
Sallamah ta yi,daga ciki aka amsa tare da tambayar"Biba ce"
"Eh ni ce"
"Shigo"
Shigowa tayi,nuna mata kan kushin tayi "zauna"
Zaunawa tayu tana kare ma dakin kallo wanda yake a kyare tsaf a ko wani lokaci,ga kamshe mai ni'ima da ke tashi,domin Ammi macece mai matukar tsafta da son kamshi,
Wani dan karamin jakka ta dauko ta zauna kusa da ita tana fito da kayan dake cikin jakkan,
Sawa tayi Nafisa ta kai su shiyan Ammi,
Nan ma sai da akai masu iso sannan suka shiga,ita sai lokacin ma ta san cewar Salma na gidan,
Basu wani jima a shiyan ba suka tashi zasu tafi,bayan Ammi ta masu Alkawarin zuwa har gida idan Suraj ya kammala abinda yake yi zasu taho tare da Biba,
"Bari na kira naku ita kuyi sallamah"
"A'a Ammi ki bar ta domin wani rigimar zata saka"
"To shikenan" Ita ma ta rakasu bayan Alkhairin data masu sosai ga kuma na Kaka da suka samu shima,gaskiya hankalin su ya kwanta sosai da mutanen.
Bayan tafiyar su ne Ammi ta nufi kofar dakin ta,ƙwanƙwasawa ta shiga yi a hankali tana kiran sunan ta,
Jin muryar Ammi ne yasa dole ta taso tazo ta buɗe ƙofar tana kauda kanta gefe,dan bata son Ammi taga waɗannan kumburarrun idanun,
Murmushi tayi tana karasa shiga tare da zama a gefen gado,nuna mata kusa da ita tayi"zo ki zauna"
A hankali take takowa kanta a kasa dan Allah ya gani tana girmama matar kuma kunyar ta take ji,
A maimakon zama saman gadon in da ta nuna mata sai zaunawa tayi a kasa kusa da ƙafafunta,cikin sanyin murya tace"Ammi ina wuni"
"Lafiya qlau Salma ya jikin naki"
"Da sauƙi" Ta faɗa tana share hawayen da yaki tsayawa,
"Har yanzun kukan ne?
Ita dai shiru tayi bata bata amsa ba,
Hannun ta tari ko cikin nata,cikin kwantar da murya irin na wanda ake rarrashi ta shiga yi mata nasiha mai ratsa jiki,akan Kaddara da kuma yarda da ita" Kaddara wata aba ce da Ubangiji ke Daura ma bawa domin ya gwada karfin imanin shi,Salma duk wani bawa mai imani da zaki gani a ɗoron duniya tabbas yana fuskantar tashi ƙaddarar,wani za'a jarabce shine ta hanyar Ya'yan shi,wasu ta Matan shi,wasu kuma ta yan uwa ko ya'yan yan'uwa ko kuma miji,
Duka dame zamu kira shi?kaddara wanda muke fatan mu cinye ta hanya mai kyau,
Ke Allah ya jarabce kine ta hanyoyi uku,na faro mijin ki,na biyu mahaifinki,na uku kuma mahaifiyar ki,amma sai gashi a lokacin daya kin manta da Allah da ya jarabce ki yana sane dake ba kuma ya manta dake bane,kin zabi hanyar saba mashi,a maimakon komawa gare shi,kin manta cewar duk in da kika je kika dawo dole wurin shi zaki koma in da yake jiran ki a madaka domin amsa tambayoyi,kin yi zina,me zaki ce masa akan haka Salma,idan da ace a wancan ranar kin mutu ba tare da kin tuba ba me zaki ce masa Salma?
Lallai Allah yana son ki da rahama da har ya nufe ki da tashi ba tare da kin samu wani nakaso ba,wannan na nuna wata dama ce da Ubangiji ya kara baki domin ganin kin share wannan kuskuren da kika aikata,shin me zaki yi game da haka?
Ina mai baki shawara da ki yi gaggawar watsar da komai ki fuskanci rayuwarki,ki kuma ga Allah ki nime yafiyar shi,domin shi gwanine a fagen yafiya,ki dage da yin istigfari ina ganin hakan zai fi idan har kika karɓi kaddara ki da hannu biyu"
Tunda Ammi ta fara magana take kuka tana kuma auna kuraruran ta da lafukanta,
Rungume Ammin tayi tana ci gaba da kuka"tabbas na aikata laifi mai tarin yawa wanda na aikata cikin sani ba cikin rashin sani ba,domin rufewar ido dana zuciya,ina ganin tamkar babu wani wanda yake cikin kuncin rayuwa sama dani,shin kina ganin idan na nime yafiyar Allah zai yafe min?
"Me zai hana,ai shi Allah mai yin gafara ne,dan haka zai gafarta maki,ke dai kawai ki tsarkake zuciyar ki,ki kuma tabbatar ba zaki ƙara komama zunu banki ba"
"Nayi Alkawari Ammi,in sha Allah daga yau na cire komai a raina,sai dai kuma VIP,ba lallai bane ya barni,sannan Suraj....
Yatsa ta saka mata a baki," Karki damu da wannan domin Suraj zai ji da komai"
"Ta yaya aka yi kuka san da batun VIP Ammi,naga shima Suraj yawancin abubuwa baya mamaki a kansu,sannan dama kin san da aikin da ya kawo ni gidan nan tun farko me yasa kika amshe ni?sannan ya akayi kika sani?
Murmushi mai ciyo a saki,wanda iyakar shi fatan bakin ta,
" Abu ne da aka fara shekaru goma sha ɗaya data wuce,har i zuwa yau,kin ga mu ba abin mamaki bane a gare mu,har balle kamar yanda suke tunanin sun san ko wani motsi na mu,to muma kusan haka ne,duk da ba duka ba,
Tun kafin zuwan ki wannan gidan nasan da batun turo ki,a lokacin da suke niman har yar shigo dake cikin gidan a lokaci na basu hanya ta hanyar zubar da man gyada na zame har samu targade a kafa,ta hakan ne suka samu damar shigo dake,
Sun saka kina masu aiki cikin duhu ba tare da sun san ta gefe ɗaya muna muna amfani dake ba,nasan ba zaki manta wanda ya kiraki yake shaida maki ki yi maza ki bar Legas ki koma Abuja domin rayuwar Ummita na a cikin hatsari,tabbas shima yaron mijin ki ne,wanda yake bibiyar dum wani motsi nasu har ma da naki,
Sannan shi karan kanshi wanda yake saka ki aiki da sunan VIP,da kuma mutanen dake zagaye dashi dukansu yanzun a tafin hannun mu suke,Domin yanzun Kaka ta farka,dama ita ce cikon shaidar mu,kuma ta tashi,"
Tunda Ammi ta fara magana ta kafe ta da ido,cikin tsananin mamaki,wato a cikin wannan wasan dai ita ce katin wasan da kowa ke bugawa yanda yaga dama ba tare da sanin ta ba,"da yaushe ta tashi"
"Ranar da za'a maki aiki,yanzun haka mijin ki na can"
Lumshe ido tayi ta buɗe "baki bani amsar yanda akayi kija sanni ba,har kome dan gane dani,ina son sanin komai"
"Zaki sani sai dai ba yanzun ba,amma na maki Alƙawarin zan warware maki komai a gaban mahaifiyar ki,a lokacin da muka haɗu,sannan nan da kwana Takwas da za'a shiga ƙoto domin Kaka ta shigar da kara a yanzun haka,amma a London za'a yi shari'ar domin a can komai ya faro"
"Amma an kama su ne?
" Ummm to wannan dai yana hannun mijin ki,sai yanda ya tsara,amma a nasu bangaren basu san yasan komai ba"
"Ammi please waye VIP" Ta tambaya tana tsare ta da ido,
Girgiza mata kai tayi"bana ce ba,amma mu jira har zuwa lokacin da za'a shiga kotu,da idanun ki zaki ga ko ma waye,dan idan na faɗa maki ba lallai ki iya yarda ba"
Tana shirin ƙara jeho mata wani tambayar ta Daura mata yatsa a baki"shiiii no more question,sannan da zaran kome ya kare zamu mai da ke gida,sai dai ina son in zaki koma ki koma cikin mutunci da kyawun gani,dan haka zuwa anjima zamu fara kyaran jikin ki"tana gama fadar haka ta tashi ta fita tana kara jawo mata ƙofa,
Gabaɗaya zuciyarta bata mata daɗi,wato a wannan wasan ita ce a tsakiya,kuma a duhu,amfani dukan su biyu suka yi da ita wurin cin ma burin su harda Suraj,wato tun farko yasan komai,gashi sanadin wannan wasan nasu Ummita ta rasa rayuwar ta har abada,ita ma kuma Allah ne yayi da sauran shan ruwan ta a duniya,da yanzun kuma ba wannan labarin ake yi ba,ita ce babbar mai asara a cikin su,domin ta baro gidan su da komai nata,ta kuma zabe hanyar da take ganin zai fi mata sauki bata san rami take tura kanta ba,
Amma babu komai ko yanzun ta koyi darasi a kan wannan aikin,dan haka zata bi shawarar Ammi ta koma ga Allah da niman tuba,sannan da an gama wannan shari'ar zata koma gida taci gaba da rayuwar ta cikin yannin ta da iyayenta,zata manta da komai ta fara gina sabuwar rayuwar ta,
Da wannan tunanin ta tsayar da zuciyar ta wuri ɗaya.......
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*80*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*
Da Sallamah ta shigo dakin hannun ta rike da tiren kuloli,ajiyewa tayi a gefe ba tare data ce mata komai ba,ita ma din dai tana zaune ne a in da Ammi ta barta tun dazu,
Ganin har tana shirin fita bata dago ta kalle ta ba yasa ta ɗan dakata"ya jikin naki?
Kara kauda kai tayi tana kwantar dashi saman gado "da sauki"
"Allah ƙara lafiya" Ta faɗa tana fita,ita a da bata son Biba ko kadan tunda ta aure yayan ta,kuma ba tada ilimi,sai gashi cikin lokaci ƙanƙani ta shayar dasu mamaki,ashe da gaskiyar hausawa da suke cewa duk yanda kake ganin mutum karka taba raina shi saboda baka San irin baiwar da Allah ya mai ba.
Bata maci abincin ba sai da tayi barci ta tashi,sannan ta watsa ruwa,ganin lokacin sallah la'asar yayi ne yasa ta dauro Alwallah tayi sallah,ko da ta idar zaman yin istigfari tayi,har kusan ƙarfe biyar da wani abu,sannan ta shafa addu'a ta tashi,dan sau biyu Ammi na aikowa a leko ko ta gama,sai da ta ci abinci sannan ta fita,ganin bata falo ne yasa ta nufe dakin ta,
Sallamah ta yi,daga ciki aka amsa tare da tambayar"Biba ce"
"Eh ni ce"
"Shigo"
Shigowa tayi,nuna mata kan kushin tayi "zauna"
Zaunawa tayu tana kare ma dakin kallo wanda yake a kyare tsaf a ko wani lokaci,ga kamshe mai ni'ima da ke tashi,domin Ammi macece mai matukar tsafta da son kamshi,
Wani dan karamin jakka ta dauko ta zauna kusa da ita tana fito da kayan dake cikin jakkan,