Sashe 6
Yar Tsanar Zinari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mai da kanshi yayi ya jingina yana lumshe ido,
Yayin da shi kuma Direba yake cigaba da jan motar shi har ya samu suka bar Traffic din,
Dafe kai tayi tana jan dogon tsaki,tare da tunanin dole ta bar garin Abuja koda na wani lokaci ne,
Dafa kujeran da direba ke zaune ta yi "kai tsaya na sauka a nan"
Da sauri ya juyo yana gangarawa gefen titi tare da yin parking,dan ba karamin tsoro da mamaki ganin ta acikin motar da Young Ustaz yake ciki yayi ba,ta yaya ta shiga,ko dama tana ciki ne,
Cikin rawar jiki ya fito yana buɗe ta bangaren da Malamin nasu ke zaune,yayin da sauran motocin dake binsu a baya suma suka tsaya,
Kallo shi tayi sai dai idanunshi a lumshe suke kamar mai yin bacci,amma ta tabbatar ba bacci yake ba,dan tafiyar da suka yi na ƴan mintuna bai ci ace har mutum yayi barci ba,
Bata cikin yana yi mai daɗi,dan haka ce mashi kawai tayi "idan kana ji na ka rage wannan suman na kanka,idan kuma kai kurma ne Allah ya baka lafiya" tana gama fadar haka ta kulle mai kofar mota ta wuce,
"Ko ina ruwana ma da suman shi ohh" ta faɗa tana tsallaka titi dayan barayin tare da tare adaidaita ta shige,
Tambayar shi suka shiga yi ko yana lafiya,
Domin dai sun ga ko da ta fito sai da ta tsaya suka yi magana dashi a nasu fahimtar,amma kuma abin ya basu mamaki domin tunda suke dashi basu taɓa ganin shi da wata mace haka ba balle har su zauna tare,to wacece wannan.
Ganin duk irin tambayoyin da suke mai yaki kula su ne yasa dole suka koma cikin motocin sannan suka tada tare da daukar hanyar Airport in da zasu kai shi.
Suna isa airport din basu wani jima ba jirginsu ya tashi,ƙarfe biyu ta musu ne a cikin Kano,ko da suka sauka motocin gidan su ne suka zo daukar shi,
Suna tsayawa kofar gida ana kiran sallah,dan haka tsayawa sukayi a bakin Get ya sauka dan sun san ka'idar shi,
Ya fara Alwallah kenan yaji an ɗan buge kafadarshi ana dariya "Ustaz Suraj an dawo kenan,yau yamma ta nawa ka haɗu da su,domin so nake ka haɗa ni da guda biyu zafafa ko na rage hanya dasu,kasan ku malamai ba a rabaku da eh yane" Ya karasa faɗa yana dariya.
Duk maganar da yake yi yana jinshi sai dai bai bashi amsa ba har ya idar da Alwallah ya dago,
Kallon shi yayi,shima dai matashi ne wanda a ƙalla zai iya ba Suraj din shekara uku zuwa huɗu,kuma suna da dibar kama sosai da shi,daga gani dai kamar suna da alaƙa sosai da juna,
Bai bashi amsa ba ya juya ya shige cikin masallaci dan in dai Ibrahim ne yasaba da irin wannan halin nashi.
Shima kuma ganin bai kula shi bane yasa ya fara daura Alwallah kafin Abba ya fito,dan yasan yanzun zai iso masallacin,idan kuma yazo bai gan shi ba zai iya samun matsala.
Koda aka idar da sallah kafin ya fita masallaci sai da ya tsaya suka gaggaisa da mutane sannan ya fito,
A ƙofar gida ya haɗu da Abbu a tsaye wanda yana ganin shi ya sake murmushi kamar shima yanda ya samu kanshi dayi,
Karasawa yayi inda yake yana ƙoƙarin tsugunnawa ya gaisheshi,sai dai kafin ma yakai ga yin haka har ya rungume shi,
"Abbu mun same ku lafiya? Ya faɗa shima yana rungume mahaifin na shi.
" Lafiya qlau ɗan albarka,ya fama da jama'a?
"Alhamdulillah Abbu,"
Riƙe hannun shi yayi "mu je Ummin ka na jira"tare suka jero suna tafiya yana ɗan mashi tambayoyi game da tafiyar tashi,wanda haka yake matukar mantar dashi damuwar shi,dama kuma shi ba mai bari karamin abu ya tsaya mai a zuciya bane,dan yanada harkoki da yawa a gabanshi shi yasa ba karamin abu bane zai sa kaga ya riƙe ka ko a fuska ne.
Gidan babban gida ne sosai mai dauke da manyan bangarori guda biyar,
Part din dake tsakiya wato na uku shi suka shiga.
Falone babba wanda ya ji kayan alatu na rayuwa dai-dai gwargwado ba a cika komai irin na nuna isa kona Almubazzaranci ba,
Sai kamshi ke tashi ta ko ina,
Da sallamah suka shiga har tsakiyar falon in da wata yar budurwa ta amsa wacce ba zata wuce shekara goma sha huɗu ba,sanye da hijabi dai dai guiwa,da fara'a ta tare su"oyoyo yaya Suraj,barka da dawowa,Allah yasa kamin tsaraba "ta faɗa tana dariya tare da isowa in da suka zauna shida Abbu,
Murmushi ya sakar mata wanda ya kara baiyana kamar dake tsakanin su,cikin kwaikwayonta yace" Oyoyo Rabi'ah, Allah yasa kin ajiye min abin daɗi "
Dariya ta saka tana buga ƙafa irin na shagwaba,"ai Ammi ta ajiye maka,"
Dariya suke mata shida Abbu,wanda yace"kinga ƙyale shi Auta wannan karon harda ne sai an ba tsaraba,ɗan mun gaji da kullun mantawa da mu da akeyi"
Karan tafiyar da suka ji ne daga gefen su yasa suka juya,
Mace ce kyakkyawa wacce da ka ganta yanda kasan an tsaga kara tsakaninta da Suraj,da kuma ƙanwar shi,abubuwan Abbu kaɗan ne suka kwasa.
Da sauri ya tashi ya karasa inda take tare bata kyakkyawar runguma"I miss you Ammi"
Shafa bayan shi tayi"baka kai ni ba Baba na,"
Dagowa yayi ya rike hannun ta ya sumbaci hannun,"Ammi na yunwa nake ji"
"Mu je ka ci abinci"
"Ammi bari nayi wanka sai nazo na ci"
Jinjina kai tayi"ok Allah yama Albarka"
"Amin My Ammi" Ya fada yana nufar kofar fita"Abbu sai zuwa anjima "
Hannu ya daga mai,"sai ka shigo "
Yana fita ta bayan shiyansu yabi inda ya ɓulla ta wani boy's quarter,babba wanda daga dukkan alamu anan samarin gidan suke,
Duka kofofin irin wanda zaka saka ɗan kati ne ya buɗe,a kwai kuma inda zaka saka number,
Dan haka da katin yayi amfani ya buɗe ƙofar wanda wani ni'imtaccen sanyi ne ya daki hanci na,nayi mamakin ganin garman dakin domin na ɗauka ɗaki daya ne,sai dai babban falo ne madaidaici mai dauke da manya kujeru sai kayan kallo da man yan labulai wanda suka ƙara kawata falon,
Sai dakin barcin shi mai hade da bayi,
Wanka yayi ya canja kaya,sannan ya fito,sai dai a maimakon ya koma shiyansu sai naga ya shiga daya daga cikin part din dake gidan wanda yake kusa dana farko.
Da sallamah ya shigo,in da wata tsohuwa dake zaune a saman babban darduma tana baran gyada ta amsa,"Me gida na barka da dawo,"
Ya mutse fuska yayi yana zama kusa da ƙafarta "kin min tsufa,ni yarinya karama nake so"
"Kai dai faɗi gaskiya kace ka rasa mai sonka, kaga ni ma manegi nake da kai tunda an rasa meso"
Dariya ya saka wanda bai yi niya ba,"ni har yanzun banga wacce ta min ba,"
"Ko dai Aljana ta aure ka ne bamu sani ba Surajo,kai ko dan irin ƴan matan nan da samari keyi kai ban taɓa ganin ka yi ba,to bari Adamu da Auwalu su zo,dole a fara ni ma maka taimako" (Adamu shine sunan Abbu,mahaifin shi,Auwalu kuma Abba,yayan mahaifinsa,baban Ibrahim)
Ɓata fuska yayi"dan Allah ki daina ɓata min suna wai Surajo,pls ƴan mata,kuma ni bani da wata Aljana data aure ni,kin ga me zan samu a dakin nan"ya faɗa yana mikewa tare da tashi ya nufe firig dinta,buɗewa yayi yana dudduba abubuwan dake ciki,wani kwanu ya dauko ya dawo ya zauna,
Kokarin mika hannu take zata ƙwace "to ka dawo kenan ko,zaka fara caje min dakin kamar kaban ajiya,bani fura ta nan,damawa nayi na sha anjima"
Kaucewa yayi yana dariya"ke dai faɗi gaskiya dama ni kika ajiye ma,dan ki kara siye zuciya ta,to karki damu ba yanzun zan yi auren ba,"ya faɗa yana yin Bismillah tare da saka ludayi aciki yana kaiwa baki,
Sallamah suka ji daga bakin ƙofa,
Kaka ce ta amsa da karfi tana bada izinin shigowa,shi dai a hankali ya amsa,
Wata budurwa ce ta shigo kyakkyawa wanda ba zata wuce sha tara ba,sanye da jallabiya baki sai karamin hijabi,hannunta riƙe da Basket da kulolin abinci,
Cikin yanga mai haɗe da natsuwa ta shigo,ɗan dukawa tayi"barka da dawowa Yaya Suraj"
Hannu kawai ya daga mata,ba tare daya bata amsa ba,
Basket din hannun ta kai gaban Kaka ta ajiye "Kaka gashi inji Momy"
"To Allah yayi Albarka,je kikai kicin"kallon shi tayi" Surajo ko a zubo maka"
Girgiza mata kai yayi ba tare daya bata amsa ba,yana cigaba da kurban furanshi.
Tana shiga kicin sai ga wasu ƴan mata su biyu suma sun shigo,sai dai su zasu kai ishirin da uku zuwa da biyu,gai dashi suka yi saku gai da Kaka sannan suka shige cikin dakin kaka,
"Yanzun zaka saka a fara min layi a ƙofar daki Sojago,ƙarfi da yaji kasa na samu karin wasu jikokin wanda ba nawa ba,sai dun saboda kai,kai kuma na rasa kanka ace ka rasa wacce ta motsa zuciyar ka sai kace wani Dutse"
Wacce ta kai abinci kicin ne ta fito ta zauna kusa da kaka,"yaya Suraj munga wa'azin ka na Abuja yayi kyau sosai "
Wani mugun kallon daya sakar mata ne yasa ba shiri ta mai da gyadar dake hannun ta wanda ta diba,tare da tashi sumui_sumui ta shige dakin kakan,in da waɗannan yan matan suke.
Kallon shi tayi"Allah raba ka da bakin hali"
Rufe kwanun yayi"dana yi me?
"Kai kenan baka son mace ta rabe ka,,daga harara sai ka dauri yi masu bakin hali,ta yaya mace zata ji daɗin zama da kai"
Hannun ta ya rike tare da sumbatar bayan hannun,"idan na tashi aure sai na baƙi mamaki"
"Allah yasa ba mamakin da zai kashe ni zaka bani ba"
Yayin da shi kuma Direba yake cigaba da jan motar shi har ya samu suka bar Traffic din,
Dafe kai tayi tana jan dogon tsaki,tare da tunanin dole ta bar garin Abuja koda na wani lokaci ne,
Dafa kujeran da direba ke zaune ta yi "kai tsaya na sauka a nan"
Da sauri ya juyo yana gangarawa gefen titi tare da yin parking,dan ba karamin tsoro da mamaki ganin ta acikin motar da Young Ustaz yake ciki yayi ba,ta yaya ta shiga,ko dama tana ciki ne,
Cikin rawar jiki ya fito yana buɗe ta bangaren da Malamin nasu ke zaune,yayin da sauran motocin dake binsu a baya suma suka tsaya,
Kallo shi tayi sai dai idanunshi a lumshe suke kamar mai yin bacci,amma ta tabbatar ba bacci yake ba,dan tafiyar da suka yi na ƴan mintuna bai ci ace har mutum yayi barci ba,
Bata cikin yana yi mai daɗi,dan haka ce mashi kawai tayi "idan kana ji na ka rage wannan suman na kanka,idan kuma kai kurma ne Allah ya baka lafiya" tana gama fadar haka ta kulle mai kofar mota ta wuce,
"Ko ina ruwana ma da suman shi ohh" ta faɗa tana tsallaka titi dayan barayin tare da tare adaidaita ta shige,
Tambayar shi suka shiga yi ko yana lafiya,
Domin dai sun ga ko da ta fito sai da ta tsaya suka yi magana dashi a nasu fahimtar,amma kuma abin ya basu mamaki domin tunda suke dashi basu taɓa ganin shi da wata mace haka ba balle har su zauna tare,to wacece wannan.
Ganin duk irin tambayoyin da suke mai yaki kula su ne yasa dole suka koma cikin motocin sannan suka tada tare da daukar hanyar Airport in da zasu kai shi.
Suna isa airport din basu wani jima ba jirginsu ya tashi,ƙarfe biyu ta musu ne a cikin Kano,ko da suka sauka motocin gidan su ne suka zo daukar shi,
Suna tsayawa kofar gida ana kiran sallah,dan haka tsayawa sukayi a bakin Get ya sauka dan sun san ka'idar shi,
Ya fara Alwallah kenan yaji an ɗan buge kafadarshi ana dariya "Ustaz Suraj an dawo kenan,yau yamma ta nawa ka haɗu da su,domin so nake ka haɗa ni da guda biyu zafafa ko na rage hanya dasu,kasan ku malamai ba a rabaku da eh yane" Ya karasa faɗa yana dariya.
Duk maganar da yake yi yana jinshi sai dai bai bashi amsa ba har ya idar da Alwallah ya dago,
Kallon shi yayi,shima dai matashi ne wanda a ƙalla zai iya ba Suraj din shekara uku zuwa huɗu,kuma suna da dibar kama sosai da shi,daga gani dai kamar suna da alaƙa sosai da juna,
Bai bashi amsa ba ya juya ya shige cikin masallaci dan in dai Ibrahim ne yasaba da irin wannan halin nashi.
Shima kuma ganin bai kula shi bane yasa ya fara daura Alwallah kafin Abba ya fito,dan yasan yanzun zai iso masallacin,idan kuma yazo bai gan shi ba zai iya samun matsala.
Koda aka idar da sallah kafin ya fita masallaci sai da ya tsaya suka gaggaisa da mutane sannan ya fito,
A ƙofar gida ya haɗu da Abbu a tsaye wanda yana ganin shi ya sake murmushi kamar shima yanda ya samu kanshi dayi,
Karasawa yayi inda yake yana ƙoƙarin tsugunnawa ya gaisheshi,sai dai kafin ma yakai ga yin haka har ya rungume shi,
"Abbu mun same ku lafiya? Ya faɗa shima yana rungume mahaifin na shi.
" Lafiya qlau ɗan albarka,ya fama da jama'a?
"Alhamdulillah Abbu,"
Riƙe hannun shi yayi "mu je Ummin ka na jira"tare suka jero suna tafiya yana ɗan mashi tambayoyi game da tafiyar tashi,wanda haka yake matukar mantar dashi damuwar shi,dama kuma shi ba mai bari karamin abu ya tsaya mai a zuciya bane,dan yanada harkoki da yawa a gabanshi shi yasa ba karamin abu bane zai sa kaga ya riƙe ka ko a fuska ne.
Gidan babban gida ne sosai mai dauke da manyan bangarori guda biyar,
Part din dake tsakiya wato na uku shi suka shiga.
Falone babba wanda ya ji kayan alatu na rayuwa dai-dai gwargwado ba a cika komai irin na nuna isa kona Almubazzaranci ba,
Sai kamshi ke tashi ta ko ina,
Da sallamah suka shiga har tsakiyar falon in da wata yar budurwa ta amsa wacce ba zata wuce shekara goma sha huɗu ba,sanye da hijabi dai dai guiwa,da fara'a ta tare su"oyoyo yaya Suraj,barka da dawowa,Allah yasa kamin tsaraba "ta faɗa tana dariya tare da isowa in da suka zauna shida Abbu,
Murmushi ya sakar mata wanda ya kara baiyana kamar dake tsakanin su,cikin kwaikwayonta yace" Oyoyo Rabi'ah, Allah yasa kin ajiye min abin daɗi "
Dariya ta saka tana buga ƙafa irin na shagwaba,"ai Ammi ta ajiye maka,"
Dariya suke mata shida Abbu,wanda yace"kinga ƙyale shi Auta wannan karon harda ne sai an ba tsaraba,ɗan mun gaji da kullun mantawa da mu da akeyi"
Karan tafiyar da suka ji ne daga gefen su yasa suka juya,
Mace ce kyakkyawa wacce da ka ganta yanda kasan an tsaga kara tsakaninta da Suraj,da kuma ƙanwar shi,abubuwan Abbu kaɗan ne suka kwasa.
Da sauri ya tashi ya karasa inda take tare bata kyakkyawar runguma"I miss you Ammi"
Shafa bayan shi tayi"baka kai ni ba Baba na,"
Dagowa yayi ya rike hannun ta ya sumbaci hannun,"Ammi na yunwa nake ji"
"Mu je ka ci abinci"
"Ammi bari nayi wanka sai nazo na ci"
Jinjina kai tayi"ok Allah yama Albarka"
"Amin My Ammi" Ya fada yana nufar kofar fita"Abbu sai zuwa anjima "
Hannu ya daga mai,"sai ka shigo "
Yana fita ta bayan shiyansu yabi inda ya ɓulla ta wani boy's quarter,babba wanda daga dukkan alamu anan samarin gidan suke,
Duka kofofin irin wanda zaka saka ɗan kati ne ya buɗe,a kwai kuma inda zaka saka number,
Dan haka da katin yayi amfani ya buɗe ƙofar wanda wani ni'imtaccen sanyi ne ya daki hanci na,nayi mamakin ganin garman dakin domin na ɗauka ɗaki daya ne,sai dai babban falo ne madaidaici mai dauke da manya kujeru sai kayan kallo da man yan labulai wanda suka ƙara kawata falon,
Sai dakin barcin shi mai hade da bayi,
Wanka yayi ya canja kaya,sannan ya fito,sai dai a maimakon ya koma shiyansu sai naga ya shiga daya daga cikin part din dake gidan wanda yake kusa dana farko.
Da sallamah ya shigo,in da wata tsohuwa dake zaune a saman babban darduma tana baran gyada ta amsa,"Me gida na barka da dawo,"
Ya mutse fuska yayi yana zama kusa da ƙafarta "kin min tsufa,ni yarinya karama nake so"
"Kai dai faɗi gaskiya kace ka rasa mai sonka, kaga ni ma manegi nake da kai tunda an rasa meso"
Dariya ya saka wanda bai yi niya ba,"ni har yanzun banga wacce ta min ba,"
"Ko dai Aljana ta aure ka ne bamu sani ba Surajo,kai ko dan irin ƴan matan nan da samari keyi kai ban taɓa ganin ka yi ba,to bari Adamu da Auwalu su zo,dole a fara ni ma maka taimako" (Adamu shine sunan Abbu,mahaifin shi,Auwalu kuma Abba,yayan mahaifinsa,baban Ibrahim)
Ɓata fuska yayi"dan Allah ki daina ɓata min suna wai Surajo,pls ƴan mata,kuma ni bani da wata Aljana data aure ni,kin ga me zan samu a dakin nan"ya faɗa yana mikewa tare da tashi ya nufe firig dinta,buɗewa yayi yana dudduba abubuwan dake ciki,wani kwanu ya dauko ya dawo ya zauna,
Kokarin mika hannu take zata ƙwace "to ka dawo kenan ko,zaka fara caje min dakin kamar kaban ajiya,bani fura ta nan,damawa nayi na sha anjima"
Kaucewa yayi yana dariya"ke dai faɗi gaskiya dama ni kika ajiye ma,dan ki kara siye zuciya ta,to karki damu ba yanzun zan yi auren ba,"ya faɗa yana yin Bismillah tare da saka ludayi aciki yana kaiwa baki,
Sallamah suka ji daga bakin ƙofa,
Kaka ce ta amsa da karfi tana bada izinin shigowa,shi dai a hankali ya amsa,
Wata budurwa ce ta shigo kyakkyawa wanda ba zata wuce sha tara ba,sanye da jallabiya baki sai karamin hijabi,hannunta riƙe da Basket da kulolin abinci,
Cikin yanga mai haɗe da natsuwa ta shigo,ɗan dukawa tayi"barka da dawowa Yaya Suraj"
Hannu kawai ya daga mata,ba tare daya bata amsa ba,
Basket din hannun ta kai gaban Kaka ta ajiye "Kaka gashi inji Momy"
"To Allah yayi Albarka,je kikai kicin"kallon shi tayi" Surajo ko a zubo maka"
Girgiza mata kai yayi ba tare daya bata amsa ba,yana cigaba da kurban furanshi.
Tana shiga kicin sai ga wasu ƴan mata su biyu suma sun shigo,sai dai su zasu kai ishirin da uku zuwa da biyu,gai dashi suka yi saku gai da Kaka sannan suka shige cikin dakin kaka,
"Yanzun zaka saka a fara min layi a ƙofar daki Sojago,ƙarfi da yaji kasa na samu karin wasu jikokin wanda ba nawa ba,sai dun saboda kai,kai kuma na rasa kanka ace ka rasa wacce ta motsa zuciyar ka sai kace wani Dutse"
Wacce ta kai abinci kicin ne ta fito ta zauna kusa da kaka,"yaya Suraj munga wa'azin ka na Abuja yayi kyau sosai "
Wani mugun kallon daya sakar mata ne yasa ba shiri ta mai da gyadar dake hannun ta wanda ta diba,tare da tashi sumui_sumui ta shige dakin kakan,in da waɗannan yan matan suke.
Kallon shi tayi"Allah raba ka da bakin hali"
Rufe kwanun yayi"dana yi me?
"Kai kenan baka son mace ta rabe ka,,daga harara sai ka dauri yi masu bakin hali,ta yaya mace zata ji daɗin zama da kai"
Hannun ta ya rike tare da sumbatar bayan hannun,"idan na tashi aure sai na baƙi mamaki"
"Allah yasa ba mamakin da zai kashe ni zaka bani ba"