Sashe 88
Yar Tsanar Zinari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da kyar yake iya magana,kai da gani kasan yana jin jiki,"na gode ma Allah da ya nuna min dawowar ki,tabbas na cutar da rayuwar mahaifiyarku da naku,gashi ta tafi ta barni,ki yafe min"
Girgiza mai kai tayi "Baba na yafe maku kai da Mama har cikin zuciya ta,ina roƙon Allah ya bar mana kai ko zamu samu sanyi"
Hawaye ne ke yawo a idon shi "ko haka Allah ya dauki raina na gode Salma,ina maki fatan nasara da farin ciki a rayuwar ki"
"A'a zaka rayu damu"
"Ina mijin ki,Abdulrahman ya fada min kin yi aure,nayi farin ciki"
"Baba zan mai da maka oxygen numfashin ka yana katsewa"
Girgiza kai yayi"ki bari nayi magana dake"
"A'a idan ka huta zuwa anjima zamu yi magana,na maka Alkawari"
Ba dan ya so ba ta mai da mashi,
Ranar sai dare suka bar Asibitin,
Acikin mota ne ya kalle ta"me yasa ba ki yi kuka ba"
Ajiyar zuciya ta sauke tana jinginar da kanta jikin Glass"na kasa"
"Ya kamata ki yi domin gudun abin da zai iya haifar maki"
"Ji nake zuciyata ta zama kamar dutse,kamar Baba wani jini dake yawo a ciki,wata kila ni ma lokaci na yana dab ne"
Bai bata amsa ba sai ma girgiza kai da yayi,dole tana buƙatar kuka ko ta yaya ne,shi shaida ne akan yanda suka Shaku da Mama,sannan ace yau bata duniya amma ko hawaye bata zubar ba,Allah kaɗai yasan irin ƙonewar da take yi a ciki,
Yanayin parking a cikin gidan,ta fito ta shige ciki,tunda bata ga motocin su Bala ba ta san sun wuce kenan,
Dakin Mama ta buɗe ta shiga,
Aunty Hulairaw ce ta biyo bayan ta"Ki yi wanka bari na kawo maki abinci "
Girgiza kai tayi"bana buƙata,hutu nake so"
"Amma kin san bai kamata ki zauna da yunwa ba ko?
Cikin tsananin damuwa ta juyo gare ta" Dan Allah!ina son in huta,ki ajiye zan ɗauka anjima "
Fita tayi kawai tana jawo mata ƙofa,gaskiya akwai matsala,ita kan ba zata bari haka kawai ka kashe kanta ba,gara ta faɗama Abdulrahman ya kira mijinta ya faɗa mashi........
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*87*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*
Tana shirin kiran shi kenan sai gata ta fito"Aunty Hulaira,zan sha Tea "
Ajiye wayar tayi"yauwa to bari na haɗa maki"cikin yan mintina ta haɗa mata shayi mai ƙauri,ta kuna zaunar da ita anan falo kasancer sauran yan uwa na ɗayan falon,
Sai da ta tabbatar ta sha sannan ta shiga yi mata nasiha,
Washegari ma bata zauna a gida ba tana Asibiti wurin Baba,wanda ba karamin daɗi hakan ya masa ba,domin ko ba komai ganin ta ya rage kaso casa'in na damuwar shi,
Ranar ma sai dare Abdulmalik ya komar da ita gida,su kansu hankalin su yafi kwanciya akan ta zauna a nan din suna ganin hankalin ta ba zai kwanta ba,
A ranar ƙarfe uku na dare suka samu kiran gaggawa daga Asibiti,
Inna'illahi wa'inna'ilaihi rajiun,kafin su isa Allah ya amshi abin shi,a wannan ranar na Laraba sha huɗu ga watan shida shekara ta dubu biyu da ishirin da uku,
Mutuwar data kara girgiza su da kara masu imani,
Basu faɗa mata ba sai da aka dawo da gawar ƙarfe takwas na safe,
Abdulrahman ne ya jawo Aunty Hulaira gefe"kin faɗa mata kuwa?
Dafe kanta tayi"na kasa,ina tunanin irin halin da zata shiga,har yanzun taki kuka akan na Mama,ka duba ka gani acikin kwana biyun nan yanda ta koma,gabaɗaya tayi rama yanka kasan wacce ke ciyo,bata cin abinci,haka kuma bata bacci,yanzun idan na faɗa mata abinda ya faru bansan me zai same ta ba"
"Dole ne zamu faɗa mata ko ba komai dole tayi sallamah da shi,bari naje na same ta"
Ɗakin ya shiga da sallamah,a zaune ya same ta a bakin gado bata dago ba sai dai ta amsa,
Ya dan jima tsaye a kanta sai dai ya rasa ta yanda zai fada mata,
"Salma" Ya kira sunan ta,
"Na'am" Ta amsa masa,ya kira ta ya kai sau uku tana amsa mashi sai dai ya kasa fadar komai,
Dago shanyayyun idanun ta tayi wandan suka zurma acikin kwanakin da basu gaza biyu zuwa uku ba,tunda yau din ne sadaka ukun Mama,
"Yau mun karasa zama marayu gabaki daya ko yaya?
Sai da ya dan zabura,kafin kuma ya sukar da kai,
Mai da kanta tayi kasa" Na rika na sani tun lokacin da kuka bar gida ƙarfe uku na dare cikin tashin hankali,na sani! Sai dai ka sani ni ba zan zamo maku damuwa ba,ni musulma ce na san hakan ƙaddara tace wanda ban isa in guje mata ba"
Rungume ta yayi yana fashewa da kuka,domin shi kam bai da karfin zuciya,
Sai da yayi kuka sosai tana jin shi amma ita ta kasa yin kukan,
Aunty Hulaira ce ta shigo ta daga ta"mu je ku sallame shi saboda lokacin yayi da za'a mika shi dakin shi na gaskiya "
Ganin kamar tana layi ne yasa ta riƙe mata hannu,a haka har suka shiga dakin shi da anan aka wantar da gawar wanda fuska kawai ya rage a ɗaure,
Duk zama sukaya suka zagaye shi,
Addu'a kowa ya shiga yi mashi da fatan samun da cewa,Abdulmalik da Abdulrahman ne hawaye ke zarya a idanun su,yayin data mai da idanun ta kan Abdulmajid da idanun shi suka yi ja suka kumbura alamun shima yaci kukan,sai ita da take yi wani irin nauyi a zuciyar ta,yayin da idanun ta suka shige ciki sannan suka yi ja yanda kasan wacce yaji ya shigar ma ido haka take jin suna mata raɗaɗi,
Kallon dakin take yi yayin da rayuwar su ke sake dawo mata acikin ƙwaƙwalwar ta,da yanda suka mu'amala dashi a cikin wannan dakin,yau kuma shine yake bankwana da wannan dakin,a hankali ta fara ji fitar numfashin ta na nimar gagaran ta,dakin kuma na juya ma a lokacin daya,
Ta dai ji an rungumi ta ana salati,daga nan bata ƙara sanin abinda ya faru bayan nan ba.
*Washegari*
A hanka ta fara buɗe idanun ta,dakin take ganin yana mata dishi_dishi,kanta na dan sarawa kaɗan,
Hannu takai tana ƙoƙarin dafa kan,sai jin saukar lallausar hannu taji saman goshin ta sannan a hankali ana mata massage,hakan yasa ta mai da idanun ta ta kulle,an dauki mintuna ana mata kafin taji an saya sannan an daga gadon da take sama kaɗan,hakan yasa ta kara dube idanun ta,jin tayi an zauna kusa da ita sannan an riƙe hannun ta,
Kokari take da idanun ta wurin son tantance wanda ke zaune kusa da ita,
Cikin shakakkiyar muryarta da baya fita sosai ta kira sunan shi domin son tabbatar da ko shi din ne "Suraj"
Sumbatar hannun ta dake cikin nashi yayi"Bebin "
"Zan sha ruwa"
Goran ruwa dake ajiye ya ɗauka tare da kofi wanda ke ajiye a cikin Basket din da aka saka kulolin abinci,tsiyaya mata ruwan yayi ya da gata baki daya ya jinginar a jikin shi,ma'ana rabin jikin ta yana saman nashi,
Ƙafa mata kofin ruwan yayi,kirɓa biyu ya bari tayi ya cire kofin ya ajiye,
"Zan kara ruwan"
Girgiza mata kai yayi"zai saki ciyon ciki,ki bari an jima sai ki sha"
Komar da kanta tayi ta jinginar a kafadarsa idanun ta lumshe,kamar minti biyu tayi wani irin zabura wanda da badan ya riƙe ta ba cikin zafin nama, da babu abinda zai hana ta faɗowa har ma taji ciyo,
"Baba" Sunan da ya fito bakin ta kenan,tana ƙoƙarin sauka daka jikin shi,
Duk yanda yaso ta nutsu kin natsuwa tayi sai kokawar sauka take yi,gashi jini har ya fara biyo Cannula dake hannun ta da aka saka mata drip,
Hakan yasa ya daka mata tsawa wanda sai da dakin ya ɗauka,ai kuma nan take ta natsu jin yanda jikin ta ya amsa wani riƙo da ya maka,
Cikin fushi yace"so kike ki kashe kanki?idan wani abu ya same ki fa?ance baki cin abinci,baki bacci,sannan baki yi kuka,me kike son ki zama?
Ita ma cikin muryar kuka tana kwace hannun ta daga nashi"ya same mana,ina rukan ka dani "
"Naji ina zaki je?
" Babu ruwan ka da in da zanje "
Kin bari ta sauka yayi"idan har ba zaki faɗamin in da zaki ba, ni kuma ba zan bari ki tashi ba"
Duk yanda taso kwace kanta kasawa tayi domin da hannu daya kawai ya rike mata hannu,"kalle ni"
Dago jajayen idanun ta tayi ta saka cikin nashi,
"Maman ki ta mutu kwanaki hudu da suka wuce,jiya kuma Baban ki shima ya mutu,dukkan su ba zasu dawo ba,kin zama marainiya,wacce ba tada uwa ba tada uba" Ganin yanda ta nasu tana kallon shi ne yasa ya sake mata hannu yana furzar da ajiyar zuciya,"sun tafi in da ba zasu taba dawowa ba,sun tafi in da babu wani abunda zaki iya yi domin su dawo,haka Allah yaga dama,bai kadarta zaki haɗu da ita ba,ba zaki iya yin komai akan haka ba,zuciyar ki zafi kawai zata ci gaba daya,idanun ki kuma zasu ci gaba da yin ja,wanda hakan ke nuna rashin karɓar ƙaddarar ki,kinki ki karɓi ƙaddara,so kike ki nuna ma Ubangiji ke mai taurin kai ce, ko kuma ke mai taurin zuciya ce,b.....
Gani yayi hawaye sharrr ya sauko daga cikin idanun ta,
Ɓoyayyen ajiyar zuciya ya sauke "wannan shi ake nufi da taushi,idan har zuciyar ka ta kuntata,har ka samu ka saka tayi laushi,to zaka samu sassauci,har ka iya ɗaukar ƙaddara,s....
Duka ta kai nasa a kirji tana fashewa da kuka" Waye ya faɗa maka ban karɓi kaddara ba?kai ba kasa halin da zuciyar mutum ke shiga ba idan ya rasa wanda yake muradin gani,kai baka san wannan kuncin ba"ta kara fada tana kara karfin kukan ta,
Girgiza mai kai tayi "Baba na yafe maku kai da Mama har cikin zuciya ta,ina roƙon Allah ya bar mana kai ko zamu samu sanyi"
Hawaye ne ke yawo a idon shi "ko haka Allah ya dauki raina na gode Salma,ina maki fatan nasara da farin ciki a rayuwar ki"
"A'a zaka rayu damu"
"Ina mijin ki,Abdulrahman ya fada min kin yi aure,nayi farin ciki"
"Baba zan mai da maka oxygen numfashin ka yana katsewa"
Girgiza kai yayi"ki bari nayi magana dake"
"A'a idan ka huta zuwa anjima zamu yi magana,na maka Alkawari"
Ba dan ya so ba ta mai da mashi,
Ranar sai dare suka bar Asibitin,
Acikin mota ne ya kalle ta"me yasa ba ki yi kuka ba"
Ajiyar zuciya ta sauke tana jinginar da kanta jikin Glass"na kasa"
"Ya kamata ki yi domin gudun abin da zai iya haifar maki"
"Ji nake zuciyata ta zama kamar dutse,kamar Baba wani jini dake yawo a ciki,wata kila ni ma lokaci na yana dab ne"
Bai bata amsa ba sai ma girgiza kai da yayi,dole tana buƙatar kuka ko ta yaya ne,shi shaida ne akan yanda suka Shaku da Mama,sannan ace yau bata duniya amma ko hawaye bata zubar ba,Allah kaɗai yasan irin ƙonewar da take yi a ciki,
Yanayin parking a cikin gidan,ta fito ta shige ciki,tunda bata ga motocin su Bala ba ta san sun wuce kenan,
Dakin Mama ta buɗe ta shiga,
Aunty Hulairaw ce ta biyo bayan ta"Ki yi wanka bari na kawo maki abinci "
Girgiza kai tayi"bana buƙata,hutu nake so"
"Amma kin san bai kamata ki zauna da yunwa ba ko?
Cikin tsananin damuwa ta juyo gare ta" Dan Allah!ina son in huta,ki ajiye zan ɗauka anjima "
Fita tayi kawai tana jawo mata ƙofa,gaskiya akwai matsala,ita kan ba zata bari haka kawai ka kashe kanta ba,gara ta faɗama Abdulrahman ya kira mijinta ya faɗa mashi........
🦂🧸YAR TSANAR ZINARI🧸🦂
Story & Writing
By
JIDDARH UMAR
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
*Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba*
*87*
*Paid book*
*300₦*
*Hauwa Umar, Zenith Bank,2284905309*
*mai buƙata sai ya tuntuɓe ni ta wannan number domin turo shaidar biya, 08141644865*
Tana shirin kiran shi kenan sai gata ta fito"Aunty Hulaira,zan sha Tea "
Ajiye wayar tayi"yauwa to bari na haɗa maki"cikin yan mintina ta haɗa mata shayi mai ƙauri,ta kuna zaunar da ita anan falo kasancer sauran yan uwa na ɗayan falon,
Sai da ta tabbatar ta sha sannan ta shiga yi mata nasiha,
Washegari ma bata zauna a gida ba tana Asibiti wurin Baba,wanda ba karamin daɗi hakan ya masa ba,domin ko ba komai ganin ta ya rage kaso casa'in na damuwar shi,
Ranar ma sai dare Abdulmalik ya komar da ita gida,su kansu hankalin su yafi kwanciya akan ta zauna a nan din suna ganin hankalin ta ba zai kwanta ba,
A ranar ƙarfe uku na dare suka samu kiran gaggawa daga Asibiti,
Inna'illahi wa'inna'ilaihi rajiun,kafin su isa Allah ya amshi abin shi,a wannan ranar na Laraba sha huɗu ga watan shida shekara ta dubu biyu da ishirin da uku,
Mutuwar data kara girgiza su da kara masu imani,
Basu faɗa mata ba sai da aka dawo da gawar ƙarfe takwas na safe,
Abdulrahman ne ya jawo Aunty Hulaira gefe"kin faɗa mata kuwa?
Dafe kanta tayi"na kasa,ina tunanin irin halin da zata shiga,har yanzun taki kuka akan na Mama,ka duba ka gani acikin kwana biyun nan yanda ta koma,gabaɗaya tayi rama yanka kasan wacce ke ciyo,bata cin abinci,haka kuma bata bacci,yanzun idan na faɗa mata abinda ya faru bansan me zai same ta ba"
"Dole ne zamu faɗa mata ko ba komai dole tayi sallamah da shi,bari naje na same ta"
Ɗakin ya shiga da sallamah,a zaune ya same ta a bakin gado bata dago ba sai dai ta amsa,
Ya dan jima tsaye a kanta sai dai ya rasa ta yanda zai fada mata,
"Salma" Ya kira sunan ta,
"Na'am" Ta amsa masa,ya kira ta ya kai sau uku tana amsa mashi sai dai ya kasa fadar komai,
Dago shanyayyun idanun ta tayi wandan suka zurma acikin kwanakin da basu gaza biyu zuwa uku ba,tunda yau din ne sadaka ukun Mama,
"Yau mun karasa zama marayu gabaki daya ko yaya?
Sai da ya dan zabura,kafin kuma ya sukar da kai,
Mai da kanta tayi kasa" Na rika na sani tun lokacin da kuka bar gida ƙarfe uku na dare cikin tashin hankali,na sani! Sai dai ka sani ni ba zan zamo maku damuwa ba,ni musulma ce na san hakan ƙaddara tace wanda ban isa in guje mata ba"
Rungume ta yayi yana fashewa da kuka,domin shi kam bai da karfin zuciya,
Sai da yayi kuka sosai tana jin shi amma ita ta kasa yin kukan,
Aunty Hulaira ce ta shigo ta daga ta"mu je ku sallame shi saboda lokacin yayi da za'a mika shi dakin shi na gaskiya "
Ganin kamar tana layi ne yasa ta riƙe mata hannu,a haka har suka shiga dakin shi da anan aka wantar da gawar wanda fuska kawai ya rage a ɗaure,
Duk zama sukaya suka zagaye shi,
Addu'a kowa ya shiga yi mashi da fatan samun da cewa,Abdulmalik da Abdulrahman ne hawaye ke zarya a idanun su,yayin data mai da idanun ta kan Abdulmajid da idanun shi suka yi ja suka kumbura alamun shima yaci kukan,sai ita da take yi wani irin nauyi a zuciyar ta,yayin da idanun ta suka shige ciki sannan suka yi ja yanda kasan wacce yaji ya shigar ma ido haka take jin suna mata raɗaɗi,
Kallon dakin take yi yayin da rayuwar su ke sake dawo mata acikin ƙwaƙwalwar ta,da yanda suka mu'amala dashi a cikin wannan dakin,yau kuma shine yake bankwana da wannan dakin,a hankali ta fara ji fitar numfashin ta na nimar gagaran ta,dakin kuma na juya ma a lokacin daya,
Ta dai ji an rungumi ta ana salati,daga nan bata ƙara sanin abinda ya faru bayan nan ba.
*Washegari*
A hanka ta fara buɗe idanun ta,dakin take ganin yana mata dishi_dishi,kanta na dan sarawa kaɗan,
Hannu takai tana ƙoƙarin dafa kan,sai jin saukar lallausar hannu taji saman goshin ta sannan a hankali ana mata massage,hakan yasa ta mai da idanun ta ta kulle,an dauki mintuna ana mata kafin taji an saya sannan an daga gadon da take sama kaɗan,hakan yasa ta kara dube idanun ta,jin tayi an zauna kusa da ita sannan an riƙe hannun ta,
Kokari take da idanun ta wurin son tantance wanda ke zaune kusa da ita,
Cikin shakakkiyar muryarta da baya fita sosai ta kira sunan shi domin son tabbatar da ko shi din ne "Suraj"
Sumbatar hannun ta dake cikin nashi yayi"Bebin "
"Zan sha ruwa"
Goran ruwa dake ajiye ya ɗauka tare da kofi wanda ke ajiye a cikin Basket din da aka saka kulolin abinci,tsiyaya mata ruwan yayi ya da gata baki daya ya jinginar a jikin shi,ma'ana rabin jikin ta yana saman nashi,
Ƙafa mata kofin ruwan yayi,kirɓa biyu ya bari tayi ya cire kofin ya ajiye,
"Zan kara ruwan"
Girgiza mata kai yayi"zai saki ciyon ciki,ki bari an jima sai ki sha"
Komar da kanta tayi ta jinginar a kafadarsa idanun ta lumshe,kamar minti biyu tayi wani irin zabura wanda da badan ya riƙe ta ba cikin zafin nama, da babu abinda zai hana ta faɗowa har ma taji ciyo,
"Baba" Sunan da ya fito bakin ta kenan,tana ƙoƙarin sauka daka jikin shi,
Duk yanda yaso ta nutsu kin natsuwa tayi sai kokawar sauka take yi,gashi jini har ya fara biyo Cannula dake hannun ta da aka saka mata drip,
Hakan yasa ya daka mata tsawa wanda sai da dakin ya ɗauka,ai kuma nan take ta natsu jin yanda jikin ta ya amsa wani riƙo da ya maka,
Cikin fushi yace"so kike ki kashe kanki?idan wani abu ya same ki fa?ance baki cin abinci,baki bacci,sannan baki yi kuka,me kike son ki zama?
Ita ma cikin muryar kuka tana kwace hannun ta daga nashi"ya same mana,ina rukan ka dani "
"Naji ina zaki je?
" Babu ruwan ka da in da zanje "
Kin bari ta sauka yayi"idan har ba zaki faɗamin in da zaki ba, ni kuma ba zan bari ki tashi ba"
Duk yanda taso kwace kanta kasawa tayi domin da hannu daya kawai ya rike mata hannu,"kalle ni"
Dago jajayen idanun ta tayi ta saka cikin nashi,
"Maman ki ta mutu kwanaki hudu da suka wuce,jiya kuma Baban ki shima ya mutu,dukkan su ba zasu dawo ba,kin zama marainiya,wacce ba tada uwa ba tada uba" Ganin yanda ta nasu tana kallon shi ne yasa ya sake mata hannu yana furzar da ajiyar zuciya,"sun tafi in da ba zasu taba dawowa ba,sun tafi in da babu wani abunda zaki iya yi domin su dawo,haka Allah yaga dama,bai kadarta zaki haɗu da ita ba,ba zaki iya yin komai akan haka ba,zuciyar ki zafi kawai zata ci gaba daya,idanun ki kuma zasu ci gaba da yin ja,wanda hakan ke nuna rashin karɓar ƙaddarar ki,kinki ki karɓi ƙaddara,so kike ki nuna ma Ubangiji ke mai taurin kai ce, ko kuma ke mai taurin zuciya ce,b.....
Gani yayi hawaye sharrr ya sauko daga cikin idanun ta,
Ɓoyayyen ajiyar zuciya ya sauke "wannan shi ake nufi da taushi,idan har zuciyar ka ta kuntata,har ka samu ka saka tayi laushi,to zaka samu sassauci,har ka iya ɗaukar ƙaddara,s....
Duka ta kai nasa a kirji tana fashewa da kuka" Waye ya faɗa maka ban karɓi kaddara ba?kai ba kasa halin da zuciyar mutum ke shiga ba idan ya rasa wanda yake muradin gani,kai baka san wannan kuncin ba"ta kara fada tana kara karfin kukan ta,