Sashe 27
Bayan Na Mutu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yanzu kuma ga zuwan Al'ameen, wani mutum da tayi kokarin yakicewa daga zuciyarta a baya, ta daurewa kanta ta hana shi yin tasiri a rayuwarta har zuwa lokacin da take ganin sun nesanta da juna, ashe k'addara ta tanadi wata hanyar, don ta d'auki wannan zuwan nasa a matsayin k'addara duk da cewa aikin gabansa ne ya kawo shi... k'addarar da take tunanin zata saita ta a yanzu da iya kokarinta.
Ta jera dukkan abinda ta gama soyawa a tray sannan ta fita dasu falo, Tv a kunne take tana nuna labaran BBC yayin da Daddy ke zaune a kujerar dake fuskantarta, a gefensa Al'ameen ne shirye cikin wata hadaddiyar gray suit kamar an auna ta a jikinsa, ya fito a kamanninsa na matashin lauya, hasken safiyar ya haska mata kyawun fuskarta da bata gani gabad'aya a daren jiya ba, kyawun fuskar daya rud'e ta a baya ta fad'a tarkonsa cikin wannan watan guda d'aya!
Magana suke yi da alamu mai muhimmanci, don ya sunkuyar da kansa kad'an yana kallon Daddyn, amma fitowarta yasa ya wulkito da idonsa ya kalle ta tsaye daga kofar kitchen d'in, sai ta juya da sauri ta nufi dining ta ajiye tray d'in sannan ta koma, haushin kanta taji sosai yadda ya kamata tana kallonsa.
"Deelah, fito da dankalin daga cikin fryer nan."
Mami ta fad'a har a lokacin tana waya, sanda ta koma falon babu kowa don haka ta shiga jera warmers d'in data d'auko a gefen sauran kayan kan tebur d'in.
Motsin tsayuwarsa a kusa da ita taji ba tare da taji sanda ya taho ba, ta rufe idonta a hankali had'e da guntuwar addu'a don bayan gaisuwar jiya, bata so ko kad'an wata magana a kusa ta k'ara had'a su, sai dai ga mamakinta bai ko kalleta ba wata 'yar guntuwar sannuki da aiki' kawai yace sannan ya jawo kujera d'aya ya zauna ya fara k'ok'arin d'aukan plate.
"Aunty deelah, ga spoon d'ina nan baki saka ba."
Muryar Iman ta katse ta sanda ta fito sanye cikin uniform d'inta, saboda haka bata amsa masa ba ta ajiye cokalin Iman daga cikin na hannunta sannan ta koma kicin, sanda ta kawo plate d'in Daddy ta k'ara juyawa ne muryarsa ta katse ta.
"Uhm, Fadeelah..."
Zuciyarta ta buga da nauyi, ya Allah! wai ta manta ne cewa ya iya fad'ar sunanta haka? bata juyo ba yace.
"In akwai tea bag na lemon ki taho min dashi dan Allah."
"Baza'a rasa ba kam, ki duba cupboard d'in can gefe daga sama."
Mami ta sake katse amsawarta sanda ta k'araso ta ajiye k'arin wani flask na ruwan zafi, Iman ta juyar da kai game da kokarin tab'e dogon hancinta.
"Mami k'amshin man suya kike yi da yawa."
Bata san me Mamin tace ba, amma tana jiyo dariyarsu daga kitchen d'in har da Al'ameen, wannan dariyar tasa da ada take saka ta nishadi kamar me.
K'arfe bakwai dai-dai sanda kowa ya fito aka zauna cin abincin, Al'ameen yana ta hirarsa da dariya musamman shi da Faruq wanda ke ta bashi labarin abubuwa da ya sani yanzu a Nigeria, har Zahra itama ta shiga hirar tana gaya masa cewa ita kanta yanzu da za'a koma America to banda ita, Sai dai yadda ka san Allah bai halicci Fadeelah dake zaune a tsallaken kujerarsa ba, haka bai ko kalle ta ba, balle yayi mata magana.
Wanda kuma saboda son zuciya, sai
rashin kulatan yasa taji ba dad'i kad'an, son zuciya mana! in ba son zuciya ba ta manta abinda tayi ne? ta manta abinda tayi shekara guda data wuce? ta manta abinda tayi masa a tsakiyar makarantarsu?
Fadeelah ki tsaya ki saurare ni dan Allah, I want to talk to you, kin hana ni ganinki tsawon lokaci... kin san yadda nake ji kuwa?
Babu maganar data rage tsakaninmu, na gaya maka kayi hakuri ba zai yiwu ba.
Komai ya riga ya yiwu Fadeelah, saboda na riga na fara sonki kuma na san ke ma kina sona, saboda haka ki bani damar da zan nuna miki duk wad'annan dalilan naki na shirme ne basu isa su tsaida mu ba.
Ta rufe locker data d'ebo litattafanta sannan ta kalle shi, yana tsaye dab! da ita yadda litattafan ne kawai suka yiwa jikinsa da nata katanga, sai ta matsa baya kad'an.
Ni a wajena babu shirme a cikinsu Al'ameen, in kana tunanin kwakwalwata tana da matsala ne shi yasa ka fad'i hakan...
Ya katseta ta cikin d'imbin hayaniyar d'aliban dake wucewa a bayansu.
Kin san ba haka nake nufi ba Fadeelah, abu mai muhimmanci anan shine muna son junanmu, me yasa zamu wahalar da kanmu...
Ban fad'a maka ina sonka ba Al'ameen.
Da na san bakya sona babu abinda zai sa in damu kaina tsawon lokacin nan, kuma har na biyo ki nan...
Fargabarta d'aya a lokacin kar su Melissa su k'araso su gansu tare, don tunda ta yanke duk wata alak'arta dashi bata son k'arin wasu mutane a rayuwarta su san dashi.
Bana sonka Al'ameen, idan baka yarda da abinda na fad'a a baya ba, ka gayawa zuciyarka wannan ka fita daga rayuwata.
Maganar ta dake shi, amma sai yayi murmushi kad'an sannan yace.
Kinyi kokari, kin fad'i abinda ni ba zan tab'a iyawa ba, duk don ki cutar da kanki...
Haushi ya fara kamata, me yasa ne wai ba zai fahimce ta ba? ta d'ago da idonta ta kalle shi.
Hanyar lafiya nake kokarin nemowa kaina Al'ameen, kaine yanzu kake kokarin cutar dani ta hanyar da zaka amfani kanka kai kad'ai.
Kamar yaya?
Zuciyarka ta gaya maka tana sona, saboda haka kana k'okarin bata abinda kake so ne kawai ba tare da tunanin halin da ni zan shiga ba.
Na gaya miki...
Baka gaya min komai ba Al'ameen sai son zuciyarka kuma na fahimce ka sarai saboda haka nima ka fahimce ni ka fita daga rayuwata, na fad'a maka bana sonka kuma bana sonka a cikin rayuwata.
Tayi maganar ne da k'arfi cikin hasala kuma da harshen turanci, saboda haka mafi yawanci d'aliban dake baya da kuma gefensu suka juyo suka kalle su sannan wasu suka fara dariya, wannan dariyar ita ta keta zuciyar Al'ameen gutsi-gutsi, ransa ya b'aci, yaji ya muzanta a tsakiyar yaran da kowannensu bai kai sa'an k'aninsa mai bi masa ba, da ace yana dashi d'in kenan, sannan wata irin kunyar kansa ta kamashi a gaban 'yar k'aramar Fadeelan da shashashar zuciyarsa ta jawo masa raini a wajenta.
Abinda ta fad'a a gaba shi yayi sanadin guntule alak'arsu tun daga wancan lokacin.
Idonta na kallon cikin nasa tace.
Wallahi bana sonka Al'ameen, kuma bana tunanin zan tab'a sonka!
"Ranar ashirin ga watan september a shekaru biyar da suka wuce kamfaninku yasa hannu akan yarjejeniyar had'in kai tsakaninku da kamfanin Dibbons P.C dake America a birnin Washington.
Daga cikin k'aidojin yarjejeniyar akwai dokar data had'a da cewar zaku dinga turo 40% na ribarku a kowacce shekara.
A shekaru biyun farko da suka biyo baya kun aika da ribar, amma daga nan kowacce shekara sai ku kawo uziri na matsalolin da kuke fuskanta da suke hana ku samun wata kwakkwarar riba, don haka a yanzu kamfanin ya turo mu, mu ma'aikatansa da kuma wasu daga cikin lauyoyin kamfanin don mu tabbatar da dukkanin hujjojin da kuke bayarwa kuma muga komai da idon mu."
Mark Bowden, d'aya daga cikin ma'aikatan da Al'ameen yazo yiwa kamfaninsu aiki ya fad'a yana kallon jerin mutanen d'aya kamfanin da suka zo bincike akansu k'asar Nigeria.
A yanzu farkon fara aikinsa dole ne ya rik'e matsayin Solicitor (lauya mai bincike a waje) kafin ya kai matsayin Barrister da zai dinga aiki tare da organization kawai, kamar yadda tsarin ma'aikatarsu yake.
Fatansa ma shine ya had'a biyu, ya rik'e muk'amin da ba kowa ke iya rikewa ba wato matsayin Solicitor da kuma Barrister kamar wani kwararren lauyan daya gani abokin kamal, duk da b'angaren da yake da nasa yasha banban amma yana fatan shima ya iya kawo hakan cikin aikinsa.
Matashi ne kamar shi, amma yana da wani irin k'ok'ari da hazak'a da yawan ma'aikatu irin nasu na lauyoyi suka san dashi, a d'an iya sanin da yayi masa daga nesa zai iya cewa shine role model d'insa a yanzu, ya yardarwa kansa cewa yana son zama irin ADAM STEVE a aikinsa, don shi d'in daban ne a cikin lauyoyi masu irin matakinsa.
A lokacin wata mace daga cikin mutanen d'aya kamfanin ta mik'e don yin bayanin dake cikin file d'in hannunta, ya kalli mayafin data yafa, irin kalarsa Fadeelah ta d'aura a kanta yau sak! tayi wani d'auri mai kyau yana reto a gefe d'aya.
Yaja tsaki a k'asan numfashinsa, shi ya san har yanzu bai yarda da zuciyarsa akanta ba, shi yasa tun farko baiyi niyyar sauka a gidan ba sanda aka had'a har da sunansa a masu tafiyar, amma zuwan Daddy ya tsaya akan cewar babu hotel d'in da zaije ya sauka alhali suna gari d'aya.
Fatansa d'aya ne a yanzu, kar yawan ganinta a kullum yasa alkawarin daya d'aukowa mahaifiyarsa ya kwance, don kamar yadda Fadeelah ta fad'a masa a baya ne, haka itama ta biya masa kuma tasa ya haddace cewar...
Abinda yake tunani tsakaninsu ba zai tab'a faruwa ba!
Saboda haka a yanzu yana yin komai ne bisa tsarin da ta kafa masa tun lokacin da taji Daddy ya kafe sai a gidansu zai sauka, yana bin duk maganganunta d'aya bayan d'aya.
Matsalar shine... bai tabbatar in hakan zai d'ore ba.
"Gobe zamu je sayayya dasu Sahla." Zahra ta fad'a da yamma tana tsaye a gaban mudubi tana taje gashinta."
"Me zaku siyo?" Iman ta tambaya daga k'asan gado inda ta baje litattafanta tana homework.
"Kayan da zamu yi decoration na class party mana, kin san ni aka nad'a caretaker."
Iman ta tab'e bakinta.
Dama ai in kina musu wannan iyayin naki dole ne a baki.
"Me kika ce?" Ta tambaya tana kallonta ta cikin mudubin.
"Cewa nayi ke ya kamata dama a bawa."
Sai tayi murmushi sannan ta cigaba da taje gashinta.
Ta jera dukkan abinda ta gama soyawa a tray sannan ta fita dasu falo, Tv a kunne take tana nuna labaran BBC yayin da Daddy ke zaune a kujerar dake fuskantarta, a gefensa Al'ameen ne shirye cikin wata hadaddiyar gray suit kamar an auna ta a jikinsa, ya fito a kamanninsa na matashin lauya, hasken safiyar ya haska mata kyawun fuskarta da bata gani gabad'aya a daren jiya ba, kyawun fuskar daya rud'e ta a baya ta fad'a tarkonsa cikin wannan watan guda d'aya!
Magana suke yi da alamu mai muhimmanci, don ya sunkuyar da kansa kad'an yana kallon Daddyn, amma fitowarta yasa ya wulkito da idonsa ya kalle ta tsaye daga kofar kitchen d'in, sai ta juya da sauri ta nufi dining ta ajiye tray d'in sannan ta koma, haushin kanta taji sosai yadda ya kamata tana kallonsa.
"Deelah, fito da dankalin daga cikin fryer nan."
Mami ta fad'a har a lokacin tana waya, sanda ta koma falon babu kowa don haka ta shiga jera warmers d'in data d'auko a gefen sauran kayan kan tebur d'in.
Motsin tsayuwarsa a kusa da ita taji ba tare da taji sanda ya taho ba, ta rufe idonta a hankali had'e da guntuwar addu'a don bayan gaisuwar jiya, bata so ko kad'an wata magana a kusa ta k'ara had'a su, sai dai ga mamakinta bai ko kalleta ba wata 'yar guntuwar sannuki da aiki' kawai yace sannan ya jawo kujera d'aya ya zauna ya fara k'ok'arin d'aukan plate.
"Aunty deelah, ga spoon d'ina nan baki saka ba."
Muryar Iman ta katse ta sanda ta fito sanye cikin uniform d'inta, saboda haka bata amsa masa ba ta ajiye cokalin Iman daga cikin na hannunta sannan ta koma kicin, sanda ta kawo plate d'in Daddy ta k'ara juyawa ne muryarsa ta katse ta.
"Uhm, Fadeelah..."
Zuciyarta ta buga da nauyi, ya Allah! wai ta manta ne cewa ya iya fad'ar sunanta haka? bata juyo ba yace.
"In akwai tea bag na lemon ki taho min dashi dan Allah."
"Baza'a rasa ba kam, ki duba cupboard d'in can gefe daga sama."
Mami ta sake katse amsawarta sanda ta k'araso ta ajiye k'arin wani flask na ruwan zafi, Iman ta juyar da kai game da kokarin tab'e dogon hancinta.
"Mami k'amshin man suya kike yi da yawa."
Bata san me Mamin tace ba, amma tana jiyo dariyarsu daga kitchen d'in har da Al'ameen, wannan dariyar tasa da ada take saka ta nishadi kamar me.
K'arfe bakwai dai-dai sanda kowa ya fito aka zauna cin abincin, Al'ameen yana ta hirarsa da dariya musamman shi da Faruq wanda ke ta bashi labarin abubuwa da ya sani yanzu a Nigeria, har Zahra itama ta shiga hirar tana gaya masa cewa ita kanta yanzu da za'a koma America to banda ita, Sai dai yadda ka san Allah bai halicci Fadeelah dake zaune a tsallaken kujerarsa ba, haka bai ko kalle ta ba, balle yayi mata magana.
Wanda kuma saboda son zuciya, sai
rashin kulatan yasa taji ba dad'i kad'an, son zuciya mana! in ba son zuciya ba ta manta abinda tayi ne? ta manta abinda tayi shekara guda data wuce? ta manta abinda tayi masa a tsakiyar makarantarsu?
Fadeelah ki tsaya ki saurare ni dan Allah, I want to talk to you, kin hana ni ganinki tsawon lokaci... kin san yadda nake ji kuwa?
Babu maganar data rage tsakaninmu, na gaya maka kayi hakuri ba zai yiwu ba.
Komai ya riga ya yiwu Fadeelah, saboda na riga na fara sonki kuma na san ke ma kina sona, saboda haka ki bani damar da zan nuna miki duk wad'annan dalilan naki na shirme ne basu isa su tsaida mu ba.
Ta rufe locker data d'ebo litattafanta sannan ta kalle shi, yana tsaye dab! da ita yadda litattafan ne kawai suka yiwa jikinsa da nata katanga, sai ta matsa baya kad'an.
Ni a wajena babu shirme a cikinsu Al'ameen, in kana tunanin kwakwalwata tana da matsala ne shi yasa ka fad'i hakan...
Ya katseta ta cikin d'imbin hayaniyar d'aliban dake wucewa a bayansu.
Kin san ba haka nake nufi ba Fadeelah, abu mai muhimmanci anan shine muna son junanmu, me yasa zamu wahalar da kanmu...
Ban fad'a maka ina sonka ba Al'ameen.
Da na san bakya sona babu abinda zai sa in damu kaina tsawon lokacin nan, kuma har na biyo ki nan...
Fargabarta d'aya a lokacin kar su Melissa su k'araso su gansu tare, don tunda ta yanke duk wata alak'arta dashi bata son k'arin wasu mutane a rayuwarta su san dashi.
Bana sonka Al'ameen, idan baka yarda da abinda na fad'a a baya ba, ka gayawa zuciyarka wannan ka fita daga rayuwata.
Maganar ta dake shi, amma sai yayi murmushi kad'an sannan yace.
Kinyi kokari, kin fad'i abinda ni ba zan tab'a iyawa ba, duk don ki cutar da kanki...
Haushi ya fara kamata, me yasa ne wai ba zai fahimce ta ba? ta d'ago da idonta ta kalle shi.
Hanyar lafiya nake kokarin nemowa kaina Al'ameen, kaine yanzu kake kokarin cutar dani ta hanyar da zaka amfani kanka kai kad'ai.
Kamar yaya?
Zuciyarka ta gaya maka tana sona, saboda haka kana k'okarin bata abinda kake so ne kawai ba tare da tunanin halin da ni zan shiga ba.
Na gaya miki...
Baka gaya min komai ba Al'ameen sai son zuciyarka kuma na fahimce ka sarai saboda haka nima ka fahimce ni ka fita daga rayuwata, na fad'a maka bana sonka kuma bana sonka a cikin rayuwata.
Tayi maganar ne da k'arfi cikin hasala kuma da harshen turanci, saboda haka mafi yawanci d'aliban dake baya da kuma gefensu suka juyo suka kalle su sannan wasu suka fara dariya, wannan dariyar ita ta keta zuciyar Al'ameen gutsi-gutsi, ransa ya b'aci, yaji ya muzanta a tsakiyar yaran da kowannensu bai kai sa'an k'aninsa mai bi masa ba, da ace yana dashi d'in kenan, sannan wata irin kunyar kansa ta kamashi a gaban 'yar k'aramar Fadeelan da shashashar zuciyarsa ta jawo masa raini a wajenta.
Abinda ta fad'a a gaba shi yayi sanadin guntule alak'arsu tun daga wancan lokacin.
Idonta na kallon cikin nasa tace.
Wallahi bana sonka Al'ameen, kuma bana tunanin zan tab'a sonka!
"Ranar ashirin ga watan september a shekaru biyar da suka wuce kamfaninku yasa hannu akan yarjejeniyar had'in kai tsakaninku da kamfanin Dibbons P.C dake America a birnin Washington.
Daga cikin k'aidojin yarjejeniyar akwai dokar data had'a da cewar zaku dinga turo 40% na ribarku a kowacce shekara.
A shekaru biyun farko da suka biyo baya kun aika da ribar, amma daga nan kowacce shekara sai ku kawo uziri na matsalolin da kuke fuskanta da suke hana ku samun wata kwakkwarar riba, don haka a yanzu kamfanin ya turo mu, mu ma'aikatansa da kuma wasu daga cikin lauyoyin kamfanin don mu tabbatar da dukkanin hujjojin da kuke bayarwa kuma muga komai da idon mu."
Mark Bowden, d'aya daga cikin ma'aikatan da Al'ameen yazo yiwa kamfaninsu aiki ya fad'a yana kallon jerin mutanen d'aya kamfanin da suka zo bincike akansu k'asar Nigeria.
A yanzu farkon fara aikinsa dole ne ya rik'e matsayin Solicitor (lauya mai bincike a waje) kafin ya kai matsayin Barrister da zai dinga aiki tare da organization kawai, kamar yadda tsarin ma'aikatarsu yake.
Fatansa ma shine ya had'a biyu, ya rik'e muk'amin da ba kowa ke iya rikewa ba wato matsayin Solicitor da kuma Barrister kamar wani kwararren lauyan daya gani abokin kamal, duk da b'angaren da yake da nasa yasha banban amma yana fatan shima ya iya kawo hakan cikin aikinsa.
Matashi ne kamar shi, amma yana da wani irin k'ok'ari da hazak'a da yawan ma'aikatu irin nasu na lauyoyi suka san dashi, a d'an iya sanin da yayi masa daga nesa zai iya cewa shine role model d'insa a yanzu, ya yardarwa kansa cewa yana son zama irin ADAM STEVE a aikinsa, don shi d'in daban ne a cikin lauyoyi masu irin matakinsa.
A lokacin wata mace daga cikin mutanen d'aya kamfanin ta mik'e don yin bayanin dake cikin file d'in hannunta, ya kalli mayafin data yafa, irin kalarsa Fadeelah ta d'aura a kanta yau sak! tayi wani d'auri mai kyau yana reto a gefe d'aya.
Yaja tsaki a k'asan numfashinsa, shi ya san har yanzu bai yarda da zuciyarsa akanta ba, shi yasa tun farko baiyi niyyar sauka a gidan ba sanda aka had'a har da sunansa a masu tafiyar, amma zuwan Daddy ya tsaya akan cewar babu hotel d'in da zaije ya sauka alhali suna gari d'aya.
Fatansa d'aya ne a yanzu, kar yawan ganinta a kullum yasa alkawarin daya d'aukowa mahaifiyarsa ya kwance, don kamar yadda Fadeelah ta fad'a masa a baya ne, haka itama ta biya masa kuma tasa ya haddace cewar...
Abinda yake tunani tsakaninsu ba zai tab'a faruwa ba!
Saboda haka a yanzu yana yin komai ne bisa tsarin da ta kafa masa tun lokacin da taji Daddy ya kafe sai a gidansu zai sauka, yana bin duk maganganunta d'aya bayan d'aya.
Matsalar shine... bai tabbatar in hakan zai d'ore ba.
"Gobe zamu je sayayya dasu Sahla." Zahra ta fad'a da yamma tana tsaye a gaban mudubi tana taje gashinta."
"Me zaku siyo?" Iman ta tambaya daga k'asan gado inda ta baje litattafanta tana homework.
"Kayan da zamu yi decoration na class party mana, kin san ni aka nad'a caretaker."
Iman ta tab'e bakinta.
Dama ai in kina musu wannan iyayin naki dole ne a baki.
"Me kika ce?" Ta tambaya tana kallonta ta cikin mudubin.
"Cewa nayi ke ya kamata dama a bawa."
Sai tayi murmushi sannan ta cigaba da taje gashinta.