Sashe 29
Kutkale Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*Free page* *Alhamdulilah, nan na kawo karshen free page...du mai son ci gaban Kutkale ya garzayo ta hanyar biyan nasa ya samu shiga cikin grup din* Ta jima tana auna maganarsa, kafin ta janye hannunta tana harararsa, A dan kufule ta ce" a ina aka taba yi? Dama an tana haka? Wace za.a dauko dan ta tsare lafiarka kace sai an daura maku aure? To danme ma za.a wani aura maka yarinyar? Ka yi yaya da ita? Kansa ya shafa yana kallon maman basa har ta gama kafin ya ce" an samu ci gaba kala daban daban a duniya Ummih, Sun buda wannan wajen dan a dauka a kuma biya su, Akoy damar ka auri mace na adadin lokacin da ka dauketa aiki, su zasu san yanda zasu yi tsarinsu, sannan ni fa ba wani abu nake nufi dan nace a yi hakan ba, halin rayuwa nake dubawa, Kanta ta dafe da hannunta na dama, Da na hagu ta yi masa nuni da ya tafi, Dan haka a hankali ya mike yana mai adu.ar Allah yasa ta ki amincewa, shi fa a gaskiya baya so, baya ra.ayi, haba, ko dan bata san shi nasa aikin da yake yi na biye bane ya saka take takurar kanta haka? Da zata san menene ainahin aikinsa, da bata damu kanta haka ba, somin ya baro saudiya ne bisa dalili kwakwara na kasancewarsa agent mai aiki a boye, ya baro ne dan shima da nasa aikin, kasuwanci da ya karanta shi duniya ta sanshi da aikinsa, idan ba wannan ba ta yaya zai ringa gane abubuwan dake faruwa a tatare da shi? Shi ba aljani ba? Horon da ya samu, ya yi imanin ba zasu taba samun irinsa ba! A haka ya baro gidan mahaifiyarsa, cikin motar da yake ja da kansa, Ya yi tuki mai nisa ya ja gefe ya tsaya sakamakon sarawa da kansa ya yi, Idannuwansa ya lumshe ya shiga karanta du wata ayar da ta zo bakinsa dan neman tsari, Kansa ya jinginar jikin kujerar da yake tuki samanta, Gabansa ne ya yanke ya fadi, ya kara yankewa ya fadi, Da sauri ya dafe daidai zuciyarsa yana mai jin wata irin zufa na karyo masa, Innalilahi wa.ina ilaihi raj.une! Shi ne abinda ya shiga maimaitawa ba ji ba gani, Wani irin ribos ya yi da motar ya dauki hanyar gidan mahaifiyarsa, gaba daya jikinsa rawa yake, Gaba dayansa ya fice a hayacinsa, irin wannan abin ne ya faru da shi, a shekarun da suka shige, shekarun da ya rasa babansa, shekarun da ya rasa kanwarsa, shi ba mahaukaci bane, kudi gata basu saka ya zauce ba.... yana rayuwar sakalci ne bisa dalilai, Horn din da ya dane ya saka mai gadi mikewa da gudu gudu ya bude masa kofa yana mamakin abinda ya dawo da shi, Yana shiga gidan abinda ya hango ya saka shi sakin sitiyarin motar ya dora hannayensa biyu saman kansa tare da fasa wani ihu mai taratsin mai fitar da innalilahi wa.ina ilaihi raj.une Hannayensa saman kansa motar ta je ta daki karfen rumfar ajiye motoci, nan rumfar ta rufto ta rufe motar baki daya, inda da wuta ka yi tunanin idan har za.a iya ciro mutun da rai daga wannan accident Wannan shi ne farko, Wannan shi ne mafarin sabuwar rayuwar da zata budewa *ABDUL JABAR*, wannan shi ne duhu, kunci, rayuwar gimgim, rayuwar gimtsewar da zata samu Abdul Jabar, daga wannan lokaci, wannan dan saurayi mai rayuwa cike da sangarta, da garari, ya dawo tamkar kurma, ya dawo wani bahagumen mutun mai wuyar zama, Ya kai sati kwonce cikin halin rashin sannin inda kansa yake a babar asibitin garin, inda sojoji ke gadinsa , A ranar da ya farka ya kai dubansa saman agendar dake dakin makekiya ta shekarar da ake, Bai gane ranar da ake ba, sai dai awar ta bashi damar gannin kamar ya kwana a wajen kennan? A lokacin da likita ke cike da murnar farfadowarsa bayan sati daya da sumarsaa ya saka shi jin wani irin bugawar zuciya, Da kyar ya iya buda bakinsa ya ce" ina Ummih? Ina Ummih? Gargadin da yarima Muhammad ya yi kan kar wanda ya bashi amsar nan ya saka su kokarin gannin sun masa alurar da zata saka shi baci, Sai dai ina, a hankali karfin zuciyarsa ya hayo inda ya shiga kokowa da su yana ihun ina Umminsa? Ta mutu ko? Ta mutu? Ku kai ni wajen gawarta, ku kai ni na ga gawarta, sun kasheta? Ummih, kina fadi sai da suka rufe maki baki? Daneshi suke son yo aman sun kasa dan haka suka baiwa sojoji biyun da suka shigo waje suka kai shi kasa suka dane kafin ya tsira masa allurar baci, Shiru dakin ya dauka, dan kuwa sai da ta kashe masa jiki idannuwansa kekashe kafin ta yi masarar daukansa, ........................................ Haushi yarinyar ke bata walahi, bata san yaya zata yi ta taro yarinyar da a haife ta girmeta aman take hauka irin haka, Dama haka mutanen dake kallonta tana tafka tsiya har wa iyayenta suke jin haushinta? A gaskiya da tana da yancin cewa ita a mayar da ita camp da ta fada domin du wani kokarin nunawa yarinyar shirmenta ya jaza mata tiwa saurayi rashin mutuncin da ya wanka mata mari da ikirarin sai ya tozartata, ta kasa fahimta, Ko yanzu da suke tsaye, Hafsat din na tsaye bayanta , ita kuma sai hauka take na fadan ita gaskiya dad a rabata da wannan mai biye da bayan nata, haba sai kace jela, wai kayan da ta yi niyar sakawa Hafsat din ta hanata, dama haka ne? Aikinta fa ta bata tsaro a biyata, to na me zata ringa shiga hurumin irin suturar da zata saka? Maimakun ya tsawatar mata ya nuna mata hanata saka kayan nan damamu shi ne daidai ko dan gudun janyo hankalin mugayen samari kanta, sai ya shiga rarashinta da fada mata ta yi hakuri ya je ya samo wannan Bodyguard din ne dan a samu a kamo yaron da ya daga hannu ya mareta , da barazana kala kala, ko so take sai ya kona mata fuskar? Jin maganar kona fuska ya sakata girgiza kai a hankali tana mai jin gabanta na dokawa, ina idan aka taba mata lafiyar fuska an gama da rayuwarta, ita dake takama da kyan fuskarta? Ita dake ji du duniya babu abinda ba zata iya sakawa ba dan gannin fuskarta ta kara kyau? Lale wannan saurayin ya aika, gashi tunda hakan ya faru da su tama daina ganninsa a makarantar ko a gida, du ya dauke kafarsa ya yi kwontan bauna , jira yake sa.a ta kama shi ya damketa Kara tsoratar da ita ya yi cikin hikima , kafin ta hakura ta fita da shigar abaya kamar yanda Hafsat din ta saka itama suka fita tare suka nufi university wajen daukan karatun yar budurwar .....wannan itace mission din Hafsat ta biyu da ta samu, inda take baiwa budurwa tsaro mai shekaru ashirin da biyu a duniya, wace ke bata wahala sosai don kuwa sam bata bata damar da zata yi aikinta yanda ya kamata, tana nuna halin yarinta da sangarta, tana matukar wahalar da aikin, hakan na konawa Hafsat rai, domin irin tsayayar da yarinyar ke nunawa na tuna mata muguwar rayuwar da ta yi har ta taka san barawo, gashi kuma mahaifinta da mahaifiyarta sun daure mata , basa gannin matsalar dake tare da su, Bayan sun dawo, dare ya tsala, Daren alhamis ne, wato wayewar juma.a, daren da yawancin bayi masu nema wajen Allah suke raya shi, Tun karfe goma mutuniyar tata ta yi baci, hakan ya sakata gyara du abinda zata gyara, ta cire abin kunnen nata ta ajiye shi ta fito cikin shiga ta abaya tare da yane kanta da mayafi baki, Tafiar kafa ne ta ci ta mamaki, wace ta sha mamakin yanda aka yi ta gane hanyar kanta, A hankali, ta rabe kofa tana kallon yanda ake dan raragewa, sai muryar malan dake tashi yana ta wa.azi, Sai da ta jima nan tsaye kafin ta yi wuf ta shiga, ta baya ta yi sando ta shake mutumen dake tsaye nan ya tafi duniyar suma, dama daga shi sai malan, ya fito sake alwallah ta yi wuf da shi,.. A hankali ta shiga masalacin, Bayansa take hange, ta rakube tana dubansa, Wasu zafafan hawaye ne suka shiga siraro mata, tana kallonsa ta saka kafarta bayan ta cire takalminta da safarta ta dan fara takawa da niyar karasawa wajensa sai dai ji ta yi an rufe mata idonta da bakinta an dauketa cimak an fita da ita inda take wutsil wutsil da kafafuwanta........ Malan dake zaune tsai ya yi da wa.azin da yake ya dan waiwayo bayansa, Wani abu ya ji kamar uwata ta ziyarci wajen, Wata irin ajiyar zuciya ya sauke, idannuwansa ya lunshe ubda ya shafi gemun fuskarsa, Hawaye ne ya ji sun cika masa ido, walahi ya san da ta mutu da Allah ya saka masa dangana a kanta, tana raye, innalilahi wa.ina ilaihi raj.une, Haka kawai sai ya cire wa.azin ya shiga wata irin kira.a ta hanyar daukan suratul Yusufa ya lumshe ido yana yi yana mai tuna irin tarihin yusufa zuciyarsa na kara tsumuwa tana kara kusanta shi da ubangijinsa........ Basu direta ko.ina ba sai cikin bakar motarsu, suka ja da mugun gudu suka nufi anguwar da take aikin, Nesa da gidan kadan suka yi parking kafin a saketa, A yanda ta hayayako da sun yi sanya wajen kare kansu tabas da ta jiwa wani, Ido cikin ido suke kallon juna ita da BS, tsaye su dukansu cikin motar inda ya saka mutun ukun da suka kamota fita aka batsu daga shi sai ita, Tamkar wasu zakaru irin yanda kowa ke kallon kowa da tarin haushin dan uwansa, San me kike saka kanki a uku, danme kike son saka mini zuciya cikin tunani da hargitsi? Me yasa ke du motsinki na wanda zaki tarwatsa min tunani ne? Ke dake bakin aiki ashe kina faman tarwatsa komai? Idan har kika je ya ganki a yanzu koda zaki saka masa glue kin isa ki hana shi yada cigiyar nemanki, a tv, a redio? Ku ku goma sha shida na hora, ban taba zuwa gado dan yin baci baki fado mini