← Book details Kuskuren Baya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 160

Sashe 9

Kuskuren Baya Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Jaguwa  zaune  cikin d'akin daya tanada  domin  tautauna bayanai masu  mahimmanci  akan aikinsa  ,gabansa laptop dinshi ne ,yana faman operating  yana sauraron  bayanan  jubi  inda yake bayani akan alhaji tanko gote wanda ya kasance shararraren dan kasuwa wanda   duniya tasan da zamansa sannan ya tara tarin  dukiya bilaadadin  anan  gida nigeria da kasashen  ketari  ,ya mallaki qadarori da dama  da companies a kowace jaha dake ƙasar nigeria " bincikenmu  ya nuna mana mutumin  baya zaman gidansa  da daddare sai da rana  bayan  haka  akwai  tsaro mai tsanani tun  daga bakin get  doping  estate  har  zuwa cikin gidansa ta kowani bangare  dakarunsa  zagaye suke  da gidan  bayan boyayyun  camerori dake lugu  da sako na gidansa, me zai hana  mu hakura da wannan taget din  muyi  facing din wani  yayi shiru hade da numfasawa  sannan ya cigaba da magana "jaguwa a ganina mu hakura da wannan aiki  kawai ko me kuka ce yan'uwa ?  ya  fadi haka yana kallon  sauran yan'uwansa dake zaune suna sauraronsa , duk suka gyara  "gaskiya mu hakura tun da tsaro yayi yawa  inji cewar kamil  ,Anas ya numfasa yace  " kuna nufin bazamu yi nasara ba akan aikin da muka ɗauki tsawon lokaci muna jiran aiwatar dashi ? a qalla wannan shine karo na hudu da muke rusa budget din aiki akan Alhaji tanko gote  gaskiya a ganina bai kamata muyi wasa da damarmu ba kawai mu fara shirin aiwatar dashi kuma a cikin satin nan "dan Allah malam ka natsu kayi nazari akan operation din nan    jabir ya katse masa hanzari  ta hanyar fadar haka"the best solution mu hakura tunda jubi da kamil suka nuna abar shi , kai koni nayi supporting dinsu mu hakura kawai muyi facing din wani aiki ......

    Sai lokacin Jaguwa ya d'ago kyawawan idanunshi masu matukar kyau jere da gashin ido  ya tsura musu yana  kallonsu daya bayan daya sai daya ɗauki tsawon minti biyar yana kallonsu  sannan ya mike  tsaye yana rufe  laptop d'insa  ya soma magana a tsanake kamar ba wannan shararraren tantirin daya addabi manya kusoshin gwanati  da manya attajirai ba  "duk naji bayaninku daya bayan daya amman kusani wannan aikina ne jiya ba yau ba , da  muna saka tsoro a zukatanmu da bamu kawo wannan matsayin ba  , matsayin ƙasar nan take bulayin neman Jaguwa ido rufe, burin duk wani dan sanda mai matsayi ya samu nasarar gano inda muke ,ko'ina acikin kasar nan magana ɗaya ne ana son ganin wanene wannan mutumin daya addabi kasa da kasa  gidajen radio dana  tv , news paper ko'ina magana ɗaya ne   amman har yau basu yi nasarar gano mu ba abinda zai faru yanzu shine ni da kaina zan tunkari tanko gote ya karasa maganar a fusace yana dukan table din dake tsakiyar su jabir  sannan ya juya musu baya rugume da hannunwansa duka  .....

Duk suka zaro ido a frigice  suna dubansa  gaba-daya jikinsu yayi mugun sanyi  da jin furucinsa   Anas ya mike ya karasa inda yake ya tsaya a gabansa "kalle ni Jaguwa ya d'ago kyawawan idanunshi ya zuba masa batare da yace uffan ba  "bazan barka ka tafi kai ɗaya ba ko kowa yaki binka ni zan bika amman me zai hana mu hakura nima jikina yayi sanyi  bamu taba samun saɓanin ra'ayi akan halqallarmu ba sai yau me zai hana mu hakura kawai  ....
  "Kawai abar aiki saboda tsoro ko me ? yayi masa tambayar yana tsareshi da kyawawan  idanunshi ,a hankali Anas ya gyada masa kai "ba saboda tsoro bane "saboda me ye faɗa min Ina jinka ? "me yasa ni ban karaya ba ku zaku karaya ? "me yasa ni bangujewa aikin ba ku zaku guje masa ? wannan karon a tsawace yayi maganar yana dubansu ransa a matukar  bace "daman mun tsara haka ne dan wata  rana zamu sakawa zukantanmu tsoron aiwatar da qudirinmu ? dukkaninsu suka gyada kai alamun a'a  suna dubansa da mamakin karfin halinsa "mun san duk abinda ka faɗa gaskiya amman .... "listing  yayi saurin daga musu hannu " banason jin komai  zanje  Kuma ni kadai zan aiwatar da komai zan nuna muku kwarewata ta wuce yadda suka tsamamnin .....

Duk wannan maganar  dake yake yinta cikin isa da izza da rashin kuruciya  yake yinta ,dan kallo ɗaya zaka masa ka fahimci  ya mallaki hankalin  kansa sannan yasan meye rayuwa babu alamun kuruciya atare dashi , ya sake kallonsu daya bayan daya "ku fito ku faɗa min cewar  matsorata ne , " a she ku din kananan yan iska ne iskancinku bai taka kara ya karye ba kuka hau matsayin da masu dakakkiyar zuciya suke hawa ...
"A she akwai abinda zaku ji tsoro bayan kuna dani kuna tare dani ? Zan fita ni kadai raina nayi gaba da gaba da tanko gote ya karasa maganar a tsawace cike da fushi jikin Anas ya dinga  kyarma ya shiga rarrashinsa dan yasan halinsa abu kankani ke bata masa rai har yayi nasarar dagula nasu lissafi yana gama maganar bai tsaya ya saurari rarrashin da Anas yake masa  ya fice daga d'akin kallon juna suka shiga yi kamil ne yayi karfin hali yin magana "yanzu ya zamuyi da alamun ya hau dokin nakin daya saba ? "Ku bar  shi tukunna  zuwa anjima  mu gani zan san yadda zanyi na shawo kansa, ni kaina  na hakura duk abinda mutun ɗaya mutun biyu har uku sukayi magana akanshi mafi alkhairi a hakura dashi    inji cewar Anas a hankali suka cigaba da tautaunawa ..

Kai tsaye special room d'insa    dake  kallon wanda tanweer take ciki ya shiga  ya zare rigar jikinsa ya saura daga shi sai vest fari da dogon wando ,ya ɓalle agogon dimond din dake daure a tsintsiyar hannunsa ya ajiye akan mirrow dinsa tare da wayoyinsa  ya dauki remut ya kara karfin ac  ,ya karasa inda karamin  fridge  dinsa yake ya ɗauki kwalban win  mai sanyi ya ɓalle   ya kafa a bakinsa  bai ajiye ba sai daya sha rabi sannan ajiye yana sauke numfashi sannan ya   kwanta  ruf da ciki  akan bed yana tunani yadda zai tunkari gidan  tanko gote a safiyar gobe ,kusan minti goma yana kwance sannan ya yunkura ya  mike tsaye  zuciyarsa na dokawa da matsanancin karfin gaske, sai dai sosai  yake jin jarumta a sansar jikinsa  sam bai ji wani karaya ba ko sarewa ko jin rashin nasara , kallon dakin yayi sosai kwakwaluwarsa ke sake  lulawa duniyar  tunani akan lamarin, motsin da yaji a bayansa shi ya sanya shi  saurin juyowa , ganin Anas ne ya dauke kansa , zama tayi a bakin gado  a lokacin da Anas ya karaso ya zauna kusa dashi tare da kamo hannunsa ya daura cikin tafin hannunsa "kayi hakuri abokina kuma aminina "da'akayi me kenan kake bani hakuri ? yayi masa tambayar yana furzar da iska mai zafi  tare da fixge hannunsa cikin nashi "ni dai kayi hakuri naga ka ɗauki zafi "akan me zan ɗauki zafi ya sake  katse shi yana haɗe  hannuwansa guri daya "ni babu wani zafi dana ɗauka aiki ne babu fashi gobe ko jibi zan aiwatar dashi akan idanunku zanje na dawo ya karasa maganar yana murnushin gefen baki alamun nasara yake ji ajikinsa  "ka fahimceni abokina "dan me zan  fahimceka akan
mutumin da babu Allah a ranshi?  kuke jin tsoron tunkarasa .....
"nasani amman ka tsaya mu shiryawa tunkararsa  tukunan irin su Alhaji tanko ba'a tukaransu haka nan dole sai anyi shiri na musamman  "listing anas akan wannan mutumin  bazan  taba fahimtarka ba, batu akan tsara tunkurarsa an wuce gurin sai dai kuma wani aikin  "shikenan shikenan ni zan bi ... , kar ku bini ko kunce zaku bini ma  bazan  lamunta ba ,ya karasa maganar cikin fushi , Anas ya sauke ajiyar zuciya "shikenan Allah ya baka Sa'a "ameen ya fada yana mik'ewa  haɗe da shiga bathorrom ....

**********
Chapter 9 · 0% Book details