← Book details Kuskuren Baya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 49 OF 160

Sashe 49

Kuskuren Baya Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read

Yana fita number minister ya fara nema kira uku yayi kafin a d'auka ,hajiya zainab ce ta dauka cikin   sanyayyiyar   murya  tace" hello yana jin sautin muryar ya fahimci mahaifiyar tanweer ce dan bazai manta da muryar ba da irin kuka da kururuwan da tayi a daren  da zai taho da tanweer muryarsa a dikile ya soma magana cikin Isa " Ina minister ?ta waiga a sukune ta Kalli Inda minister yake zaune aqasan tayis yayi tagumi da hannunsa d'aya cikin tsananin tashin hankali "wake magana ?ta tmby cike da faduwar gaba "babu buqatar sanin haka sai dai dalilin Kiran shine ki fad'awa mijinki idan yana kusa " cewar ya dakatar da kawalayen daya tura haushi  gari dan nemammamu  wato jami'an tsaro  idan ba haka ba zai zama  sanadin rasa rayuwar diyarsa tanweer   ".
nan take jikin hjy zainab ya kama rawa hawayen dake makale a kwarnin idanunta suka sauka akan quncinta , a hankali ta soma karanta hasbinallahu wa ni'imal wakil  tana  cigaba da  sauraransa "ki fad'a masa ya janye if not you'll lose your daughter  ko Kuma musa ayi reping dinta mu yada a social media  yana gama fad'ar haka yayi disconnecting din kira yana fesar da iska.
wani kuka hjy zainab ta fashe dashi ta zube kasa tana  furta kalmar  " inna lillahi wa inna ilaihi rajiun da sauri minister ya matso kusa daita dan tunda ta d'auki wayar tana kallonsa shima ya tattara hankalinsa da natsuwarsa gurinta a rud'e yake tambayarta "menene zainab me akace miki   a  wayar  da'aka  kira ?" dan girman  Allah ka kira   office  din commissioner yanzu yanzu ka  sheida masa a tsaida jami'an tsaron nan bana son na rasa tanweer ,bana son wani mummunar abu ya faru daita  iya abinda ta fad'a kenan ta zube jikinsa tana sake fashewa da wani sabon kuka  numfashinta na sama da kasa. kamota yayi ya rungumeta yana shafa bayanta"is  okay zainab babu abinda zai samu tanweer dinmu da izinin allah  lafiya zata  dawo  garemu . yayinda ita Kuwa hjy zainab babu abinda take cewa sai "ka kira commissioner ."
Can  bangaren  jami'n tsaro kuwa suna  Isa 1829  plaza  dake  gaban isalo a  matukar  harzuke suka   firfito  suka  shiga  ciki  kmr  d'azu wasu suka tsaya a waje Wanda suka shiga suka fara  tambayar manager gurin, Kai tsaye aka nuna musu Inda yake  nan da nan suka fara aika masa tambayoyi akan mutane da suka shigo plaza din a wanni da suka gabata  "ai mutane dayawa sun shigo a yau din nan yalla'bai  "ko zaka iya gane fuskokin wanda da suka shigo ya fad'a  tare da nuna masa hoton jaguwa ?" gsky bazan iya ba  amman  tunda ga hoto  bari mu qunna cctv  camera mu duba  " take  yayi rewarning   cctv   suka tsurawa   tv din dake gurin kusa guda biyar idanunsu , idanun manager ne ya Kai kan motar jaguwa   "yalla'bai  ga wata   mota nan ta tsaya a haraban plaza a awa biyu  data gabata nan  dukkaninsu  suka   bada attention dinsu suna duban motar suna sauraronsa "  mutun d'aya ne ya fito daga cikin motar  fuskarsa  rufe da face   mask   nima Kuma a wannan  lokacin na fita  Kuma tabbas naga wannan motar mai number 2548 bayan ya shigo nima na dawo Ina kallonsa yana daukar dogayen  riguna na mata haka kawai naji hankalina bai kwanta dashi ba  idanuna na kanshi har sanda ya biya kudin kayan  ya wuce duk yadda akayi wannan mutumin ne duk da fuskarsa bata bayyana ba kamar yadda hotonsa yake  suna tsaka da sauraronsa kiran commissioner ya shigo wayar  dcp, ya d'auka cikin sauri yana cewa "hello sir "kuyi maza ku dawo akwai matsala "matsala Kuma sir ?
"Eh babba kuwa  domin rayuwar yarinyar na cikin hatsari idan aka cigaba da bibiyarsu ga dukkanin alamun akwai wanda yake yiwa  hukuma zagon kasa".  aikuwa yayi babban kuskure ya cuci alluma har ma da zaqaqarun yansanda masu k'okarin ganin an kawar da ta'addanci a kasa  inji cewar dcp batare da bata lokaci ba dcp ya juya yana  bawa yaransa  umarni ."Tafiya kawai dcp yake baya ko gamin gabansa saboda takaici da bakinciki wai sai yaushe ne zasu yi nasara akan jaguwa ?sai yaushe zasu yi nasara akan shi Kawar dashi daga doron duniya da wannan tunani ya Isa gidansa.

Jaguwa ya dade tsaye a lambun gidansa byn ya  gama waya  da mahaifiyar tanweer   yana shawagi agurin tare  da  tunani kala dabam dabam cikin  haka wayarsa ta soma ringing ya d'auka ya manna a kunne ya tura hannunsa cikin  aljihun wandonsa maganar minti biyar kacal sukayi ya katse Kiran  ya cigaba da shawagi  sai gasu anas  kowannensu hannunsa rike da tabar wiwi yayinda anas ke rike da biyu ya mikawa jaguwa d'aya, ya amsa ya kai bakinsa ya fara zuka sannan gabad'ayansu suka samu guri suka zauna suna magana akan  mata "ya kamata mu dan fita yau ko Kuma muyi invent dinsu zuwa gidan nan ?"ai rayuwa babu mace quntatawa ne kasamu mace lafiyiyayya  Kuma me shaye shaye ka sauke gajiyarka akanta  inji  cewar jubi murmushi jabir yayi "wallahi kamar kuwa kasani mace me shaye shaye tafi dadin muamula  ga juriya saboda bata haiyacinta  haka dai  sukayita hirarsu akan  mata
yayinda  jaguwa ya lula  duniyar  tunanin wanda  tunanin  kusan duk  na tanweer ne .yana  jin kamar ya shareta amman zuciyarsa ya kasa aiwatar da hakan  ko  babu komai tana bukatar kulawarsa  tunda bata da  lafiya  kuma idan bata ci abinci ba  taya za'a yi ta sha magungunanta ?
wannan tunanin yasa ya kira aliyu ya aika siyo mata  abinci bayan kamar awa d'aya aliyu  ya dawo hannunsa rike da  farar leda ya amsa ya ajiye ya cigaba da zugar wiwi , sai da yayi mankas sannan ya mike ya  nufi  d'akinta   bakinsa d'auke  da  sallama hannunsa  rike da farar leda  yayinda  gbdy jikinsa ke warin wiwi hade da turaren jikinsa .
Chapter 49 · 0% Book details