Sashe 16
Kuskuren Baya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*****
A hankali ya bude kyawawan idanunshi ya daura akan ƙaramin agogon dake ajiye akan abun gado, karfe takwas ya gani har ta wuce da wasu yan mintuna tsaki yaja saboda ya makara idan akwai abinda ya tsana bai wuce makara gurin sallah ba , ya kwantar daita tare da lullu'beta da bargo ya mirgina ya sauko ya janyo towel ya d'aura ajikinsa cike da natsuwa ya shiga bathorrom , bathtube ya shiga ya tsaya ya soma sakarwa jikinsa ruwa, wankar tsarki yayi tukuna domin tsaftace jikinsa sannan yayi wanka soso da sabulu bai dade ba ya fito yana goge jikinsa yana kallon fuskarta da gashin kanta mai tsantse da sheki komai nata mai kyau ya furta hakan a kasan ranshi ..
Jallabiya ya ciro wani design din yasa ya karasa kibabben gurin sallarsa ya soma gabatar da sallah gabansa na faduwa , yana matukar fargaba da tsoron mahalincisa a duk sanda zai yi sallah sai yaji gaba-daya komai ya kwance masa ,yasan abinda yake aikatawa bai da kyau har yana jin tamkar ibadar da yake ma ba'a amsa ,yayinda take zuciyarsa ta kawar masa da wasi wasin data shiga ya dinga yi mata naci da karfafa gwiwar da ana amsa har ya idar zuciyarsa rawa take ya mike ya dawo inda take kwance tana sauke numfashi hannuwansa duka ya kai jikinta ya d'agota ta zube jikinsa ta lafe tare da turo masa karamin bakinta gaba , bakinsa ya kai cikin kunneta "ki tashi kiyi sallah lokaci ya tafi mika tayi ajikinsa wanda ya haddasa masa jin wani irin shock , "uhm zanyi zuwa anjima bacci nake ji jikina duk ciwo yake min ,gefen kunneta ya ciza da dan karfi ta saki qara tana sake shigewa jikinsa "dole ki tashi kiyi sallah me kika yi da kika gaji ya k'arasa maganar yana busa mata iskan bakinsa take tsigar jikinta suka mike sake turo masa bakinta tayi tana kokarin buɗe bakinta taji yayi sama daita ya shige bathorrom daita ya sakata a bathtube "ba'a lattin sallah a gidana oya kiyi alwala ya juya ya koma d'aki bayan kamar minti uku ya dawo hannunsa rike da jallabiya ya ajiye mata ya sake fita ..
Jiki a mace ta fito tana kallon inda yake zaune rigingine da gado ta isa inda taga dadduma ta tada sallah bayan ta idar ta koma dayan bangaren da yake ta zauna "good morning ?"morning ya faɗa atakaice batare daya kalleta ba "ya kamata na koma gida ina so..
"zaki tafi nan da wasu awani dan zamanki bashi da wani amfani , ya fada yana mik'ewa akan katifa bata sake cewa komai ba ta zame ta kwanta tana runtse idanunta "komai cikin gadara da isa da nuna rashin kulawa ta fadi haka a kasan ranta .......
ya mike ya fita daga dakin zuwa wani dakin , yayi shirin fita operation dinsa tsaf ya shirya cikin bakaken kaya riga da wonda na suit ya ɗauki bindigarsa pistor guda har guda biyu ya soke ajikinsa yabi jikinsa da turare mai sanyi kamshi sannan ya fito zuwa babban parlou'n gidan yana d'aura agogo a tsintsiyar hannunsa turus yayi ganin jabir kamil jubi da Anas zaune suna tautaunawa akansa ganinsa yasa suka mike suna kallonsa , kallonsu shima yayi daya bayan daya yana tabe baki sannan yace "ku kuma fa ? "a tare suka bude baki mun zo ne akan wannan fitartaka bama son ka fita aikin nan dan Allah ka hakura ,"me yasa bakwa gajiya da magana ɗaya nifa wannan ba sabon abu bane agurina,",Koda yaushe kana jayayya damu akan ra'ayinka amman akan wannan dole mu fi karfin ka "karfin wa ? ya furta yana musu wani irin kallon kasan ido
"Duk ma abinda zakuce kuce but I must face tanko gote zasu sake magana ya dakatarsu har zai fita yaji jikinsa yayi masa wani iri a hankali ya juya ya koma ciki ,kai tsaye d'akin da tanweer take ya shiga ya hawo har saman gado ya shige jikinta yana kissing din bayan wuyanta jinta yake kamar matarsa ya zira harshensa cikin kunneta sannan ya kamo hannunta cikin nashi "zani wani aiki mai mahimmanci da zarar na dawo zan kai ki gidanku ajiyar zuciya ta sauke tana juyo ta zuba masa ido batare da tace komai ba shima bai sake furta komai ba wani iri suka ji ajikinsu a lokacin da kwayar idanunsu suka tsarke cikin juna ,bai sake cewa komai ba ya fice tabi bayansa da kallo kamar ta hanashi fitar duk da batasan inda zashi ba , har lokacin su Anas suna tsaye ya nufi haraban gidan suka biyo bayansa suna masa magana amman ko tari bai yi bare su saka rai zai amsa musu , kai tsaye dakin ajiye makamansa ya nufa ya dibi harsashi da kudi masu yawa ya ɗauki keyn motarsa city ya fito still suna biye dashi ya karasa inda aka tanada domin ajiye motocinsa ya danna key din hannunsa ya bude kofa mazaunin direba ya shiga ya tayar mai gadi na ganin hancin motarsa ya bude masa, ya cilla motarsa waje .
mutanen dake tsaye jiran fitowarsa suka mike tsaye ,kamar ba zai tsaya ba sai kuma ya tsaya batare daya kashe motar ba ,yayi warning glass din motar ya ciro bandir din kudi yan dubu day day ya soma raba musu kamar yadda ya saba suka dinga amsa suna zuba masa ruwan addu'a da samun nasara yana kada kai ,sai daya sallamesu sannan ya dauki hanyar zuwa donping estate ..
"Taurin kai taurin kai mutun kamar mutanen farko duk abinda kaji ance ka barshi barinsa shine alkhairi duk kuma abinda zaka samu a duniya zaka bar shi jubi ya faɗa cike da taikaici da bakinciki taurin kan Jaguwa "wayyohlly Allah wallahi har na fara tausayawa yan'uwansa da halin da zasu shiga idan wani abu ya faru dashi kamil ya fada yana marairaice fuska , jabir yace " wallahi tunda ya soma shirin aikin nan naji ajikina babu nasara "muyi masa addu'a kawai Allah ya dawo dashi lafiya domin shine karfin gwiwarmu bamu taba samun saɓanin ra'ayi ba sai a wannan lokacin inji cewar anas daya fi kowa shiga damuwa " ameen suka had'a baki gurin fadar haka..
A hankali yake murza stearing yana tunanin yadda abubuwan zasu kasance gaba-daya ya gama tsara komai da yadda zai shiga ya fito har ya dauki titin da zai kai shi estate din ya karaso bakin get din estate din yayi parking ya ɗan dade sannan ya fito daga cikin motarsa yana gyara zaman suit d'insa kai tsaye gurin securitys din bakin get ya nufa suka gaisa a mutunce bazakace masa dan fashi ba bayan sun gaisa yace "ina son ganin Alhaji tanko gote ..
Daya daga cikin securitys ya leko daga cikin wani karamin daki yana dubansa ganinsa cikin shiga ta kamala ya koma ya zauna dayan yace "me ye sunanka na duba ko kana cikin list din masu son ganinsa ? Shiru yayi ya kasa magana yana ciza lip's d'insa na kasa security ya sake kallonsa yana tambayarsa "uhm don't worry bari na kirasa "better dan ba'a bawa Kowa damar shiga sai da izininsa wayarsa ya ciro kamar zai yi kira ya koma cikin motarsa ya zauna yana tunanin yadda zai shiga cikin sauki .
" Anas........"
jabir ya kira sunansa yana zama a gefensa "na'am jabir Anas ya amsa jiki a sanyaye" everything will be fine naga duk ka damu tunda jaguwa ya bar gidan nan "dole na damu jabir ina jinsa tamkar danuwana bana son wani abu ya sameshi bana son na rasashi yayi mgnr kamar zai zubar da kwalla "jaguwa ba kamar sauran mutane bane , gabad'aya alamuransa akwai lisssfi ,yana da kaifin kwakwaluwa bazai bari mu rasa shi ba saboda yasan muna son shi "jabir nasan da haka nasan yana son mu duk duniya bashi da aminan da suka kai mu but bansan me yasa yayi irin wannan taurin kan ba ,nayi kokari fahimtar dashi nayi komai akan ya bar wannan aikin amman yaki ya kasa fahimtata jabir zuciyata na cike da tsoro yanzu idan wani abu ya sameshi adalilin tango gote ya zanyi da rayuwata ? "Anas kana tsoro da tausayinsa with reason nima zuciyata tana cikin damuwa amman abinda na lura dashi yana sane so yake mu rasa shi inji cewar kamil wallahi idan wani abu ya sameshi bazan taba yafe masa ba yayi maganar yana goge hawaye "ba haka bane kamil Anas ya fada shima hawaye ne cike da idanunshi "zai dawo zai dawo anas ya dinga maimaitawa zai dawo da kafafunsa domin shi din ba mutun bane kamar sauran mutane mutun ne mai matukar amfani ga rayuwar mutane yayi handling din matsaloli a rayuwar data gabata ina da tabbacin zai dawo da kafafunsa suka rungume juna suna kuka ..
****
Alhaji tanko gote zaune a cikin tangamemen parlou'n sa daya ji kayan more rayuwar duniya tare da manya abokansa kowane hannunsa rike da glass cup suna kurban ruwan win yayinda gabansu table ne dake dauke da kayan itatuwa kala dabam dabam,tun daga kan ginin gidan da tsarin da'aka bi dashi za ka san mamalakin gidan attajirin ne,gidan zagaye yaje da flowers sannan yafi Kowane gida dake cikin estate din kyau da tsaruwa .
shewa ne ke tashi acikin parlou'n "mutunen da zasu ce meye namu acikin lamuran kasar nan ina tunanin mutanen sun tabbata dakikai ne , domin daga kasar nan tamu har zuwa kashen ketari sunanmu ya zagaya sannan a san da zamanmu, maga Wanda ya isa yace meye namu acikin lamarin kasar nan bayan mune gwanati "wannan haka ne inji cewar Alhaji amadu dan iya wanda ke fuskantar alhj tanko gote "muna da tarin kudi muna da tarin mutane muna da hanyoyi daban daban akwai connection me muke so acikin kasar nan da bamu samu ba da har wasu zasu dinga cewa meye namu aciki ? "babu ma wanda ya isa domin mune gwanati kuma ko ana so ko ba'a so dole a dama damu kuma muyi abinda muke so "wannan gaskiya ne ...
A hankali ya bude kyawawan idanunshi ya daura akan ƙaramin agogon dake ajiye akan abun gado, karfe takwas ya gani har ta wuce da wasu yan mintuna tsaki yaja saboda ya makara idan akwai abinda ya tsana bai wuce makara gurin sallah ba , ya kwantar daita tare da lullu'beta da bargo ya mirgina ya sauko ya janyo towel ya d'aura ajikinsa cike da natsuwa ya shiga bathorrom , bathtube ya shiga ya tsaya ya soma sakarwa jikinsa ruwa, wankar tsarki yayi tukuna domin tsaftace jikinsa sannan yayi wanka soso da sabulu bai dade ba ya fito yana goge jikinsa yana kallon fuskarta da gashin kanta mai tsantse da sheki komai nata mai kyau ya furta hakan a kasan ranshi ..
Jallabiya ya ciro wani design din yasa ya karasa kibabben gurin sallarsa ya soma gabatar da sallah gabansa na faduwa , yana matukar fargaba da tsoron mahalincisa a duk sanda zai yi sallah sai yaji gaba-daya komai ya kwance masa ,yasan abinda yake aikatawa bai da kyau har yana jin tamkar ibadar da yake ma ba'a amsa ,yayinda take zuciyarsa ta kawar masa da wasi wasin data shiga ya dinga yi mata naci da karfafa gwiwar da ana amsa har ya idar zuciyarsa rawa take ya mike ya dawo inda take kwance tana sauke numfashi hannuwansa duka ya kai jikinta ya d'agota ta zube jikinsa ta lafe tare da turo masa karamin bakinta gaba , bakinsa ya kai cikin kunneta "ki tashi kiyi sallah lokaci ya tafi mika tayi ajikinsa wanda ya haddasa masa jin wani irin shock , "uhm zanyi zuwa anjima bacci nake ji jikina duk ciwo yake min ,gefen kunneta ya ciza da dan karfi ta saki qara tana sake shigewa jikinsa "dole ki tashi kiyi sallah me kika yi da kika gaji ya k'arasa maganar yana busa mata iskan bakinsa take tsigar jikinta suka mike sake turo masa bakinta tayi tana kokarin buɗe bakinta taji yayi sama daita ya shige bathorrom daita ya sakata a bathtube "ba'a lattin sallah a gidana oya kiyi alwala ya juya ya koma d'aki bayan kamar minti uku ya dawo hannunsa rike da jallabiya ya ajiye mata ya sake fita ..
Jiki a mace ta fito tana kallon inda yake zaune rigingine da gado ta isa inda taga dadduma ta tada sallah bayan ta idar ta koma dayan bangaren da yake ta zauna "good morning ?"morning ya faɗa atakaice batare daya kalleta ba "ya kamata na koma gida ina so..
"zaki tafi nan da wasu awani dan zamanki bashi da wani amfani , ya fada yana mik'ewa akan katifa bata sake cewa komai ba ta zame ta kwanta tana runtse idanunta "komai cikin gadara da isa da nuna rashin kulawa ta fadi haka a kasan ranta .......
ya mike ya fita daga dakin zuwa wani dakin , yayi shirin fita operation dinsa tsaf ya shirya cikin bakaken kaya riga da wonda na suit ya ɗauki bindigarsa pistor guda har guda biyu ya soke ajikinsa yabi jikinsa da turare mai sanyi kamshi sannan ya fito zuwa babban parlou'n gidan yana d'aura agogo a tsintsiyar hannunsa turus yayi ganin jabir kamil jubi da Anas zaune suna tautaunawa akansa ganinsa yasa suka mike suna kallonsa , kallonsu shima yayi daya bayan daya yana tabe baki sannan yace "ku kuma fa ? "a tare suka bude baki mun zo ne akan wannan fitartaka bama son ka fita aikin nan dan Allah ka hakura ,"me yasa bakwa gajiya da magana ɗaya nifa wannan ba sabon abu bane agurina,",Koda yaushe kana jayayya damu akan ra'ayinka amman akan wannan dole mu fi karfin ka "karfin wa ? ya furta yana musu wani irin kallon kasan ido
"Duk ma abinda zakuce kuce but I must face tanko gote zasu sake magana ya dakatarsu har zai fita yaji jikinsa yayi masa wani iri a hankali ya juya ya koma ciki ,kai tsaye d'akin da tanweer take ya shiga ya hawo har saman gado ya shige jikinta yana kissing din bayan wuyanta jinta yake kamar matarsa ya zira harshensa cikin kunneta sannan ya kamo hannunta cikin nashi "zani wani aiki mai mahimmanci da zarar na dawo zan kai ki gidanku ajiyar zuciya ta sauke tana juyo ta zuba masa ido batare da tace komai ba shima bai sake furta komai ba wani iri suka ji ajikinsu a lokacin da kwayar idanunsu suka tsarke cikin juna ,bai sake cewa komai ba ya fice tabi bayansa da kallo kamar ta hanashi fitar duk da batasan inda zashi ba , har lokacin su Anas suna tsaye ya nufi haraban gidan suka biyo bayansa suna masa magana amman ko tari bai yi bare su saka rai zai amsa musu , kai tsaye dakin ajiye makamansa ya nufa ya dibi harsashi da kudi masu yawa ya ɗauki keyn motarsa city ya fito still suna biye dashi ya karasa inda aka tanada domin ajiye motocinsa ya danna key din hannunsa ya bude kofa mazaunin direba ya shiga ya tayar mai gadi na ganin hancin motarsa ya bude masa, ya cilla motarsa waje .
mutanen dake tsaye jiran fitowarsa suka mike tsaye ,kamar ba zai tsaya ba sai kuma ya tsaya batare daya kashe motar ba ,yayi warning glass din motar ya ciro bandir din kudi yan dubu day day ya soma raba musu kamar yadda ya saba suka dinga amsa suna zuba masa ruwan addu'a da samun nasara yana kada kai ,sai daya sallamesu sannan ya dauki hanyar zuwa donping estate ..
"Taurin kai taurin kai mutun kamar mutanen farko duk abinda kaji ance ka barshi barinsa shine alkhairi duk kuma abinda zaka samu a duniya zaka bar shi jubi ya faɗa cike da taikaici da bakinciki taurin kan Jaguwa "wayyohlly Allah wallahi har na fara tausayawa yan'uwansa da halin da zasu shiga idan wani abu ya faru dashi kamil ya fada yana marairaice fuska , jabir yace " wallahi tunda ya soma shirin aikin nan naji ajikina babu nasara "muyi masa addu'a kawai Allah ya dawo dashi lafiya domin shine karfin gwiwarmu bamu taba samun saɓanin ra'ayi ba sai a wannan lokacin inji cewar anas daya fi kowa shiga damuwa " ameen suka had'a baki gurin fadar haka..
A hankali yake murza stearing yana tunanin yadda abubuwan zasu kasance gaba-daya ya gama tsara komai da yadda zai shiga ya fito har ya dauki titin da zai kai shi estate din ya karaso bakin get din estate din yayi parking ya ɗan dade sannan ya fito daga cikin motarsa yana gyara zaman suit d'insa kai tsaye gurin securitys din bakin get ya nufa suka gaisa a mutunce bazakace masa dan fashi ba bayan sun gaisa yace "ina son ganin Alhaji tanko gote ..
Daya daga cikin securitys ya leko daga cikin wani karamin daki yana dubansa ganinsa cikin shiga ta kamala ya koma ya zauna dayan yace "me ye sunanka na duba ko kana cikin list din masu son ganinsa ? Shiru yayi ya kasa magana yana ciza lip's d'insa na kasa security ya sake kallonsa yana tambayarsa "uhm don't worry bari na kirasa "better dan ba'a bawa Kowa damar shiga sai da izininsa wayarsa ya ciro kamar zai yi kira ya koma cikin motarsa ya zauna yana tunanin yadda zai shiga cikin sauki .
" Anas........"
jabir ya kira sunansa yana zama a gefensa "na'am jabir Anas ya amsa jiki a sanyaye" everything will be fine naga duk ka damu tunda jaguwa ya bar gidan nan "dole na damu jabir ina jinsa tamkar danuwana bana son wani abu ya sameshi bana son na rasashi yayi mgnr kamar zai zubar da kwalla "jaguwa ba kamar sauran mutane bane , gabad'aya alamuransa akwai lisssfi ,yana da kaifin kwakwaluwa bazai bari mu rasa shi ba saboda yasan muna son shi "jabir nasan da haka nasan yana son mu duk duniya bashi da aminan da suka kai mu but bansan me yasa yayi irin wannan taurin kan ba ,nayi kokari fahimtar dashi nayi komai akan ya bar wannan aikin amman yaki ya kasa fahimtata jabir zuciyata na cike da tsoro yanzu idan wani abu ya sameshi adalilin tango gote ya zanyi da rayuwata ? "Anas kana tsoro da tausayinsa with reason nima zuciyata tana cikin damuwa amman abinda na lura dashi yana sane so yake mu rasa shi inji cewar kamil wallahi idan wani abu ya sameshi bazan taba yafe masa ba yayi maganar yana goge hawaye "ba haka bane kamil Anas ya fada shima hawaye ne cike da idanunshi "zai dawo zai dawo anas ya dinga maimaitawa zai dawo da kafafunsa domin shi din ba mutun bane kamar sauran mutane mutun ne mai matukar amfani ga rayuwar mutane yayi handling din matsaloli a rayuwar data gabata ina da tabbacin zai dawo da kafafunsa suka rungume juna suna kuka ..
****
Alhaji tanko gote zaune a cikin tangamemen parlou'n sa daya ji kayan more rayuwar duniya tare da manya abokansa kowane hannunsa rike da glass cup suna kurban ruwan win yayinda gabansu table ne dake dauke da kayan itatuwa kala dabam dabam,tun daga kan ginin gidan da tsarin da'aka bi dashi za ka san mamalakin gidan attajirin ne,gidan zagaye yaje da flowers sannan yafi Kowane gida dake cikin estate din kyau da tsaruwa .
shewa ne ke tashi acikin parlou'n "mutunen da zasu ce meye namu acikin lamuran kasar nan ina tunanin mutanen sun tabbata dakikai ne , domin daga kasar nan tamu har zuwa kashen ketari sunanmu ya zagaya sannan a san da zamanmu, maga Wanda ya isa yace meye namu acikin lamarin kasar nan bayan mune gwanati "wannan haka ne inji cewar Alhaji amadu dan iya wanda ke fuskantar alhj tanko gote "muna da tarin kudi muna da tarin mutane muna da hanyoyi daban daban akwai connection me muke so acikin kasar nan da bamu samu ba da har wasu zasu dinga cewa meye namu aciki ? "babu ma wanda ya isa domin mune gwanati kuma ko ana so ko ba'a so dole a dama damu kuma muyi abinda muke so "wannan gaskiya ne ...