← Book details Kuskuren Baya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 37 OF 160

Sashe 37

Kuskuren Baya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Dan Allah kawata ki cire kishin nan a ranki mude bukatarmu ta biya  ya rabu da yarinyar shine abinda muke so  ,  har suka k'araso tasha magana daya dai suke yi blessing na kokarin shawo kan Zahra , shiru  zahra tai taki cewa komai zuciyarta na tuttukin bakinciki Adnan zai kusanci tanweer Kuma shi zai amshi budurcinta.
bangaren tanweer kuwa   taki cin  abinci,  yadda ya   kawo mata abincin   jiya  haka ya  fitar dashi   bata ci ba ,ai ko shima   ya  hau  dokin zuciya  yaki bin ta kanta bare ya  rarrasheta ." duk yadda blessing ke Jan  zahra da hira  acikin mota ta kasa cewa komai har suka sauka a lagos   kowacce ta kama gabanta gbdy Zahra ta  kasa samun kwanciyar hankali sam bata ji zata iya wannan kasadar sai  tayi kmr ta kira boka  tace ta fasa  aikin sai Kuma  ta fasa   ."

*****
Zaune jaguwa yake  cikin baban falonsa system ne a gabansa yana aiki   eku ya shigo tare da rusunawa ya gaishesa ya amsa batare daya d'ago ba eku ya  soma magana cike da ladabi "boss kamar ka manta da wancan mutumin "  Jaguwa ya d'ago ya  kallesa  a tsanake yana bukatar qarin bayani "wancan mutumin dakace mu dauko a Rita Lori hotel mu  killace maka shi " sai lokacin jaguwa ya tuna ya lumshe idanunshi  "Yana Ina ne ?"yana boys quarter ya gyada Kanshi kawai ya cigaba da abinda yake eku  bai  wuce  ba sai da jaguwa ya gama abinda yake ya mike yana tafiya kamar baya son taka kasa yayinda eku ke biye dashi har suka k'araso bakin kofar d'akin da alqali yake , eku yayi saurin  bude  masa kofar  d'akin , alqali najin motsin mutane ya shiga zare Ido jaguwa ya tsura masa Ido ya rame sosai  rama ta tashin hankali acikin kwana biyu  da yayi wanda idan ka kallesa bazaka sake marmarin kallonsa ba duk ya fita haiyacinsa, zaune yake jugun hannunwansa da kafafunsa duk kulle su da handcuff kamar wanda yake prison a hankali  jaguwa  ya shiga Taku a hankali  yana masa wani wulakantaccen kallo sannan ya tsaya a tsakiyar d'akin  yana cewa"waye Kai menene yasa kake bibiyata ?alqali da bakinsa ya bushe sosai ya fara magana cikin wahala "babu dalilin da yasa na  bibiyeka ya karasa maganar cikin tsananin tashin hankali .
"waye Kai ?"shiru alqali yayi ya kasa cewa komai jaguwa ya juya ya soma tafiya "Ina ganin azabar yunwar da'aka masa  bai ishesa  ba ka cigaba da barinsa babu ci babu sha har ya zamo sanadinsa "  alqali wanda muryarsa ta fara dashewa babu karfi a tattare dashi yace "kayiwa Allah kayi hakuri na tuba  "jaguwa ya cigaba da tafiya batare da juyo ba  "idan na fada maka bazaka kasheni ba ?"yayi masa bmbyr a gigice cak jaguwa ya tsaya tare da goya hannuwansa duka  a baya ya juyo
ya tsura masa Ido alamun yana sauraronsa "ni ..ni  ...sai Kuma yayi shiru yaji tsoron sheida masa cewar shi din jami'in sirri ne  " kayi hakuri dan Allah ka tausaya min nayi kuskure bazan sake ba "runtse idanu  jaguwa yayi  ,ba dan baya son aikata kissa a rayuwarsa ba da babu shakka da sai  ya shake wuyan  wannan
mutumin da hanunsa har sai ya mutu
"kaga nayi  kama da wanda za'a bibiyi rayuwarsa for the  last time  ka fad'a min wanda yasa ka bibiyeni?  yayi masa tmbyr yana hade fuskarsa kmr hadari.  shiru  alqali yay ya kasa magana Dan Bai San abinda zai ce ba har kusan minti biyar Yana tsaye yana jiransa  ,eku ya Ciro karamar pestol  ya saita gefen brain dinsa "na baka minti biyu ka fadi Wanda ya sakaka  kafin na tarwatsa brain  dinka na aikaka lahira  "wa ..wallahi babu kowa Ina tafiya ne na gansa tare da yarinyar minister of health da ake nema  shine na dinga binsa a baya naga Inda zashi daita wallahi  byn wannan babu Wanda ya aikoni .
"ka cigaba da ajiyarsa anan har sanda zai fadi  gskiyar  wanda ya aikosa sannan ka ciyar dashi da  gari zalla da ruwa ,ruwan ma kwatan tea cup haka ma gari muddin yayi  wata bai fadi Wanda ya aikosa ba  ka tashesa aiki yana gama fad'ar haka ya fice daga daki  haka ma eku ya nufi kofar fita kmr wani  zautacce alqali ya rarrafa da gwiwawinsa   yana k'okarin riko ka'fafun  eku Amman Ina tuni ya fice ya maida kofar ya rufe cikin rashin tausayawa,   hawayen danasani suka silalowa alqali ya fara zubar da hawaye yana adduar Neman mafuta "me yasa ka biyosa gashi ka jefa rayuwarka cikin hatsari kuka yake sosai  kamar karamin yaro."

******

"Wai  waye wannna jaguwa  din ne  ? waye km ?.gbdy sai da tanko gote ya kira sunayensu d'aya  bayan d'aya ka  amsa min tambayata boka " ya san sunansu ne  a bakin wasu daga cikin mufukan' yansanda da sukayi attacking  dinsu a wancan satin ". shiru bokansa    yayi  yana dube dube acikin kasa ,abubuwa   da yawa  ya gani akan jaguwa km abun ya balain tsoratar dashi dan har wani gumi ya had'a da  kyar yayi jarumtar yin magana "wannan  yaron da Jamar'sa  rikakkun  y'an fashi da makami ne  da suka ga gari kowa  acikin garin nan yana da karfin da zai iya karawa da kowa acikin garin nan ,haka yana da karfin da zai iya shiga duk Inda yaso yayi sata  batare da an dakatar dashi ba , yafi karfin kowa duk yadda kake tunanin yan fashi sun  zarta tunaninka basa ji basa gani akan aikinsu  sai dai abinda na gani a dubana  shi jaguwa  yana fanshinsa ne akan masu kudi da azzaluman kasar nan , yana da hatsarin fuskanta it's not easy to be known as the CEO of armerobber's association .
wannan ya wuce da tunaninka ranka shi dade karka bata lokacinka gurin sanin ko shi waye ko matakin d'auka  akanshi  tunda har ya barka da ranka da lafiyarka sai mu godewa Allah domin shifa satarsa me dalili ne Kuma ya dade acikin harkar Kuma shi kad'ai yasan abinda ya taka wanda yasa ya gagari kasa da kasa har da  jami'an tsaro suka kasa kamashi tanko gote ya numfasa kana yace "zan so yayi aiki a karkashina domin irinsa nake nema "bazai had'a Kai da Kai  ba dan baya zalinci burinsa ya taimakawa talakawa marasa  galihu Kai Kuma burinka ka danne hakin mutane da talakawa  "wai boka ya kake min  magana haka  ne ? " kayi wani Abu da zai kawo kanshi gareni "babu abinda zan iyayi domin duba  taurarinsa ma kawai zai iya sa mutun cikin tashin hankali, kaima idan baka cire hannunka akansa ba zaka iya rasa komai naka jin abinda boka yace yasa tanko gote  shiga damuwa bai sake cewa komai ba ya kakkabe bababan rigarsa ya baro gurin boka da zumar zai nemi had'in kan jaguwa ta kowani hali ".   

*****
Jaguwa na zaune  tare da abokinsa da yaransa a gurin  shakatawarsa   gabansu  kwalban giya ne yayinda kowannensu hannunsa ke rike da karan sigari har  jaguwa  suna tautaunawa akan sabon aikin da zasu fita zuwa garin  Ogun state sai ga me gadinsa ya rusuna ya gaishesa tare da cewa "ga wannan dattijon daya zo neman taimakonka   ya dawo ranka shi dade" "shi da nace ya dawo karshen sati  amman dai   shigo dashi kawai "  mai  gadi ya juya da sauri jaguwa ya kashe sigarin hannunsa  dan yana matukar jin kunyar wani yaga yana shan sigari  eku tattara gurin nan  kafin azo da  dattijon nan take yabi umarninsa .ko cikakken minti biyar  ba'a yi  ba sai ga me gadi ya dawo  tare da mutumin da yaronsa wanda bai wuce shekara talatin ba  dattinjo na kokarin rusunawa 
jaguwa ya tsaidashi  yana nuna masa gurin zama "ka zauna baba  dattijon ya zauna a Inda ya nuna masa  yana rawar  jiki, gbdy su jubi suka gaishesa ya amsa yana Saka musu albarka "d'ana ga yarona  nazo dashi "jaguwa ya waigo ya  kalli Inda  yaron  yake  tsaye cikin wasu kod'ad'un kaya marasa fasali da sauri  matashin saurayin ya dan rusuna ya  gaishesa ya amsa da Kai tare da cewa " ya sunanka sannan wani course ka karanta ? " sunana aliyu Ahmed abinda na karanta lissafi wato  accounting .ya bashi amsa cike da girmama.
shiru jaguwa  yayi yana nazarin yaro kafin daga baya yace  "shikenan zaka zauna damu  ka zama dan aikenmu kafin  lokacin da zan  samo maka aiki inshallahu , dattijon najin haka ya fara hawaye yana godiya " na gode na gode Allah yayi maka albarka "karka damu baba mu daman aikinmu kenan taimakawa marasa shi ,aiki kuwa ka fara hasasho  ganinsa cikin  jerin ma'akatan banking   kasar nan  yana gama fad'ar haka yasa aka dibo kudi masu yawa aka bawa dattijon "baba ga wannan   kudin kaje dashi kayi bukatunka dasu, sosai dattinjo ya zube yana godiya kafin daga baya yay sallama dasu ya wuce ya bar d'ansa ."

******
D'akin  taro ne dake cike da manyan  jami'an tsoro kowannensu  sanye da kankinsu  na aiki  police, yayinda  gabansu  ruwan roba ne mai sanyi   da abun   magana  a hankali cp ya fara magana cikin tsadaddan turancinsa "
Daga  ashirin da biyar ga watan daya na wannan  shekarar ta  2021 zuwa ga karshen shekarar shadaya  da muke ciki  an samu farmarki ta'addanci a qalla ashirin da biyar a cikin garin nan, duk  da k'okarin  da jami'an tsoro keyi akan suga sun kama wadan nan  yan fashi abun ya faskara wanda ni a nawa tunanin ina ganin akwai manyan kasan nan dake mara musu baya,  taya  zamu samu nasarar kama wannan  mutumin dake jagoransu wanda shi ke shirya komai  na ta'addanci   ? cp ya karasa maganar yana kallon hoton jaguwa dake ajiye akan makeken table din gabansa ." yanzu haka wannan shine tantiri na biyu da ake nema acikin kasar nan idan kuma acikin garin nan ne shine na daya , jaguwa  kenan   duk wani sata da'ake wa manyan kasar  nan da  yan siyasa da hannunsa aciki abun mamaki yadda wasu daga cikinmu suke bashi kariya ta hanyar sanar masa da halin da'ake aciki,  a offishin hukumar tsoro kuma suna yi masa duk wani alfarma daidai da wani mai fada aji a kasar  nan ".
Chapter 37 · 0% Book details