← Book details Kuskuren Baya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 41 OF 160

Sashe 41

Kuskuren Baya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

gudu jaguwa yake sosai akan titi isolo gbdy ya nemi natsuwarsa ya rasa ji yake kmr zuciyarsa zata kama da wuta haka ne ma yasa yaga kamar baya gudu tsaki yake taja akai akai duk jikinsa tsuma yake kwakwa luwarsa  ta  hargitse kamar wanda aka aikowa da sakon mutuwar d'aya daga cikin ahlinsa , doguwar tafiya yayi ya k'araso daf  da unguwarsu
tun kafin ya k'araso ya soma Kiran number sadiq kaninsa  kira uku ya d'auka hankalinsa a matukar tashe "ka fito ka bude min get"  abinda ya fad'a kenan ya katse Kiran yana karasowa kofar gidansu sadiq har ya fito yana ƙoƙarin bude get da sauri ya bud'e murfin motar ya fito sadiq ya bashi hanya ya shiga ya maida get ya rufe "Lafiya father  kazo da tsakar daren nan? "lafiyar nan dai da sauki sadiq, ya fad'a yana dosar kofar part din ammi wacce tuni ta farka sakamakon jin muryarsa cikin bacci  dan window dakinta na daga tsakar gidan "Adnan ! ta kira sunansa a rud'e tana durowa daga kan bed dinta  ta fito tana k'okarin bud'e kofar tana sake Kiran sunansa ya amsa da" Na'am ammina Ina ganye magariyar da kika ta'ba nuna min ana yiwa gawa wanka dashi ? yana nan Lafiya kake nemansa da tsohon daren nan waye ya mutu ?ta tambayesa a rude "babu wanda ya mutu wani za'ayi amfani dashi domin karya sihiri "   daga haka bata  sake  furta Komai ba ta juya ta koma cikin d'akinta da sauri sai lokacin sadiq ya sauke naunayen ajiyar zuciya Jin ba wani abu bane "suna tsaye ammi ta fito ta mika masa bakar ledar da gayen ke ciki ya amsa ya juya da sauri yana ce mata sai da safe ",Allah ya tashemu Lafiya Allah ya  tsareka ta fad'a tana kallon bayansa  "Ameen" ya amsa yana k'arasa fita daga gidan sadiq ya biyo bayansa ya kulle get ."

Wannan karon ba k'aramin gudun wasa yayi ba sai dai yana kawowa titin da mutun zai hau isalo road ya  karya stearing motarsa ya d'auki titin da zai Kai shi lawansi road adalilin faduwar gaba  daya  ji ya dirar masa  ,ya  Kai hannunsa d'aya  ya  kunna  wutar motar ta ciki ya Kalli zoben  hannunsa  nan yaga ya koma baki  daga ruwan zuman da yake iska ya furzar yana girgiza Kai ,gudu   yayi   sosai  cikin  kankanin lokaci  ya k'araso unguwar tun kafin ya k'araso get din gidan yake hon mai gadi ya bud'e masa ya shiga ya fito da mugun sauri daga cikin mota .
a falo ya wuce su anas suna ganinsa suka biyo bayansa Kai tsaye kitchen ya shiga suna kallonsa ya d'auki karamar roba ya tsiyaya ruwa aciki ya nufi  falonsa ya wuce bedroom dinsa kamar su biyosa sai Kuma suka tsaya cirko cirko suna zagaye falon, can suka ji ya kulle kofar nan suka fita d'aya byn daya ban da anas da ya nemi guri ya zauna zaman jiransa ."

Yayi duk abinda baba yace ya tofa acikin ruwan sannan yayi sama da jallabiyarsa ya hau kan gadon tana kwance tamkar matacciya sai dai zuwa yanzu babu wannan hayakin jikinsa na rawa ya sake Kiran layin baba yana dauka yace "baba babu wannan hayakin yanzu "okay to to shikenan ya fad'a a rud'e ya ajiye wayar ya tattarota zuwa jikinsa ya mannata a gefensa ya bud'e bakinta hakoranta sun cije guri d'aya ,a hankali ya dinga shafa mata ruwan maganin a fuska zuwa ilahirin jikinta yafi karfin awa d'aya yana bin jikinta da ruwa sannan tay atishawa mai karfi  sai dai idanunta a runtse suke ....

Naunayen ajiyar zuciya ya sauke idanunshi na kanta shi kad'ai yasan irin farinciki daya tsinci kanshi da numfashinta ya dawo gangar jikinta  ya rungumeta gam ajikinsa yana jin wani sanyin dadi na ratsashi ,
tausayinta  ne ya cigaba da ratsashi dan duk wani abinda ya sameta shine ya jawo mata, tana zaman zamanta tare da iyayenta ya daukota  "Allah sarki a she ba laifinki bane "a she tursasaki akayi? " me yasa ? waye wanda yayi wannan aiki ?" me yarinyar mutane tayi muku kuka sa na zama silar rabata da budurcinta ? "shikenan Kunsa  na mayar daita bazawara alhalin bata cancanci hk ba ,kunsa nayi mata  tabon da har abada bazai gogu ba , wannan abu bai min dadi ba," me yasa  tun tuni ban fahimci abinda ke tattare dake ba? wasu hawayen tausayin ta ne suka shiga zubo masa ."

da qunar zuciya ya sake  matsowa jikinta ya riko hannunta cikin nashi yana wani irin kuka  yana duban  jikinsa daya  kusanceta dashi "na Kusanceta da jikina "na zamo silar yi mata tabo a rayuwarta .." me yasa  ban fahimceta ba na Kusanceta ? why why why Adnan !!! ? ya zabura ya mike tsaye tamkar mahaukaci yana hargagi ya shiga buga k'ansa da bagon d'akin yana nadamar abinda yayi mata "kafin kace me tunin jini ya balle a goshinsa ya shiga tsiyaya ya d'auki lokaci yana kukan nadama Yana kallon jikinsa yana tunanin cikin yan matansa wace wacce zata iya wannan  danyen   aikin  ? babu wacce  tazo  masa arai sai zahra ...."
ita kad'ai ce macen da zata iya komai akansa Kuma ita kad'ai ce ta gansa tare da tanweer ai kuwa babu shakka itace ,zata raina kanta a hannunsa ,
zan  bata  mamaki ,zai  mata abinda sai taji ta  tsaneshi a rayuwarta ya kai hannunsa  goshinsa  sakamakon dumin  da   yaji,  ya  kalla yatsansa  jini ya gani ya karasa ya d'auki tissue ya tsaya gaban mirrow ya goge sannan ya dawo ya d'auki rigarta yana kokarin saka mata nan ya ga digon  jini  had'e  da spam dinsa .
ya lumshe idanuwanshi qirjinsa na zafi abinda yafi tsanar mutane akanshi gashi shine ya aikata da kanshi ,cike da tashin hankali ya sauko  daga  kan bed din ya goge mata kasanta sannan ya zira mata riga ya  ɗauketa ya fito zuwa   falo   ya  wuce  anas zaune wanda ya zabga  tagumi yana ganinsa ya zabura  ya mike  ya biyosa  yana tambayarsa  jaguwa bai tsaya ba ya  nufi d'akinta  ya  shimfideta  akan   gado   idanunshi 
na  kanta  yana tsaye yana kallonta sai ga anas ya shigo d'akin cike da tashin hankali yana ganinsa ya janyo blanket ya lullu'beta yaja ya tsaya tare da rungume hannunwansa duka a qirjinsa cikin tsananin damuwa
anas    ya  zubawa tan Ido yana kallonta Ko cikakken minti biyar bai  yi ba sai ga jabir, jubi ,kamil sun shigo  .

duk  suka  zuba  mata  idanunsu suna kallonta  kowa da abinda yake sakawa a cikin  ransa a hankali  jaguwa ya runtse  idanunshi tare da Kai hannunsa daidai saitin zuciyarsa dake bugawa da sauri sauri ,anas ne yayi karfin halin tambayarsa abinda ke faruwa daita "daman itace babu Lafiya me ya sameta ?"aikin wancan tsinanniyar yarinya ce ya fad'a a tsawace "wacce yarinya kenan ?anas ya tambayesa a rud'e "wace ce banda waccen yar iskan zahra din asiri tayiwa yarinyar mutane amman na rantse da Allah sai naci ubanta inga uban daya tsaya mata acikin garin nan"take it easy jaguwa Kai ya akayi kasan tayi mata asiri ? tsaki jaguwa yaja da karfi idanunshi na kan tanweer dan yasan daman haka zai ce tunda baya ganin laifinta  .
a tsanake jabir yace "Allah ya kyauta yanzu dai me ye solution dan  naga kmr yarinyar bata numfashi ?ga tan nan dai tana numfashin sai dai ba sosai ba da kyar na samu numfashinta ya dan dawo wallahi muddin wani abu ya ta'ba lafiyarta zan shayar da Zahra mamaki inji cewar jaguwa ,gyada kai suka yi  gbdy sannan jubi , jabir ,kamil suka juya suka fita daga d'akin dan babu me iyawa dashi idan yana cikin fushi sai anas ."

"kayi hakuri jaguwa ba lallai abinda kake zargi akan zahra  ta aikata ba anas yayi mgnr yana dafashi a fusace ya buge masa hanun yana cewa "Daman nasan haka zakace  tunda kafi qaunar dani "no !no !! jaguwa saboda qaunar da zahra take maka yasa nake kulata taya ma zaka had'a matsayinka daita gsky karka sake min hk banaso Kai fa jinin jikina ne  ita Kuwa fa ?  jaguwa yayi shiru tare da  tsurawa tanweer Idanunshi wasu kwalla masu zafi suka zubo akan kuncinsa cike  da  takaici da nadamar abinda ya aikata mata, nadama irin wacce bata da amfani .
anas yayi matukar mamaki ganin jaguwa ya tasa tanweer gaba yana kwalla "lallai haka rayuwa take tana cike da abun mamaki "jaguwa ne yau yake kuka akan mace ? "Jaguwa !
Anas ya kira sunansa "yana jinsa yayi masa banza tamkar ba dashi yake mgn ba " kana mutuwar son yarinyar nan amman Kaki yarda da kana sonta , Kalli yadda kake zubar da hawaye akanta ,Kalli yadda tausayi mai hade da soyayya suke dawainiya da Kai ,ka yarda jaguwa kana sonta ka daina karyata zuciyarka , ka daina hasashen bazaka iya sonta ba, ita fa rayuwa kafi ni sanin rubutaccen alamari ne daga rabbi, hatta wannan Sana'ar tamu qaddara ce Killa da iyayenmu sun san zamu zo duniya mu kasance yan fashi wallahi da tuni sun kashemu da hannunsu ".yayi shiru yana dubansa "ka yarda Kuma ka amince kana sonta sai mu taru mu bar wannan rayuwar ,zamu tayaka inganta rayuwarka jaguwa domin sama maka farinciki .........."
"ka daina fad'a min haka anas banaso ji wannan kalmar  daga bakinka sau nawa zan fada maka tausayi ne ba so ba ?"yayi saurin karyata amininsa taya ma zai sota byn tanweer tafi karfinsa a aure, waye shi ,? waye yan'uwansa a fad'in kasar nan ?
duk da a yanzu ya taka matsayin da kudi ba matsalarsa bane amman yasan aurenta zai masa wahala, ya sake fuskantarta sosai yana Jin kamar yayi mata numfashi ,sosai  ya  fad'a kogin tunani hankalinsa ya bar duniyar da yake ciki ya Lula wata duniyar dabam ."
Chapter 41 · 0% Book details