Sashe 19
Kuskuren Baya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mutuwar tsaye suka yi gabad'aya suna kallonsa take bindigar hannun sp yusif ta subuce yayi saurin sake ja da baya idanunshi na kan jaguwa dake ƙoƙarin fitowa daga cikin motar, duk ilahirin jikinsu rawa yake har sp yusif wanda hankalinsa kusan yafi na sauran tashi dan yanayin bugawar zuciyarsa da yanayin tsoronsa sai ya baka mamaki tamkar ba jami'in tsaro ba "
cikin isa da izza jaguwa yake takowa zuwa inda sp yusif yake tsaye , ya tsaya nisa kaɗan dashi wanda bai fi taku biyu su fuskanci juna ba , idanunshi dake a lumshe ya ware su fesss akan sp yusif yana ciza gefen lip's d'insa na kasa,sp yusif ya kalli jaguwa kamar zai yi kuka saboda gigita da ganinsa a raye da yayi , tunda yake bai taɓa ganin abinda ya d'aga masa hankali irin wannan ba , "bai taɓa ganin dan adam din da aka yiwa harbi irin wanda suka yiwa motar jaguwa ba amman ya rayu har ya samu damar fitowa daga cikin motar cikin isa da izza ,tabbas yasan akwai wata a kasa ,wannan abu akwai tsarkakkiya acikinta "
Jaguwa ya had'iye dariyar sp yusif dake neman kufce masa saboda gabad'aya ya gama karantar yadda sp yusif da yaransa suka tsorata dashi ,dan gabadaya fuskokinsu ya sauya daga farinciki zuwa matsanancin tsoro da firgici kallo ɗaya zaka musu kasan suna cikin tashin hankali mai tsanani ...
"waye kai sp yusif karaye ? mutumin da cin hanci da rashawa ya aura tun kana ƙaramin mataki har zuwa yanzu daka taka wannan matsayin , har kake godiya ga Allah bisa samun nasara akaina "wani mataki ka taka tukunan ma a rayuwarka da zaka so kama mutun irina "?yayi masa tambayar yana kafeshi da kyawawan idanushi hade da sauke numfashi .
"Ya kamata kusan ko waye ni kafin ku dinga bibiyar rayuwata kana min kallon mamakin ko ? "Kana mamakin yadda na rayu ko ? Zan so bude maka hanyar da zaka fahimci ko wanene ni da kai da sauran tawagar dake bibiyar rayuwata amman bazan yi ba zan barku cikin duhu da wasi wasi da kai da waɗan nan yaran naka daka taso gaba " babu abinda zaku iya akan jaguwa sp yusif karaye , ba ku ba hatta shugaban tawagarku gaba-daya wato commition of police yayi kankatar da zai iya gaba da gaba dani bare kai da yaranka ya karasa maganar a fusace yana nuna sp yusif da yatsansa "
"a kasar nan kowa abinda ranshi yake so yake tare da aiwatar da son zuciya akan kaskantattu marasa galihu , "to bari kaji wani labari da baku isa ba dubunku ma basu isa suja da yaran jaguwa ba bare shi kanshi jaguwa , ni nan nafi karfinku nafi karfin hukuma kuma yanzu na sama addabar rayuwar manyan kasar nan ya karasa maganar yana dukan qirjinshi yana murmushi ......
"Anyway nasan daga inda shiriku yake kowanen daga cikinku ƙoƙarin raya kanshi da ahlinsa yake ba domin kare kasa da kasa kuke yin komai ba domin raya kanku kuke ,dana soma wannan aikin domin ɗaukar ran wani to da ina tabbatar maka kai ne mutun na biyu bayan wancan tantarin tanko gote ...."
duk wannan Maganar da yake yana yi yana jujjuya jikinsa ne kafin daga baya ya shafa fuskarsa ya cire fuskar dake manne da fuskarsa wata fuskar ta bayyana da tsananin kyau da sage zagaye daita "ka kalleni da kyau sp yusif muddin akaina zaka samu double promotion ina tabbatar maka bazaka taba samu ba har duniya ta nade saboda jaguwa mutun ɗaya ne mai fuska daban daban yana gama maganar ya zaro bindiga daga kugunsa ya saita daidai gwiwar sp yusif ya sakar masa bullet biyu a jere wata irin razananniyar qara ya saki tare da durkushewa a gurin "jaguwa ya nuna sa da bakin bindiga "bance ku daina farautata ba , sai dai ku shirya iya shiryawa kafin ku tunkareni yana gama fadar haka ya juya a fusace tamkar mayunwacin zaki yana taku kamar baya son taka kasa ya buɗe motarsa ya shiga yayi mata key a hankali motar ke motsawa tana moving gbdy suka bi bayan motar da kallon mamaki har sanda motar tayi musu nisa .....
*****
A natse yake murza stearing motarsa, lokacin daya shigo unguwar aguje su Anas dake tsaye a kofar gidan sukayi gurin motarsa suna murnar ganinsa, kanshi kawai ya girgiza yana murmushin sannan ya saita hancin motarsa get din gidan , kamil ya zundumawa mai gadi kira ganin zai 'bata musu lokaci yasa suka shiga sauri saurin buɗe masa tafkeken get din gidan yana gama karasa shigowa ko gama daidaita tsayuwar motar bai yi ba suka hau kiciniyar bude motar suka fito dashi tare da d'aga shi sama suna ihun jin dadin sake ganinsa "Winner ooo winner Winner ooo winner ,Winner we don win ooo winner
Pata pata we go win forever winner suka nufi babban parlou'n gidan dashi suka zaunar dashi akan kujera mai zaman mutun uku , Anas ya karasa da sauri ya bude fridge ya d'auko masa power horse mai sanyi ya bude ya mika masa yana zama kusa dashi cike da tsananin murna jubi ya d'auko ruwa mai sanyi ",wayyo Allah nah jaguwa nasan kasha wahala ko da ganin yadda motarka tayi " "babu wata wahala tunda gani a gabanku yanzu"
a tare sukayi dariyar jin dadi sannan sukace "Allah mun gode maka daka dawo mana da farincikinmu lafiya "shine abun godiya ya fada yana furzar da iska "gasky kai din na daban ne namijin duniya ,jaguwa ya ɗan lumshe idanunshi sannan ya gyara zamansa ya soma ƙoƙarin cire yar saman rigarsa Anas yayi saurin cire masa jubi ya dawo gabansa ya soma cire masa takalmin kafafunsa ya saura safa kallonsu kawai yake yana girgiza kai "kasan tun da ka bar gidan nan babu wanda ya sakawa cikinsa wani abu tsabar tashin hankali inji cewar jabir "
"uhmm bari jabir ban taba tsintar kaina cikin tashin hankali irin na yau ba wallahi da zarar na runtse idanuna sai inga kamar wani abu zai same shi anas ya fada yana shafa fuskar jaguwa ,ya ɗan juyo ya kalle shi yana haɗe rai "duk cikin murna dan ban maka kiss ba suka sa dariya gabadaya "yau fa akwai celebrate jubi ya fada yana dauko musu kwaban win ya jere a gabansu "kamar kuwa kun sani ,"ina zamu samowa jaguwa mai zafi data iya chilling fiyye da zahra ?
"ai babu wata mai zafi sosai data wuce zahra ita zan kira yanzu "zaro ido jaguwa yayi "lallai ku yanzu wannan shirmen ne a gabanku ni yadda zanga ammina nake tunani ba wannan shirmen ba "
"Ogbeni ejalo shaye jare Oti sele oppprr kpk Eyonla chuwale sir🙌🏽 se kinwa gbenusi no be atenu " zaka gun ammi amman amman dole zahra zata yi aiki "
A hankali Anas ya kira su eku remo cikin minti goma suka karasao suka shiga fito da buhuhun kudadde da jaguwa yazo dasu suna shigowa dashi daya bayan daya , yayinda su Anas ke zaune suna mamaki yadda har ya iya rabo tanko gote da wadan nan makudan kudaden shi kadai , cikin minti da bai wuce goma ba sukaji mai gadi yana kwankwasa kofa jubi ne ya tashi ya tsaya daga bakin kofa ya bude , cikin yaren turanci mai gadi yace "akwai wani bako da yake ta zuwa gidan nan yau shine zuwansa na biyar baya samun nasarar ganin oga yana fama da matsalolin rayuwa ne gashi yana da yarinya mara lafiya mai kimanin shekara goma tana igondo general hospital ,likitoci sunki bata kulawa sakamakon rashin kuɗi , kafin jubi yace wani abu jaguwa yayi gyaran murya , juyowa jubi yayi a hankali ya dawo inda suke ya tsaya yana duban jaguwa nuna masa wata yar kamara jaka mai zip yayi da hannunsa "zuba masa adadin da zai cika jakar nan ka bashi "yesssss boss an gama Allah yaja da nisan kwana ,jakar ya cika da kudi yayi ziping dinsa ya mikawa mai gadi da hanzari mai gadi ya amsa jakar ya rungume ya juya ya nufi kofar waje ya mikawa mutumin , mutumin na ganin kudin gabad'aya ya rude ya gigice ya soma wani irin kuka mai ban tausayi da taba zuciya,lallai baa rasa na allah koina kuma yadda aka bashi labari wannan matashin mai tsatsanin kirki da tausayi haka ne, take ya nemi mai gadi da yayi masa iso gurin mai gidan domin yi masa godiya , amman mai gadi yaki saboda sanin da yayi wa jaguwa baya son godiya ko kyauta yayi maka kace ka gode sai yace ka godewa Allah ,duk da ban samu ganinsa ba tabbas zan dangwama ina yiwa rayuwarsa addua domin allah ya buda masa kofofin farinciki kamar yadda yayi min , iri mutanen da ake so kenan masu taimako dan allah"
" karka damu ba kai ba duk wanda kaga yana bukatar taimako kana iya masa hanya wannna gidan gidan masu tallafawa rayuwa marasa shi ne da marasa galihu a haka nasan shi da zaka zo kofar gidan a duk safiyar allah zakayi mamakin yadda mutane suke shawagi kayi masa adduar kamar yadda ka kudurta domin shine zai zama tsani na rayuwarsa "mutumin ya sauke numfashi ya kama gabansa yana masa addua.
Duk yadda yake kallon buhubuhun kudaden dake gabansa hakan bai sanya shi jin farinciki ba, waɗan nan makudan kudadde daya amsa daga Tanko gote ba zai taɓa goge abinda yayi masa a shafukan rayuwarsa ,sannan bazasu taɓa maida masa jin dadin daya rasa a shekarun da suka gabata ba, fuskar ƙaramar kanwarsa ne ya shiga yi masa gezo a lokacin da numfashinta na karshe ke shirin barin gangar jikinta tana kallonsa hawaye na turereniyar zubowa daga kwarnin idanunta bakinta na amai jini ,yayinda mahaifinsa da mahaifinyarsa ke manne da jikin bangon daki sun dawo tamkar matattu a tsaye tsabar firgici da tashin hankalin halin da diyarsu ke ciki kukan zuci dana zahiri suke a wannan lokacin har rai yayi halinsa wanda sanadiyyar haka zuciyar mahaifinsa ya buga take shima yace ga garinku ......."
cikin isa da izza jaguwa yake takowa zuwa inda sp yusif yake tsaye , ya tsaya nisa kaɗan dashi wanda bai fi taku biyu su fuskanci juna ba , idanunshi dake a lumshe ya ware su fesss akan sp yusif yana ciza gefen lip's d'insa na kasa,sp yusif ya kalli jaguwa kamar zai yi kuka saboda gigita da ganinsa a raye da yayi , tunda yake bai taɓa ganin abinda ya d'aga masa hankali irin wannan ba , "bai taɓa ganin dan adam din da aka yiwa harbi irin wanda suka yiwa motar jaguwa ba amman ya rayu har ya samu damar fitowa daga cikin motar cikin isa da izza ,tabbas yasan akwai wata a kasa ,wannan abu akwai tsarkakkiya acikinta "
Jaguwa ya had'iye dariyar sp yusif dake neman kufce masa saboda gabad'aya ya gama karantar yadda sp yusif da yaransa suka tsorata dashi ,dan gabadaya fuskokinsu ya sauya daga farinciki zuwa matsanancin tsoro da firgici kallo ɗaya zaka musu kasan suna cikin tashin hankali mai tsanani ...
"waye kai sp yusif karaye ? mutumin da cin hanci da rashawa ya aura tun kana ƙaramin mataki har zuwa yanzu daka taka wannan matsayin , har kake godiya ga Allah bisa samun nasara akaina "wani mataki ka taka tukunan ma a rayuwarka da zaka so kama mutun irina "?yayi masa tambayar yana kafeshi da kyawawan idanushi hade da sauke numfashi .
"Ya kamata kusan ko waye ni kafin ku dinga bibiyar rayuwata kana min kallon mamakin ko ? "Kana mamakin yadda na rayu ko ? Zan so bude maka hanyar da zaka fahimci ko wanene ni da kai da sauran tawagar dake bibiyar rayuwata amman bazan yi ba zan barku cikin duhu da wasi wasi da kai da waɗan nan yaran naka daka taso gaba " babu abinda zaku iya akan jaguwa sp yusif karaye , ba ku ba hatta shugaban tawagarku gaba-daya wato commition of police yayi kankatar da zai iya gaba da gaba dani bare kai da yaranka ya karasa maganar a fusace yana nuna sp yusif da yatsansa "
"a kasar nan kowa abinda ranshi yake so yake tare da aiwatar da son zuciya akan kaskantattu marasa galihu , "to bari kaji wani labari da baku isa ba dubunku ma basu isa suja da yaran jaguwa ba bare shi kanshi jaguwa , ni nan nafi karfinku nafi karfin hukuma kuma yanzu na sama addabar rayuwar manyan kasar nan ya karasa maganar yana dukan qirjinshi yana murmushi ......
"Anyway nasan daga inda shiriku yake kowanen daga cikinku ƙoƙarin raya kanshi da ahlinsa yake ba domin kare kasa da kasa kuke yin komai ba domin raya kanku kuke ,dana soma wannan aikin domin ɗaukar ran wani to da ina tabbatar maka kai ne mutun na biyu bayan wancan tantarin tanko gote ...."
duk wannan Maganar da yake yana yi yana jujjuya jikinsa ne kafin daga baya ya shafa fuskarsa ya cire fuskar dake manne da fuskarsa wata fuskar ta bayyana da tsananin kyau da sage zagaye daita "ka kalleni da kyau sp yusif muddin akaina zaka samu double promotion ina tabbatar maka bazaka taba samu ba har duniya ta nade saboda jaguwa mutun ɗaya ne mai fuska daban daban yana gama maganar ya zaro bindiga daga kugunsa ya saita daidai gwiwar sp yusif ya sakar masa bullet biyu a jere wata irin razananniyar qara ya saki tare da durkushewa a gurin "jaguwa ya nuna sa da bakin bindiga "bance ku daina farautata ba , sai dai ku shirya iya shiryawa kafin ku tunkareni yana gama fadar haka ya juya a fusace tamkar mayunwacin zaki yana taku kamar baya son taka kasa ya buɗe motarsa ya shiga yayi mata key a hankali motar ke motsawa tana moving gbdy suka bi bayan motar da kallon mamaki har sanda motar tayi musu nisa .....
*****
A natse yake murza stearing motarsa, lokacin daya shigo unguwar aguje su Anas dake tsaye a kofar gidan sukayi gurin motarsa suna murnar ganinsa, kanshi kawai ya girgiza yana murmushin sannan ya saita hancin motarsa get din gidan , kamil ya zundumawa mai gadi kira ganin zai 'bata musu lokaci yasa suka shiga sauri saurin buɗe masa tafkeken get din gidan yana gama karasa shigowa ko gama daidaita tsayuwar motar bai yi ba suka hau kiciniyar bude motar suka fito dashi tare da d'aga shi sama suna ihun jin dadin sake ganinsa "Winner ooo winner Winner ooo winner ,Winner we don win ooo winner
Pata pata we go win forever winner suka nufi babban parlou'n gidan dashi suka zaunar dashi akan kujera mai zaman mutun uku , Anas ya karasa da sauri ya bude fridge ya d'auko masa power horse mai sanyi ya bude ya mika masa yana zama kusa dashi cike da tsananin murna jubi ya d'auko ruwa mai sanyi ",wayyo Allah nah jaguwa nasan kasha wahala ko da ganin yadda motarka tayi " "babu wata wahala tunda gani a gabanku yanzu"
a tare sukayi dariyar jin dadi sannan sukace "Allah mun gode maka daka dawo mana da farincikinmu lafiya "shine abun godiya ya fada yana furzar da iska "gasky kai din na daban ne namijin duniya ,jaguwa ya ɗan lumshe idanunshi sannan ya gyara zamansa ya soma ƙoƙarin cire yar saman rigarsa Anas yayi saurin cire masa jubi ya dawo gabansa ya soma cire masa takalmin kafafunsa ya saura safa kallonsu kawai yake yana girgiza kai "kasan tun da ka bar gidan nan babu wanda ya sakawa cikinsa wani abu tsabar tashin hankali inji cewar jabir "
"uhmm bari jabir ban taba tsintar kaina cikin tashin hankali irin na yau ba wallahi da zarar na runtse idanuna sai inga kamar wani abu zai same shi anas ya fada yana shafa fuskar jaguwa ,ya ɗan juyo ya kalle shi yana haɗe rai "duk cikin murna dan ban maka kiss ba suka sa dariya gabadaya "yau fa akwai celebrate jubi ya fada yana dauko musu kwaban win ya jere a gabansu "kamar kuwa kun sani ,"ina zamu samowa jaguwa mai zafi data iya chilling fiyye da zahra ?
"ai babu wata mai zafi sosai data wuce zahra ita zan kira yanzu "zaro ido jaguwa yayi "lallai ku yanzu wannan shirmen ne a gabanku ni yadda zanga ammina nake tunani ba wannan shirmen ba "
"Ogbeni ejalo shaye jare Oti sele oppprr kpk Eyonla chuwale sir🙌🏽 se kinwa gbenusi no be atenu " zaka gun ammi amman amman dole zahra zata yi aiki "
A hankali Anas ya kira su eku remo cikin minti goma suka karasao suka shiga fito da buhuhun kudadde da jaguwa yazo dasu suna shigowa dashi daya bayan daya , yayinda su Anas ke zaune suna mamaki yadda har ya iya rabo tanko gote da wadan nan makudan kudaden shi kadai , cikin minti da bai wuce goma ba sukaji mai gadi yana kwankwasa kofa jubi ne ya tashi ya tsaya daga bakin kofa ya bude , cikin yaren turanci mai gadi yace "akwai wani bako da yake ta zuwa gidan nan yau shine zuwansa na biyar baya samun nasarar ganin oga yana fama da matsalolin rayuwa ne gashi yana da yarinya mara lafiya mai kimanin shekara goma tana igondo general hospital ,likitoci sunki bata kulawa sakamakon rashin kuɗi , kafin jubi yace wani abu jaguwa yayi gyaran murya , juyowa jubi yayi a hankali ya dawo inda suke ya tsaya yana duban jaguwa nuna masa wata yar kamara jaka mai zip yayi da hannunsa "zuba masa adadin da zai cika jakar nan ka bashi "yesssss boss an gama Allah yaja da nisan kwana ,jakar ya cika da kudi yayi ziping dinsa ya mikawa mai gadi da hanzari mai gadi ya amsa jakar ya rungume ya juya ya nufi kofar waje ya mikawa mutumin , mutumin na ganin kudin gabad'aya ya rude ya gigice ya soma wani irin kuka mai ban tausayi da taba zuciya,lallai baa rasa na allah koina kuma yadda aka bashi labari wannan matashin mai tsatsanin kirki da tausayi haka ne, take ya nemi mai gadi da yayi masa iso gurin mai gidan domin yi masa godiya , amman mai gadi yaki saboda sanin da yayi wa jaguwa baya son godiya ko kyauta yayi maka kace ka gode sai yace ka godewa Allah ,duk da ban samu ganinsa ba tabbas zan dangwama ina yiwa rayuwarsa addua domin allah ya buda masa kofofin farinciki kamar yadda yayi min , iri mutanen da ake so kenan masu taimako dan allah"
" karka damu ba kai ba duk wanda kaga yana bukatar taimako kana iya masa hanya wannna gidan gidan masu tallafawa rayuwa marasa shi ne da marasa galihu a haka nasan shi da zaka zo kofar gidan a duk safiyar allah zakayi mamakin yadda mutane suke shawagi kayi masa adduar kamar yadda ka kudurta domin shine zai zama tsani na rayuwarsa "mutumin ya sauke numfashi ya kama gabansa yana masa addua.
Duk yadda yake kallon buhubuhun kudaden dake gabansa hakan bai sanya shi jin farinciki ba, waɗan nan makudan kudadde daya amsa daga Tanko gote ba zai taɓa goge abinda yayi masa a shafukan rayuwarsa ,sannan bazasu taɓa maida masa jin dadin daya rasa a shekarun da suka gabata ba, fuskar ƙaramar kanwarsa ne ya shiga yi masa gezo a lokacin da numfashinta na karshe ke shirin barin gangar jikinta tana kallonsa hawaye na turereniyar zubowa daga kwarnin idanunta bakinta na amai jini ,yayinda mahaifinsa da mahaifinyarsa ke manne da jikin bangon daki sun dawo tamkar matattu a tsaye tsabar firgici da tashin hankalin halin da diyarsu ke ciki kukan zuci dana zahiri suke a wannan lokacin har rai yayi halinsa wanda sanadiyyar haka zuciyar mahaifinsa ya buga take shima yace ga garinku ......."