← Book details Kuskuren Baya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 19 OF 160

Sashe 19

Kuskuren Baya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Mutuwar tsaye suka yi gabad'aya  suna kallonsa take  bindigar hannun sp yusif ta subuce  yayi saurin sake  ja da baya idanunshi na kan jaguwa dake ƙoƙarin fitowa daga cikin motar,  duk ilahirin jikinsu rawa yake har sp yusif wanda hankalinsa kusan yafi na sauran tashi dan yanayin bugawar zuciyarsa da yanayin tsoronsa sai ya baka mamaki tamkar ba jami'in tsaro ba  "

  cikin isa da izza jaguwa  yake takowa zuwa inda sp yusif yake tsaye , ya tsaya nisa kaɗan dashi wanda bai fi taku biyu su fuskanci juna ba  , idanunshi dake a lumshe  ya  ware su fesss  akan  sp  yusif yana ciza gefen  lip's d'insa na kasa,sp   yusif  ya kalli jaguwa  kamar zai yi kuka saboda gigita da ganinsa a raye da yayi , tunda yake bai taɓa ganin abinda ya d'aga masa hankali irin wannan ba , "bai taɓa ganin dan adam din da aka yiwa harbi irin wanda suka yiwa motar jaguwa ba amman ya rayu har ya samu damar fitowa  daga cikin motar cikin isa da izza ,tabbas yasan akwai wata a kasa ,wannan abu akwai tsarkakkiya acikinta     "

  Jaguwa  ya had'iye dariyar sp  yusif dake  neman kufce masa saboda gabad'aya ya gama karantar yadda sp yusif da yaransa suka tsorata dashi  ,dan gabadaya fuskokinsu ya sauya daga farinciki  zuwa matsanancin tsoro da firgici  kallo ɗaya zaka musu kasan suna cikin tashin hankali mai tsanani ...

"waye  kai  sp yusif karaye  ? mutumin da cin hanci da rashawa ya aura  tun kana ƙaramin  mataki har zuwa yanzu daka taka wannan matsayin , har kake godiya ga Allah bisa samun nasara akaina  "wani mataki ka taka tukunan ma a rayuwarka da zaka so kama mutun irina  "?yayi masa tambayar yana kafeshi da kyawawan idanushi hade da sauke numfashi .

"Ya kamata kusan ko waye ni kafin ku dinga bibiyar rayuwata  kana min kallon mamakin ko ? "Kana mamakin yadda na rayu ko ? Zan so bude maka hanyar da zaka fahimci ko wanene ni  da kai da sauran tawagar dake bibiyar rayuwata amman bazan yi ba zan barku  cikin duhu da wasi wasi da kai da waɗan nan yaran naka daka taso  gaba " babu abinda zaku iya  akan jaguwa sp yusif karaye  , ba ku   ba hatta shugaban tawagarku  gaba-daya wato commition of police yayi kankatar da zai iya gaba da gaba dani bare kai da yaranka  ya karasa maganar a fusace yana nuna sp  yusif da yatsansa "

"a kasar nan  kowa abinda ranshi yake so yake tare da aiwatar da son zuciya akan kaskantattu marasa  galihu  , "to bari kaji wani labari  da baku isa ba   dubunku ma  basu isa suja da yaran jaguwa ba bare shi kanshi jaguwa , ni nan nafi karfinku nafi karfin hukuma kuma yanzu na sama addabar rayuwar manyan kasar nan   ya karasa maganar yana dukan qirjinshi yana murmushi ......

"Anyway nasan daga inda shiriku  yake kowanen daga cikinku ƙoƙarin raya kanshi  da ahlinsa yake ba domin kare kasa da kasa   kuke yin komai ba domin raya kanku kuke  ,dana soma wannan aikin domin ɗaukar ran wani  to da ina tabbatar maka  kai ne mutun na biyu bayan wancan tantarin tanko gote ...."

duk wannan  Maganar da yake yana yi yana jujjuya jikinsa  ne  kafin daga baya ya shafa fuskarsa ya cire  fuskar dake manne  da fuskarsa wata fuskar ta bayyana da tsananin kyau da sage zagaye daita  "ka kalleni da kyau sp yusif   muddin akaina  zaka samu double  promotion ina tabbatar maka  bazaka taba samu ba har duniya ta nade  saboda jaguwa mutun ɗaya ne mai fuska daban  daban  yana gama  maganar ya zaro  bindiga daga kugunsa ya  saita daidai  gwiwar sp yusif  ya sakar masa bullet biyu a jere   wata irin razananniyar qara ya saki tare da  durkushewa a gurin  "jaguwa ya nuna sa da bakin bindiga "bance ku daina farautata ba , sai dai ku shirya iya shiryawa kafin ku tunkareni  yana gama fadar  haka ya juya a fusace tamkar mayunwacin zaki  yana taku  kamar baya son taka kasa ya buɗe motarsa  ya shiga yayi mata key a hankali motar ke motsawa tana  moving  gbdy suka bi bayan  motar da kallon mamaki har sanda motar tayi musu nisa  .....

*****

A natse yake murza stearing  motarsa, lokacin  daya shigo unguwar  aguje  su  Anas dake  tsaye a kofar gidan  sukayi  gurin motarsa suna  murnar ganinsa, kanshi  kawai  ya  girgiza yana murmushin  sannan  ya saita hancin motarsa  get din gidan  , kamil ya zundumawa mai  gadi kira  ganin  zai 'bata musu lokaci yasa  suka shiga sauri saurin  buɗe masa tafkeken get din  gidan  yana gama  karasa  shigowa ko gama daidaita tsayuwar motar bai yi ba  suka hau kiciniyar  bude motar  suka  fito dashi tare da d'aga shi sama  suna ihun jin dadin sake ganinsa   "Winner ooo winner Winner ooo winner ,Winner we don win ooo winner
Pata pata  we go win forever winner  suka nufi babban  parlou'n  gidan dashi  suka  zaunar dashi akan kujera mai zaman mutun uku , Anas ya karasa da sauri  ya bude fridge  ya d'auko  masa power  horse mai sanyi  ya bude ya  mika masa yana zama kusa dashi cike  da  tsananin murna jubi ya d'auko ruwa mai sanyi  ",wayyo  Allah nah  jaguwa nasan kasha wahala  ko da ganin yadda motarka tayi " "babu wata wahala tunda gani a gabanku  yanzu"
a tare sukayi  dariyar jin dadi  sannan sukace "Allah  mun gode maka daka  dawo mana da farincikinmu lafiya  "shine  abun godiya  ya fada yana furzar da iska  "gasky kai  din na daban ne namijin duniya  ,jaguwa ya ɗan lumshe  idanunshi  sannan ya gyara  zamansa   ya soma ƙoƙarin cire yar saman rigarsa Anas yayi saurin cire masa jubi ya dawo gabansa ya soma cire masa takalmin kafafunsa  ya  saura safa  kallonsu kawai yake yana girgiza kai "kasan tun da ka bar gidan nan  babu wanda ya sakawa cikinsa wani abu tsabar tashin hankali inji cewar jabir "

"uhmm bari jabir ban taba tsintar kaina cikin tashin hankali irin na yau ba wallahi   da zarar na runtse idanuna sai inga kamar wani abu zai same shi  anas ya fada yana shafa fuskar jaguwa  ,ya ɗan juyo ya kalle shi yana haɗe rai "duk cikin murna dan ban maka kiss ba suka sa dariya gabadaya  "yau fa akwai celebrate jubi ya fada yana dauko musu kwaban win ya jere a gabansu  "kamar kuwa kun sani ,"ina zamu samowa jaguwa mai zafi data iya chilling fiyye da zahra ?
"ai babu wata  mai zafi sosai data wuce zahra ita zan kira yanzu "zaro ido jaguwa yayi "lallai ku yanzu  wannan  shirmen ne a gabanku ni yadda zanga ammina nake tunani ba wannan shirmen ba "
"Ogbeni ejalo shaye jare Oti sele oppprr kpk Eyonla chuwale sir🙌🏽 se kinwa gbenusi no be atenu " zaka gun ammi amman amman dole zahra zata yi aiki "

A hankali Anas ya kira su eku remo cikin minti goma  suka karasao suka  shiga fito da buhuhun kudadde da jaguwa yazo dasu  suna shigowa dashi daya bayan daya  , yayinda su Anas ke zaune suna mamaki yadda har ya iya rabo  tanko gote da wadan nan  makudan kudaden shi kadai , cikin  minti da bai wuce goma ba sukaji mai gadi yana  kwankwasa kofa jubi ne ya tashi   ya tsaya daga bakin kofa ya bude , cikin yaren turanci mai gadi yace  "akwai wani bako da yake ta zuwa gidan nan yau shine zuwansa na biyar baya samun nasarar ganin  oga yana fama da matsalolin rayuwa ne gashi yana da yarinya  mara lafiya mai kimanin shekara goma  tana igondo  general  hospital ,likitoci sunki bata kulawa sakamakon rashin kuɗi , kafin  jubi yace wani abu  jaguwa  yayi  gyaran murya , juyowa jubi   yayi a hankali  ya  dawo inda suke ya tsaya yana duban jaguwa  nuna masa wata yar kamara jaka mai zip yayi da hannunsa  "zuba masa adadin da zai cika jakar nan ka bashi "yesssss boss an gama Allah yaja da nisan kwana ,jakar  ya cika da kudi  yayi ziping  dinsa  ya mikawa mai gadi da hanzari mai gadi ya amsa jakar ya rungume  ya juya ya  nufi kofar waje ya mikawa mutumin  , mutumin na ganin kudin gabad'aya ya rude ya gigice ya soma  wani irin kuka mai ban tausayi da taba zuciya,lallai baa rasa na allah koina kuma yadda aka bashi labari wannan matashin mai tsatsanin kirki da tausayi haka ne,  take ya nemi mai gadi da yayi masa iso gurin mai gidan domin yi masa godiya , amman mai gadi  yaki saboda sanin da yayi wa jaguwa baya son godiya ko kyauta yayi maka kace ka gode sai yace ka godewa Allah  ,duk da ban samu ganinsa ba tabbas zan dangwama ina yiwa rayuwarsa addua  domin allah  ya  buda masa  kofofin  farinciki kamar yadda  yayi min , iri mutanen da ake so kenan  masu taimako dan allah"
" karka damu ba kai ba duk wanda kaga yana bukatar taimako kana iya masa hanya wannna gidan gidan masu tallafawa rayuwa marasa shi ne da marasa galihu a haka nasan shi da zaka zo kofar gidan a duk safiyar allah zakayi mamakin yadda mutane suke shawagi kayi masa adduar kamar yadda ka kudurta domin shine zai zama tsani na rayuwarsa "mutumin ya sauke numfashi ya kama gabansa yana masa addua.

Duk yadda yake kallon buhubuhun  kudaden dake gabansa  hakan bai sanya shi jin  farinciki ba, waɗan nan  makudan kudadde daya amsa daga Tanko gote ba zai taɓa  goge  abinda yayi masa  a shafukan rayuwarsa  ,sannan bazasu taɓa  maida masa  jin dadin daya rasa a shekarun da suka gabata ba, fuskar ƙaramar  kanwarsa ne ya shiga yi masa gezo a lokacin da numfashinta na karshe ke shirin barin gangar jikinta tana kallonsa hawaye na turereniyar zubowa daga kwarnin idanunta bakinta na amai jini  ,yayinda  mahaifinsa da mahaifinyarsa ke manne da jikin bangon daki  sun dawo tamkar matattu a tsaye  tsabar firgici da tashin hankalin halin da diyarsu ke ciki   kukan  zuci dana zahiri suke   a wannan lokacin har rai  yayi halinsa wanda sanadiyyar haka zuciyar mahaifinsa ya buga take shima yace ga garinku ......."
Chapter 19 · 0% Book details