← Book details Kuskuren Baya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 48 OF 160

Sashe 48

Kuskuren Baya Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Yayi  d'an murmushin gefen baki  wanda  ya  bayyana  ainihin  sirrin kyawun  da Allah yayi masa "Ina  ce  kince  zaki  tona  min  asiri  byn kin bar gidan nan ? "tayi saurin  girgiza masa  Kai alamun a'a "bazan yi ba na maka wannan alkwarin duk runtsi duk wuya bazan aikata hakan gareka ba muddin ka fad'a min  ".
"kada ki damu idan kin shirya  fad'awa  duniya  kiyi   karki   fasa , idan kin koma  gida ki tara gbdy 'yan jaridan garin nan ki sheida  musu cewar Adnan dan fashi ne abinda nayi Imani dashi   Allah  bazai  basu  nasara akaina  ba ,  mahaifiyata tana tsaye  a  kaina da adduointa haka mutane  da dama suna min addua , duk da Ina  aikata  zunubai   Allah zai   tsareni   daga sharrin duk wani  jami'n  tsaron  albarkancin  adduar mahaifiya data mutanen kirki  ."
shiru tayi tana  kallonsa hawaye na gangaro mata cike da sanyin jiki  ta zare hannuwanta dake  cikin  nasa  ta soma k'okarin zare jikinta daga garesa  ,yana  kallonta tayi baya da kujeran da take zaune ta  maida jikinta ta kwanta  tana mai runtse idanunta ,  yatsun hannunta ya kamo  bai san yadda akayi ba ya tura cikin bakinsa  ya  fara tsotsa , wani iri ta dinga ji a sansar jikinta kmr ana zarar ranta , tayi k'okari cirewa ya rike yatsun  da  karfi  yana cigaba da tsotsa kamar ya samu sweet  sai daya tsotsa son ranshi sannan ya cire bakinsa ya ciro hanky ya goge mata hancinta dake digar  jini  yana cewa "ki kwantar da hankalinki zan  fad'a miki ko waye amman  ba yau ba   ". yana  gama fad'ar haka ya sakar  mata  hannu ya    bud'e  murfin motar ya   fito ya  zagayo  bangarenta da  take  ya  bud'e mata  ta fito  jiki a sanyaye,  ya d'auki ledar maganin  da aka  basu   ta dubeshi fuska da hawaye  .
bai tsaya bi ta kanta ba ya riko    hannunta  ta turje  alamun bazata ba ya juyo ya watsa mata  idanunshi fuskarsa a d'aure  "karki  min  taurin kai " ya  fada tare da sake  juyawa  suka shiga cikin  gidan bakinsa d'auke da  addua (bismillahi  walajna
wa  bismillahi  kharajna wa'allahi rabana tawakkalna ) tana jinjinawa  girman  iliminsa,  gashi tantiri  gashi  malami   ta  fad'a  acikin  ranta .

Kai tsaye d'akinta  ya shiga daita  ya  kamota ya  zaunar daita abakin gado ya janyo  kujerar  madubi ya zauna yana  bin  d'akin da Kallo duk ta hargitsa   d'akin ko d'azu daya shigo yaso yayi magana yanayinta yasa ya share    ya  girgiza Kansa  sannan ya  fuskanceta  ,baya  jin dadin yadda  take d'aga  hankalinta  akan gida ,
shi  bashi  da niyyar  cutar daita , ko abinda ya faru daren  shekaranjiya ma  ba yin  Kansa  bane itace sila ,  tillastawarta ce    ta  janyo  hakan ta faru   ban cin haka babu abinda zai kai shi aikata zina daita.
"tan ...!
Ya kira sunanta cikin kasalalliyar muryarsa yana  sake  kamo  hannunta tare  da kafeta da  tsumammun idanunshi  masu  kashe mata sansar  jiki , d'ago idanunta tayi ta zuba masa tana sauraronsa tare da jin wani iri a sansar  jikinta duk sanda zata kalleshi sai taji wannan yanayi wanda babu tantama na qunar da take masa ne . "wanda  ya  tura mu fashi gidanku  bashi da  hannun  cikin zamanki  tare damu , rikeki da nayi Kuma nayi amfani da maganar da mukayi  dashi  a  karshen maganarmu  cewa "yayi  yana da wasu  target  akanki  a dawo dake  ya aiwatar da nufinsa  wannan  shine dalilin da yasa  na rikeki  ba dan raina na so ba ".

"Dan  ranka  na so dai ka rikeni  idan ba haka ba meye aciki  ? tayi maganar a  matukar fusace  " ka mayar dani  Inda ka d'auko  ko ka fad'i  wanda ya turaku  gidanmu  kawai  a wuce gurin , ya runtse idanunshi  yana nazari wasu  abubuwa akanta .
ta dubeshi  idanunta cike da ruwan  hawaye "adnan ka d'auke ni a daren nan  ka mayardani  gidanmu   dukkanin  alamun  sun nuna min  iyayena na cikin tsananin damuwar rashina da.... ...."
"na  sani Kuma zan mayar dake amman ba yau ba ki bani lokaci wallahi zan mayar dake akwai binciken da nake da  zarar  na gama zamammu  tare  zai zama  tarihi  ".
ta  matso kusa dashi sosai har gwiwowinsu na gogan juna "naji amman dan Allah ka sanar dani Wanda ya tura ku gidanmu  fashi ?ya girgiza mata Kai  sannan yace "idan ma kika ji ko waye ba lallai ki yarda ba, Killa Kuma  ma kiji kin tsanani kanki  sannan tabbas wasu rigingimu zasu  faru  saboda kusancin dake tsakanin mahaifinki da wanda ya bamu  aikin ." ta kamo hannunsa  ta rike gam cikin wani yanayi "cikin   dangin dad dina ne  ko na mum dina ke son ganin bayan iyayena  da ni kaina ? ya girgiza mata Kai alamun "a'a"to sanar dani dan Allah zan barwa cikina bazan ta'ba fad'awa  kowa ba  ".

Shiru yayi yana nazari akan  lamarin ya fad'a mata ne ko ya shareta "abinda yasani  tabbas  idan batun
ya fito ya sa'bawa dokarsu domin a aikinsu babu wannan tsarin ,duk  runtsi duk wuya ba'a tonawa juna asiri tunda tun farko da wajewa ake tsara komai ba'a juyawa juna baya.
ta katse masa tunani ta hanyar cewa  "kana  ganin zan iya tona maka asiri ne ?"  Allah na  dai fad'a ne amman  bazan iya aikata hakan  ba. "na sani  dan  fad'awa soyayya  ba  abu  ne me sauki  ba  da  har   zaki tona asirin masoyinki I know  you  can't  do that to me tanweer    bazaki  iya fad'ar  komai akaina ba   saboda qaunar da  kike min."

ta lumshe tsumammun idanunta na second biyu tare da jan tsaki acikin zuciyarta dan muddin tayi a fili balai zai mata a hankali   ta bud'e idanunta  akan kyakkyawar  fuskarsa  "ba  wannan story din   na  tambayeka ba ,ka ajiye  batun wani soyayya dan a yanzu  babu ita acikin  raina buqatata   ka min bayani wanda yasakaka aikin  bana son jan  aji  da salo  tayi  mgnr tana murgud'a masa  k'aramin bakinta .yayi  murmushin gefen baki yace "to  da gaske zaki rufa min asiri agurin iyayenki ? da sauri tace "me zai hana in bukatar hakan  ya  taso ?"
"sannan  Ina fatan zaki fahimceni  ?" ta gyada masa  alamun zata fahimcesa, shiru tayi tana jiran ya faiyace mata  Komai  kawai taga ya zare hannunsa ya mike tsaye tare da zura hannuwansa duka cikin aljihunsa , a hankali ya juya mata baya yayi taku zuwa  daf da kofar  bayinta  ya tsaya tare da waigowa yace "ni zaki yaudara  ko ? ta girgiza masa Kai alamun "a'a  "karya  kike  tanweer yaudarata  zakiyi  dan  zuciyata  bata yarda dake ba   duk  da d'arurar soyayyata dake cikin kwayar idanunki da zuciyarki   kina son na fad'a  miki wanda ya tura mu fashi gidanku sai  ku taru  ke da jami'an tsaro ku  cutar  damu ko  ? 
yana rufe baki yaji ta rungumesa tsam  ta bayansa tana cewa  "wallahi kaji na rantse maka  bazan sheidawa kowa ba ,bazan zamo me Saka hannu gurin cutar da kai ba  ,ya juyo daita gabansa suka  fuskanci juna  "dame zaki gamsar  dani  bayan tun farko kice da bakinki kika fad'a min zaki tona min asiri ?" ta tsugunna gwiwowinta  biyu a kasa ",ka  yarda dani Adnan na rantse  maka bazan aikata  hakan  ba ".  ya tako  a hankali ya tsugunna a gabanta "na sani bazaki fad'a ba amman ni ba mahaukaci bane da zan fad'a miki wanda ya tura mu a aiki gidanku ,  babu wannan ajandar  acikin aikinmu  ko gaban alqali za'a Kai d'aya daga cikinmu da wahala ya fad'a  ,kada ki damu ki bar son jin komai  gida ne dai zan kaiki a duk sanda wa'adi ya kai   ya fad'a yana janyota jikinsa  ya makaleta tare da Kai bakinsa daidai kunnenta   "ki K'ara natsuwa  da  jin  dumin jikina ."

Tayi  shiru zuciyarta na quna  da  tuttukin bakinciki ,duk  abinda take  tana  yi  ne dan ya fad'a mata wanda ya bashi aikin amman shine zai  rainawa kansa hankali  yace ita ya rainawa  ?"   cike da matsanacin  bakinciki  fixge jikinta  tace " kar Allah yasa ka fad'a kuma Allah ya Isa da rungumata da kayi ban yafe maka ba  mugu kawai  me   zuciyar  dutse  duk  irin rantsuwar dana  yi maka bai sa ka  yarda dani ba  saboda muguwar zuciya irin taka  ." cikin  dariya ya sake  janyota jikinsa sosai ya  rungumeta tsam yana busa mata numfashinsa   tare da cewa "kada ki damu da irin zuciyata  dan babu abinda zai qareki dashi  Allah ya Isa  Kuma daman allah   isashe ne ko  baki ce  ba  , wayonki yayi  matukar  burgeni I love  it keep it  up  yayi  mata  kiss  a goshi sannan  yace "zaki cigaba da zama da Adnan har zuwa sanda yaga damar  maidake gidanku   sannan kiyi k'okari ki rage wannan  soyayyar da kike  masa  idan ma da hali ki cireta  gbdy  ya saketa ya koma jikin window  ya tsaya yana kallon farfajiyar  gidan  kusan minti biyar yana tsaye sannan ya juyo "me zaki  ce akawo miki  kici  ki sha magani ? babu abinda zanci ta fad'a a fusace  tana dubansa hawaye na tsiyayowa akan quncinta  "daman Kin saba  kwana da yunwa  idan shi kike ra'ayi  fine  ,I don't care ya nufi  kofar fita daga d'akin ya barta cikin tsananin damuwa da sake  shiga tashin hankali ."
Chapter 48 · 0% Book details