Sashe 156
Kuskuren Baya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Leko da kanta tayi ta duba hagu da dama bata ganshi ba ta sauke naunayen ajiyar zuciya sannan ta fito ta cigaba da tafiyarta ,bai fi taku uku tayi ba taji saukar hannun mutun ajikinta da sauri ta juyo a matukar tsorace tana qokarin bud'e baki ta kurma ihu ta gansa tsaye dan haka tayi shiru tare da sauke ajiyar zuciya,ya zuba mata ido duk da ba asalin idanunsa bane amman sai data ga wasu abubuwa na fitowa daga cikinsu suna daure jijiyoyin jikinta ."
Ya d'auki second goma yana tsaye yana kallonta sannan ya kai hannunsa ya riko tsintsiyar hannuta cikin nashi ya nufi wata hanya da mutane basu kai kawo ya tsaya ya sake zuba mata ido, had'e fuskar tayi sosai tana cewa "wai meye haka ne ?"da sauri jaguwa ya girgiza mata kai "kinga ni bawani tashin hankali nake nema ba kawai ina bukatar ki bar nan kuma a yanzu ."
"saboda me kenan zan bar nan ? saboda banason wani abu ya ta'ba min lafiyrki "wacece ni da zaka
ce baka son wani abu ya ta'ba lafiyata ? ya lumshe idanunshi yana shafa goshinsa da hannunsa ya dauki second biyu a haka sannan ya dago kanshi "kinga malama ki maida hankalinki kiyi abinda nace kafin raina ya baci "tsaki taja da karfi ta cigaba da magana cikin tsananin fushi "kaga nifa banason wata matsla idan wani abu ya sameni meye damuwaarka ?"kamar yace mata babu amman ya kasa furta mata hakan ya cigaba da dubanta a tsanake . "kaga kaje dan Allah kayi abinda ya kawoka dan ni babu ruwana da abinda ya kawoka duk ma abinda ya kawoka nasan bai wuce ..."
cikin tsananin fushi yasa hannu zai buge mata baki ta kauce da sauri muryarsa cike da hassala yace "wannan bakin ina mutuwar sonshi amman sam bashi da mutunci amman zanyi maganinsa ne ."
wani irin kallo tayi masa wanda ya shagaltar dashi dan bai san sanda ya soma murza hannunta dake cikin bashi ba “wannan ikon duk na da ne a yanzu babu me maganin wannan bakin ta hanyar isa ko nuna iko sai wanda zan aura dan haka ka tsaya a matsayinka na wanda naso a ada ".tana gama fadar haka ta zame hannunta dake rike cikin nashi ta juya ,hannunsa taji ya riko kugunta gam ya hadeta da jikinsa sosai kmar zai hade bakinsu gurin daya "karya ne tanwer har yanzu ina cikin zuciyarki bama zaki iya saka wani mahaluki acikin zuciyarki ba wannan zuciyar tawa ce kuma ni kadai ". tanwer ta lumshe idanunta tana jin yadda soayyyarsa ke sake hud'a jiki da zuciyarta "wayyo allah adnan gbdy ka mamaye komai nawa amman duk da haka bazan ta'ba sadaukar maka da farincikina ba har sai ka saduda ka zubar da makaman yakinka kayi abinda nake so , cikin murya me cike da kasala ya cigaba da magana "dan allah tanwer kiyi abinda nake bukata".
hancinta ta hura masa kawai batare data amsa masa zatai ko bazatai ba sai dai alamunta ya nuna masa bazatai abinda yake bukata ba dan sai kokarin turesa take domin ta bar gurin dan haka ya jata zuwa wani madaidaicin plaza dake cikin shopright din wanda ake siyar da dafaffen abinci ya zaunar daita akan daya daga cikin kujerun dake ajiye agurin , ya matsota sosai kamar zai shige jikinta yana shafa gefen fuskarta "kiji maganta ki zauna anan kada kiyi Kuskuren barin gurin nan duk runtsi duk wuya har na dawo ya furta cikin wani irin salo me kashe sansar jiki ,bata amsa ba ta dauke kanta daga kallonsa ta fuskanci masu siyar da abincin shi kuma ya juya cikin sauri ,bata juyo ta kallesa ba har ya fice daga gurin yana fita ya gyara abun kunnensa ta yadda kowannensu zai jiyosa "lokacin kutse yayi ." ya fada cikin zafin nama bayan fitarsa da minti biyar tanwer ta mike cike da tsinkewar zuciya tana jan tsaki ta fito sai dai batayi nisa ba opposite din plaza data fito ta shiga tana duba agogon mata qirjinta na cigaba da faduwa wanda ta danganta faruwar hakan da ganin jaguwa da tayi duk da a nata bata dauka operation yazo kasancewar shi kadai ta gani ."
kai tsaye indoor cikin inda aka tanada domin yin shoping ya shiga bayan ya karbi bakar jaka a hannun daya daga cikin yaransa aciki gurin ya hadu da mutanen daya zo domin su, hannu ya mika masu daya byn daya suka gaisa sannan ya dan waiga hagu da dama dan a d'an tsorace yake amman fahimtar babu wanda idanunsa ke kansu ya saki jikinsa sosai ya bude jakar hannunsa ya ciro leda daya ta coken ya mikawa mutun daya, ya kar'ba tare da ciro qaramin wuka a gaban aljihunsa ya tsaga ledar ya dibi coken din kadan ya kai bakinsa domin tabbatar da me kyau ne ko akasin haka ."jinjina kai yayi alamun tayi dan haka ya mika masa ya mayar inda ya cirota shi kuma ya mika masa jakar dake dauke da makudan kudade ,shima indoor ya bude ya tabbatar da kudaden ne a ciki ya sake mika masa hannu sannan suka fito atare indoor yayi hannunsa na hagu yayinda fararen fata sukayi na dama ."
daga cikin abun jin magana su suka ji muryar jaguwa yana cewa "duk ku ankare fa gasu nan da alamar sun gama kasuwancisu kada kuyi harbi har sai idan nace kuyi jakar dake hannunsu kawai muke bukata sannan muyi kokari jami'an tsoro suyi gaba dasu idan sunki su bayar ne kawai zan iya cewa ayi wani abu akai ."Indoor na tafiya kawai yaga kamar ana binsa abaya ya waiga bai ga kowa ba ya sauke naunayen ajiyar zuciya ya sake rike jakar kudinsa da kyau ya canza hanya, bangaren wadan can mutane suma anas ne da kamil har ma dasu jubi ke biye dasu abaya duk inda suka bi suna biye dasu ."
tafiya kadan indoor yayi kawai yaga mutun ta gabansa tsaye yana kallonsa jaguwa bai tsaya wata wata ba ya daura masa bakin bindiga a goshinsa wata irin firgita yayi ya shiga zazzare idanunwa ya juya da niyyar guduwa nan ma yaga mutun biyu abayansa duk rike da bindiga ,nan take hankalin babban yaronsa wanda kuma ya kasance kani garesa ya tashi domin idanunshi na kan yayansa a bisa yadda suka tsara atare ya waiga hagu da dama bai ga alamun polisawa ba hakan ya tabbatar masa da 'yan fashi ne aka musu cune.”
"Miko min jakar hannunka."Idan kai jami'in tsaro ne gara kawai ka danganani da hukuma ko kuma mu sasanta anan dan zamu iya gyarota ,girgiza masa kai jaguwa yayi "ko daya mu masu amsar rabonmu né kawai mu qara gaba bamu da wata halaqa da polisawa hasalima abokan gabarmu né "gaskiya bazan baku wannan jakar ba gara ma ku daina wannan sana'ar kuzo ku hada kai dani ni nan zansa rayuwarku ta canza ".bazan iya aikinka ba domin aiki ne dake gurbata rayuwar yayan al'umma bazan zama silar bata zukata ta hanyar siyar da abinda zai saka bushewar zuciyar ga ya’yan alumma ba kai ma ina baka shawarar ka daina domin kuwa gara alqallata akan taka.” sam maganarsa bai sa farinciki ya mamaye zuciyarsa ba sai ma duhu daya gilma a qirjinsa "ka bani jakar kudin ya sake maimaita maganarsa yana miko masa hannunsa .”
Atare daga inda yake a maboyarsa ya saki harsashi guda biyu nan take jaguwa ya juyo a matukar firgice sauran mutun biyu din dake tare dashi suka zagayesa suna duba ta inda harbin ya fito kanin indoor ya nuna kansa domin su san ko waye mutun biyu suka biyosa kamar iska yabi wata hanya anan ma boyewa yayi yana kallonsu .
gurin ne ya hargitse da hayaniyar mutane kowa ya fara neman takansa wanda hakan ya bawa indoor damar kwasa da mugun gudu rike da jakar hannunsa, jaguwa ya biyosa aguje shi jakar kudin yake bukata daya ajiyeta sannan yaga sun shiga hannun polisawa shi kenan sun gama dashi babu wani binsa da zai yi dashi ."
acan dayan bangaren ma anas biye yake da mutane guda biyu inda mutun daya yabi wata hanya nan kawunansu ya rabu gida biyu wasu suka bi mutun daya anas yabi me rike da jakar koken cikin haka jubi da kamil suka biyo hanyar da anas yabi tare da cire abun kunnensu “wannan dama ce kamil kar mu bari ta subuce mana cikin nida kai duk wanda ya samu damar kawar dashi kawai yayi.”
atare suka gyada kai tare da maida abun kunnensu suka cigaba da tafiya cikin sauri cikin haka suka hango anas yayi nasarar hard’e kafafun mutumin tare da saita kanshi da bakin bindiga ,da kai kamil yayiwa jubi alamar ya harbesa ai kuwa babu wani bata lokaci ya saita kanshi da bindiga zai harbi keyarsa yayinda shi kuma kamil ya kalli bayansa saboda tsaro dan kar wani daga cikin yaransu su
ya gansu ,adaidai lokacin sky ya sanyo kai ganinsa yasa kamil ya rike hannun jubi yayi kasa dashi ya harbin kafafun mutumin anas ya juyo da sauri cikin tsananin firgici sai dai ganinsu sune a bayansa yasa ya samu natsuwar zuciya ya maida hankalinsa ga
kafafun mutumin dake gabansa jini ne ke zuba kamar an yanka qaramar dabba “oga ya kuka tsaya anan kuzo mu qarasa mana “ya fad’a tare da wucesu ya qarasa inda anas yake wanda yayi nasarar kar'bar jakar hannun mutumin ya kallesu daya bayan daya yana cewa “waye yayi harbin acikinku ?”a dan rikice suka kalli junansu jubi ne yayi karfin hali cewa “kamil ne “ dan haka ya fuskanci kamil “gsky da bakayi harbin ba tunda gbdynmu ance kar muyi ya kamata mu dinga kiyayewa ya qarasa maganar yana cewa muje ko.”
Ya d'auki second goma yana tsaye yana kallonta sannan ya kai hannunsa ya riko tsintsiyar hannuta cikin nashi ya nufi wata hanya da mutane basu kai kawo ya tsaya ya sake zuba mata ido, had'e fuskar tayi sosai tana cewa "wai meye haka ne ?"da sauri jaguwa ya girgiza mata kai "kinga ni bawani tashin hankali nake nema ba kawai ina bukatar ki bar nan kuma a yanzu ."
"saboda me kenan zan bar nan ? saboda banason wani abu ya ta'ba min lafiyrki "wacece ni da zaka
ce baka son wani abu ya ta'ba lafiyata ? ya lumshe idanunshi yana shafa goshinsa da hannunsa ya dauki second biyu a haka sannan ya dago kanshi "kinga malama ki maida hankalinki kiyi abinda nace kafin raina ya baci "tsaki taja da karfi ta cigaba da magana cikin tsananin fushi "kaga nifa banason wata matsla idan wani abu ya sameni meye damuwaarka ?"kamar yace mata babu amman ya kasa furta mata hakan ya cigaba da dubanta a tsanake . "kaga kaje dan Allah kayi abinda ya kawoka dan ni babu ruwana da abinda ya kawoka duk ma abinda ya kawoka nasan bai wuce ..."
cikin tsananin fushi yasa hannu zai buge mata baki ta kauce da sauri muryarsa cike da hassala yace "wannan bakin ina mutuwar sonshi amman sam bashi da mutunci amman zanyi maganinsa ne ."
wani irin kallo tayi masa wanda ya shagaltar dashi dan bai san sanda ya soma murza hannunta dake cikin bashi ba “wannan ikon duk na da ne a yanzu babu me maganin wannan bakin ta hanyar isa ko nuna iko sai wanda zan aura dan haka ka tsaya a matsayinka na wanda naso a ada ".tana gama fadar haka ta zame hannunta dake rike cikin nashi ta juya ,hannunsa taji ya riko kugunta gam ya hadeta da jikinsa sosai kmar zai hade bakinsu gurin daya "karya ne tanwer har yanzu ina cikin zuciyarki bama zaki iya saka wani mahaluki acikin zuciyarki ba wannan zuciyar tawa ce kuma ni kadai ". tanwer ta lumshe idanunta tana jin yadda soayyyarsa ke sake hud'a jiki da zuciyarta "wayyo allah adnan gbdy ka mamaye komai nawa amman duk da haka bazan ta'ba sadaukar maka da farincikina ba har sai ka saduda ka zubar da makaman yakinka kayi abinda nake so , cikin murya me cike da kasala ya cigaba da magana "dan allah tanwer kiyi abinda nake bukata".
hancinta ta hura masa kawai batare data amsa masa zatai ko bazatai ba sai dai alamunta ya nuna masa bazatai abinda yake bukata ba dan sai kokarin turesa take domin ta bar gurin dan haka ya jata zuwa wani madaidaicin plaza dake cikin shopright din wanda ake siyar da dafaffen abinci ya zaunar daita akan daya daga cikin kujerun dake ajiye agurin , ya matsota sosai kamar zai shige jikinta yana shafa gefen fuskarta "kiji maganta ki zauna anan kada kiyi Kuskuren barin gurin nan duk runtsi duk wuya har na dawo ya furta cikin wani irin salo me kashe sansar jiki ,bata amsa ba ta dauke kanta daga kallonsa ta fuskanci masu siyar da abincin shi kuma ya juya cikin sauri ,bata juyo ta kallesa ba har ya fice daga gurin yana fita ya gyara abun kunnensa ta yadda kowannensu zai jiyosa "lokacin kutse yayi ." ya fada cikin zafin nama bayan fitarsa da minti biyar tanwer ta mike cike da tsinkewar zuciya tana jan tsaki ta fito sai dai batayi nisa ba opposite din plaza data fito ta shiga tana duba agogon mata qirjinta na cigaba da faduwa wanda ta danganta faruwar hakan da ganin jaguwa da tayi duk da a nata bata dauka operation yazo kasancewar shi kadai ta gani ."
kai tsaye indoor cikin inda aka tanada domin yin shoping ya shiga bayan ya karbi bakar jaka a hannun daya daga cikin yaransa aciki gurin ya hadu da mutanen daya zo domin su, hannu ya mika masu daya byn daya suka gaisa sannan ya dan waiga hagu da dama dan a d'an tsorace yake amman fahimtar babu wanda idanunsa ke kansu ya saki jikinsa sosai ya bude jakar hannunsa ya ciro leda daya ta coken ya mikawa mutun daya, ya kar'ba tare da ciro qaramin wuka a gaban aljihunsa ya tsaga ledar ya dibi coken din kadan ya kai bakinsa domin tabbatar da me kyau ne ko akasin haka ."jinjina kai yayi alamun tayi dan haka ya mika masa ya mayar inda ya cirota shi kuma ya mika masa jakar dake dauke da makudan kudade ,shima indoor ya bude ya tabbatar da kudaden ne a ciki ya sake mika masa hannu sannan suka fito atare indoor yayi hannunsa na hagu yayinda fararen fata sukayi na dama ."
daga cikin abun jin magana su suka ji muryar jaguwa yana cewa "duk ku ankare fa gasu nan da alamar sun gama kasuwancisu kada kuyi harbi har sai idan nace kuyi jakar dake hannunsu kawai muke bukata sannan muyi kokari jami'an tsoro suyi gaba dasu idan sunki su bayar ne kawai zan iya cewa ayi wani abu akai ."Indoor na tafiya kawai yaga kamar ana binsa abaya ya waiga bai ga kowa ba ya sauke naunayen ajiyar zuciya ya sake rike jakar kudinsa da kyau ya canza hanya, bangaren wadan can mutane suma anas ne da kamil har ma dasu jubi ke biye dasu abaya duk inda suka bi suna biye dasu ."
tafiya kadan indoor yayi kawai yaga mutun ta gabansa tsaye yana kallonsa jaguwa bai tsaya wata wata ba ya daura masa bakin bindiga a goshinsa wata irin firgita yayi ya shiga zazzare idanunwa ya juya da niyyar guduwa nan ma yaga mutun biyu abayansa duk rike da bindiga ,nan take hankalin babban yaronsa wanda kuma ya kasance kani garesa ya tashi domin idanunshi na kan yayansa a bisa yadda suka tsara atare ya waiga hagu da dama bai ga alamun polisawa ba hakan ya tabbatar masa da 'yan fashi ne aka musu cune.”
"Miko min jakar hannunka."Idan kai jami'in tsaro ne gara kawai ka danganani da hukuma ko kuma mu sasanta anan dan zamu iya gyarota ,girgiza masa kai jaguwa yayi "ko daya mu masu amsar rabonmu né kawai mu qara gaba bamu da wata halaqa da polisawa hasalima abokan gabarmu né "gaskiya bazan baku wannan jakar ba gara ma ku daina wannan sana'ar kuzo ku hada kai dani ni nan zansa rayuwarku ta canza ".bazan iya aikinka ba domin aiki ne dake gurbata rayuwar yayan al'umma bazan zama silar bata zukata ta hanyar siyar da abinda zai saka bushewar zuciyar ga ya’yan alumma ba kai ma ina baka shawarar ka daina domin kuwa gara alqallata akan taka.” sam maganarsa bai sa farinciki ya mamaye zuciyarsa ba sai ma duhu daya gilma a qirjinsa "ka bani jakar kudin ya sake maimaita maganarsa yana miko masa hannunsa .”
Atare daga inda yake a maboyarsa ya saki harsashi guda biyu nan take jaguwa ya juyo a matukar firgice sauran mutun biyu din dake tare dashi suka zagayesa suna duba ta inda harbin ya fito kanin indoor ya nuna kansa domin su san ko waye mutun biyu suka biyosa kamar iska yabi wata hanya anan ma boyewa yayi yana kallonsu .
gurin ne ya hargitse da hayaniyar mutane kowa ya fara neman takansa wanda hakan ya bawa indoor damar kwasa da mugun gudu rike da jakar hannunsa, jaguwa ya biyosa aguje shi jakar kudin yake bukata daya ajiyeta sannan yaga sun shiga hannun polisawa shi kenan sun gama dashi babu wani binsa da zai yi dashi ."
acan dayan bangaren ma anas biye yake da mutane guda biyu inda mutun daya yabi wata hanya nan kawunansu ya rabu gida biyu wasu suka bi mutun daya anas yabi me rike da jakar koken cikin haka jubi da kamil suka biyo hanyar da anas yabi tare da cire abun kunnensu “wannan dama ce kamil kar mu bari ta subuce mana cikin nida kai duk wanda ya samu damar kawar dashi kawai yayi.”
atare suka gyada kai tare da maida abun kunnensu suka cigaba da tafiya cikin sauri cikin haka suka hango anas yayi nasarar hard’e kafafun mutumin tare da saita kanshi da bakin bindiga ,da kai kamil yayiwa jubi alamar ya harbesa ai kuwa babu wani bata lokaci ya saita kanshi da bindiga zai harbi keyarsa yayinda shi kuma kamil ya kalli bayansa saboda tsaro dan kar wani daga cikin yaransu su
ya gansu ,adaidai lokacin sky ya sanyo kai ganinsa yasa kamil ya rike hannun jubi yayi kasa dashi ya harbin kafafun mutumin anas ya juyo da sauri cikin tsananin firgici sai dai ganinsu sune a bayansa yasa ya samu natsuwar zuciya ya maida hankalinsa ga
kafafun mutumin dake gabansa jini ne ke zuba kamar an yanka qaramar dabba “oga ya kuka tsaya anan kuzo mu qarasa mana “ya fad’a tare da wucesu ya qarasa inda anas yake wanda yayi nasarar kar'bar jakar hannun mutumin ya kallesu daya bayan daya yana cewa “waye yayi harbin acikinku ?”a dan rikice suka kalli junansu jubi ne yayi karfin hali cewa “kamil ne “ dan haka ya fuskanci kamil “gsky da bakayi harbin ba tunda gbdynmu ance kar muyi ya kamata mu dinga kiyayewa ya qarasa maganar yana cewa muje ko.”