Sashe 31
Kuskuren Baya Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
" ya mike tsaye yana cewa "zanyi nazarin akan haka yana gama fad'ar haka ya fita daga d'akin ta kwanta sharaf akan makeken gadonsa tana kuka tana tunanin yadda zata bar gidan ta kowani hali .Kai tsaye d'akin ajiya makamansa ya nufa Inda ya iske abokansa da yaransa suna zaman jiransa a hankali ya shiga yi musu bayanin Inda kowannensu zai tsaya da zarar sun Isa airport ya d'auki sama da awa biyu yana musu bayanin har sanda karfe goma shabiyu ta buga ya d'ago yana duba agogon dake d'aure a tsintsiyar hannunsa a natse ya d'auke kyawawan idanunshi ya d'aura akan Scorpio tare da bashi umarni "kaje ka siyowa tanweer abinci ya lumshe sexy eye's na second biyu sannan ya Bude ya jiyo ya Kalli eku "Kai Kuma kaje ma'ajiyin kudi ka diba ka siyo kayan d'anye abinci da duk abinda kasan za'a bukata na abinci ka tabbatar ka siyo "okay boss ".
gbdy abokansa suka zuba masa Ido kawai suna kallonsa cike da tsananin mamakinsa " kamil ne yayi karfin halin tambayarsa "me za'a yi da d'anye abinci Kuma ?""Wa wannan yarinyar ne ya bashi amsa atakaice yana furzar da iska , duk da yaki yarda da son yarinyar yake amman su sun fahimci matakin soyayyar da yakewa yarinyar , soyayya ce me zafi da wuyar bari, soyayya ce da mutun bai Isa ya iya barinta ba cikin dadin rai " jaguwa amman dai ...." saurin d'agawa anas hannu yayi saboda yasan me zai fito daga bakinsa "ya zaka katseshi ka barshi yayi magana mana ?".bazan barshi ba dan nasan maganarsa iska ce da shirme ya fad'a yana runtse idanuwanshi tare da shafa sumar kanshi . kamil yace "kenan mu din yan iskanka ne sannan mashiririta ? tsuke bakinsa yayi yana kallonsu d'aya byn daya yana girgiza musu Kai alamun a'a "haka ne mana jubi ya fad'a "ada Kai din mai son a fad'a maka gsky ne amman me yasa yanzu duk ka canza bafa ayi haka damu ba ,ba'ayi damu zamu d'auko yarinyar mutane mu ajiyeta ba meye ma amfanin rike musu yarinya idan kana son yarinyar why not ka fada mana mu san abunyi ?"no no jubi Sam babu wannan a raina ta ya ma zan d'aukarwa kaina soyayya soyayyar ma da diyar minster Sam Sam hakan ba me yiwu bane ?
"me yasa zaka fadi haka byn zuciya gareka kamar kowani halitta "kunga dan Allah ku bar maganar nan haka, bama zan iya wata soyayya ba a yanzu kawai dai Ina gudar mata sharrin wannan mutumin ne me Katon ciki ban San wani tuggu zai sake had'a mata ba Ina tausayinta Ina Jin kamar zai cutar daita ne Idan na mayar daita ",saboda zunzurutun qaunar da kake mata ba shiyasa kake Jin tausayinta ",oh my god jubril wai ya kuke min haka ne ?"idan Ina son yarinyar nan wallahi zan fad'a muku dan bamu Saba boyewa juna komai ba , ku yarda bana son yarinyar nan " shiru sukayi suka cigaba da kallonsa ba dan sun yarda dashi ba har ya juya ya kusan kofar fitar sannan yace " eku Scorpio "zaman munafurcin me kukeyi dan Allah ku tashe kuje kuyi abinda na sakaku bamu da lokaci " da sauri suka mike suna shafa kansu ."
Cikin takun Isa da Jin shi wani ne ya nufi haraban gidan hannunsa d'aya soke cikin aljihun wandonsa eku da Scorpio suka fice da sauri suka nufi Inda ya aikesu , yana nan tsaye yaga fitowar tanweer tana karewa haraban gidan kallo fuskarta d'auke da murmushin jin dadi ba kamar d'azu ba , a kallon da yake mata ya lura hankalinta na kan shukokin gidan ne ,yana kallonta ta cigaba da takawa a hankali har ta Isa Inda shukokin suke tana shafawa a hankali tana lumshe idanu , a natse ta karya kwana tabi hannunta na hagu ,cike da natsuwa ya biyo bayanta , bata tsaya koina ba sai gurin fararen fure dake shuke cikin ruwa har lokacin fuskarta da murmushi , ya k'araso ya tsaya a bayanta yana sauke numfashi, saukar numfashinsa yasa ta juyo a tsorace har qirjinta na ta'ba nashi saurin d'auke numfashi yayi qirjinsa na tsananta bugu , ganin shine tsaye yasa ta sauke naunauyen ajiyar zuciya sannan ta juya ta cigaba da kallon fararen fure muryarta a sanyaye tace " ina son fararen fure ko zaka tsinko min? ta fad'a tana duban Inda yake tsaye har lokacin hannunsa na soke cikin aljihunsa " kina son fure ne haka ? ya tmbyeta yana kare mata kallo tsab " sosai Ina qaunar fararen fure arayuwata ya qara taku biyu yayi kusa daita sosai yana cewa "yarinyar da nake so itama tana matukar son fure " qirjinta ne yayi wani irin bugawa da karfi , taji saukar maganarsa kamar saukar aradu ,zafi ta dinga ji a qirjinta tamkar ana diga mata ruwan dalma nan take ta nemi natsuwarta ta rasa idanunta na kan furen tace "wacece ita yarinyar da kake so ? ta tambayesa kwayar idanunta cikin nashi ,bai bata amsa ba duk da ya lura da canzawar da tayi a lokaci daya sakamakon jin yana son wata dariya taso subuce masa dan yadda ta had'e rai abun babu sauki kace shi din mijinta ne .
ranta a 'bace ta soma tafiya zuwa wani bangaren "ke Ina zaki ?itama banza tayi masa kamar yadda yayi mata "ba dake nake magana ba kina jina ? still banza ta masa " ki koma ciki kar na sake ganin kafafunki kin fito haraban gidan nan bare nan. "dan me yasa bazan fito ba ? ta fad'a a fusace tana Jin wani irin zafi mara misaltuwa sannan ta juyo ta fuskancesa fuskarta a had'e tamakr ba itace take murmushi a sakwanin da suka wuce ba , ta rasa dalilin wannan so da take masa , soyayyarsa me karfi ce agareta ,bata ta'ba sanin tana da kishin irin haka ba sai yanzu daya furta yana son wata ba ita ba yace baya son zahra sannan baya sonta to wacece wannan daya furta da bakinsa ? Ido cikin Ido suke kallon cikin kwayar idanun juna kamar ta rufesa da duka ko zata samu sausauci ,k'okarin danne kishin tayi ta sanyawa jikinta jarumta "ko bazanje koina ba ka barni na dinga fitowa Ina ganin fararen fure tayi mgnr kmr zatayi kuka ,bai ce mata Komai ba ya riko tsintsiyar hannunta ya soma tafiya daita bai tsaya a koina ba sai d'akinta ya bud'e kofar ya turata "iya nan na yarda kiyi rayuwa aciki ko falon gidan nan ban yarda ki fito ba idan Kuma kikayi kuskuren fitowa zaki ga abinda zan miki ya k'arasa maganar tare da ya janye kofar ya rufe garam , ita duk wannan abun da yayi bai dameta ba akan zance budurwa da yayi mata shi yafi komai ta'ba zuciyarta da d'aga mata hankali, tsaki taja yafi sau goma ajere " Allah! Allah !! ka tsi ...." shiru tayi ta kasa tsine masa shi da budurwar da yake so ta koma karshen gado ta zauna tare da zuba tagumi ."
ya shiga d'akinsa ya cire kayan jikinsa ya shiga wanka ya tsaya shiru cikin bathtube ruwa na tsiyaya a sansar jikinsa yana tunanin maganar abokansa akan yarinyar "duk suna min kallon d'an soyayya alhalin ba haka bane acikin zuciyarsa ," taimako ai ba soyayya ce? ya tambayi kanshi ya d'an dade ruwa na sauka ajikinsa sannan ya fito kugunsa d'aure da farin towel wanda bai wuce cinyoyarsa ba byn ya goge jikinsa
ya shafa body lotion yayi cumb din sumar kanshi ya soma shirya kansa cikin Kanana kaya riga blue wanda a gabansa aka rubuta polo 1967 yayinda wondon da canvers din kafafunsa suka kasance ja ,kansa sanye da facing cap ja kmr yadda rigar jikinsa yake , tsintsiyar hannunsa d'aure da agogon rolex ya rufe idanunshi da glass baki ya feshe ilahirin jikinsa da turare mai sanyi kamshi, sosai kyawunsa ya bayyana ya soke hannunsa daya cikin aljihun wandonsa kamar Koda yaushe ya nufi kofar fita, falon ya dawo Inda ya iske scopio ya dawo bai tsaya bata lokaci ba ya karbi farar ledar hannunsa ya juya zuwa d'akin da tanweer take ."
tana Jin shigowarsa amman taki d'agowa daga kwance da take dan wani irin haushinsa take ji ,ya ajiye ledar akan bedside yana cewa "ga abinci nan ki tashi kici sannan zanje wani aiki me mahimmanci zan dan dade kafin na dawo batare data d'ago ba tace "a dawo Lafiya amman dan Allah ka bani waya ". "ki daina damun kanki ba waya ba gidan ma zaki bari gbdy idan lokaci yayi ya juya ya fara tafiya cikin hanzarin wannan karon d'akin dake gefen d'akinsa ya shiga ya jima sosai dan kusan awa d'aya yayi sautin muryar scopio ya fito dashi "boss komai ya kammala "okay kana iya tafiya ya fad'a d'akin tanweer yana cewa " nasa a kawo komai na kayan abinci muje kiga kitchen din ". banza tayi masa taki cewa komai hakazalika taki tashi hatta abincin da ya kawo bata ci ba ya zuba mata Ido har kusan minti biyar kome ta tuna tayi zumbur ta mike tsaye tana dubansa yayi gaba ta biyosa a baya har cikin had'ad'd'en kitchen din ."
gbdy abokansa suka zuba masa Ido kawai suna kallonsa cike da tsananin mamakinsa " kamil ne yayi karfin halin tambayarsa "me za'a yi da d'anye abinci Kuma ?""Wa wannan yarinyar ne ya bashi amsa atakaice yana furzar da iska , duk da yaki yarda da son yarinyar yake amman su sun fahimci matakin soyayyar da yakewa yarinyar , soyayya ce me zafi da wuyar bari, soyayya ce da mutun bai Isa ya iya barinta ba cikin dadin rai " jaguwa amman dai ...." saurin d'agawa anas hannu yayi saboda yasan me zai fito daga bakinsa "ya zaka katseshi ka barshi yayi magana mana ?".bazan barshi ba dan nasan maganarsa iska ce da shirme ya fad'a yana runtse idanuwanshi tare da shafa sumar kanshi . kamil yace "kenan mu din yan iskanka ne sannan mashiririta ? tsuke bakinsa yayi yana kallonsu d'aya byn daya yana girgiza musu Kai alamun a'a "haka ne mana jubi ya fad'a "ada Kai din mai son a fad'a maka gsky ne amman me yasa yanzu duk ka canza bafa ayi haka damu ba ,ba'ayi damu zamu d'auko yarinyar mutane mu ajiyeta ba meye ma amfanin rike musu yarinya idan kana son yarinyar why not ka fada mana mu san abunyi ?"no no jubi Sam babu wannan a raina ta ya ma zan d'aukarwa kaina soyayya soyayyar ma da diyar minster Sam Sam hakan ba me yiwu bane ?
"me yasa zaka fadi haka byn zuciya gareka kamar kowani halitta "kunga dan Allah ku bar maganar nan haka, bama zan iya wata soyayya ba a yanzu kawai dai Ina gudar mata sharrin wannan mutumin ne me Katon ciki ban San wani tuggu zai sake had'a mata ba Ina tausayinta Ina Jin kamar zai cutar daita ne Idan na mayar daita ",saboda zunzurutun qaunar da kake mata ba shiyasa kake Jin tausayinta ",oh my god jubril wai ya kuke min haka ne ?"idan Ina son yarinyar nan wallahi zan fad'a muku dan bamu Saba boyewa juna komai ba , ku yarda bana son yarinyar nan " shiru sukayi suka cigaba da kallonsa ba dan sun yarda dashi ba har ya juya ya kusan kofar fitar sannan yace " eku Scorpio "zaman munafurcin me kukeyi dan Allah ku tashe kuje kuyi abinda na sakaku bamu da lokaci " da sauri suka mike suna shafa kansu ."
Cikin takun Isa da Jin shi wani ne ya nufi haraban gidan hannunsa d'aya soke cikin aljihun wandonsa eku da Scorpio suka fice da sauri suka nufi Inda ya aikesu , yana nan tsaye yaga fitowar tanweer tana karewa haraban gidan kallo fuskarta d'auke da murmushin jin dadi ba kamar d'azu ba , a kallon da yake mata ya lura hankalinta na kan shukokin gidan ne ,yana kallonta ta cigaba da takawa a hankali har ta Isa Inda shukokin suke tana shafawa a hankali tana lumshe idanu , a natse ta karya kwana tabi hannunta na hagu ,cike da natsuwa ya biyo bayanta , bata tsaya koina ba sai gurin fararen fure dake shuke cikin ruwa har lokacin fuskarta da murmushi , ya k'araso ya tsaya a bayanta yana sauke numfashi, saukar numfashinsa yasa ta juyo a tsorace har qirjinta na ta'ba nashi saurin d'auke numfashi yayi qirjinsa na tsananta bugu , ganin shine tsaye yasa ta sauke naunauyen ajiyar zuciya sannan ta juya ta cigaba da kallon fararen fure muryarta a sanyaye tace " ina son fararen fure ko zaka tsinko min? ta fad'a tana duban Inda yake tsaye har lokacin hannunsa na soke cikin aljihunsa " kina son fure ne haka ? ya tmbyeta yana kare mata kallo tsab " sosai Ina qaunar fararen fure arayuwata ya qara taku biyu yayi kusa daita sosai yana cewa "yarinyar da nake so itama tana matukar son fure " qirjinta ne yayi wani irin bugawa da karfi , taji saukar maganarsa kamar saukar aradu ,zafi ta dinga ji a qirjinta tamkar ana diga mata ruwan dalma nan take ta nemi natsuwarta ta rasa idanunta na kan furen tace "wacece ita yarinyar da kake so ? ta tambayesa kwayar idanunta cikin nashi ,bai bata amsa ba duk da ya lura da canzawar da tayi a lokaci daya sakamakon jin yana son wata dariya taso subuce masa dan yadda ta had'e rai abun babu sauki kace shi din mijinta ne .
ranta a 'bace ta soma tafiya zuwa wani bangaren "ke Ina zaki ?itama banza tayi masa kamar yadda yayi mata "ba dake nake magana ba kina jina ? still banza ta masa " ki koma ciki kar na sake ganin kafafunki kin fito haraban gidan nan bare nan. "dan me yasa bazan fito ba ? ta fad'a a fusace tana Jin wani irin zafi mara misaltuwa sannan ta juyo ta fuskancesa fuskarta a had'e tamakr ba itace take murmushi a sakwanin da suka wuce ba , ta rasa dalilin wannan so da take masa , soyayyarsa me karfi ce agareta ,bata ta'ba sanin tana da kishin irin haka ba sai yanzu daya furta yana son wata ba ita ba yace baya son zahra sannan baya sonta to wacece wannan daya furta da bakinsa ? Ido cikin Ido suke kallon cikin kwayar idanun juna kamar ta rufesa da duka ko zata samu sausauci ,k'okarin danne kishin tayi ta sanyawa jikinta jarumta "ko bazanje koina ba ka barni na dinga fitowa Ina ganin fararen fure tayi mgnr kmr zatayi kuka ,bai ce mata Komai ba ya riko tsintsiyar hannunta ya soma tafiya daita bai tsaya a koina ba sai d'akinta ya bud'e kofar ya turata "iya nan na yarda kiyi rayuwa aciki ko falon gidan nan ban yarda ki fito ba idan Kuma kikayi kuskuren fitowa zaki ga abinda zan miki ya k'arasa maganar tare da ya janye kofar ya rufe garam , ita duk wannan abun da yayi bai dameta ba akan zance budurwa da yayi mata shi yafi komai ta'ba zuciyarta da d'aga mata hankali, tsaki taja yafi sau goma ajere " Allah! Allah !! ka tsi ...." shiru tayi ta kasa tsine masa shi da budurwar da yake so ta koma karshen gado ta zauna tare da zuba tagumi ."
ya shiga d'akinsa ya cire kayan jikinsa ya shiga wanka ya tsaya shiru cikin bathtube ruwa na tsiyaya a sansar jikinsa yana tunanin maganar abokansa akan yarinyar "duk suna min kallon d'an soyayya alhalin ba haka bane acikin zuciyarsa ," taimako ai ba soyayya ce? ya tambayi kanshi ya d'an dade ruwa na sauka ajikinsa sannan ya fito kugunsa d'aure da farin towel wanda bai wuce cinyoyarsa ba byn ya goge jikinsa
ya shafa body lotion yayi cumb din sumar kanshi ya soma shirya kansa cikin Kanana kaya riga blue wanda a gabansa aka rubuta polo 1967 yayinda wondon da canvers din kafafunsa suka kasance ja ,kansa sanye da facing cap ja kmr yadda rigar jikinsa yake , tsintsiyar hannunsa d'aure da agogon rolex ya rufe idanunshi da glass baki ya feshe ilahirin jikinsa da turare mai sanyi kamshi, sosai kyawunsa ya bayyana ya soke hannunsa daya cikin aljihun wandonsa kamar Koda yaushe ya nufi kofar fita, falon ya dawo Inda ya iske scopio ya dawo bai tsaya bata lokaci ba ya karbi farar ledar hannunsa ya juya zuwa d'akin da tanweer take ."
tana Jin shigowarsa amman taki d'agowa daga kwance da take dan wani irin haushinsa take ji ,ya ajiye ledar akan bedside yana cewa "ga abinci nan ki tashi kici sannan zanje wani aiki me mahimmanci zan dan dade kafin na dawo batare data d'ago ba tace "a dawo Lafiya amman dan Allah ka bani waya ". "ki daina damun kanki ba waya ba gidan ma zaki bari gbdy idan lokaci yayi ya juya ya fara tafiya cikin hanzarin wannan karon d'akin dake gefen d'akinsa ya shiga ya jima sosai dan kusan awa d'aya yayi sautin muryar scopio ya fito dashi "boss komai ya kammala "okay kana iya tafiya ya fad'a d'akin tanweer yana cewa " nasa a kawo komai na kayan abinci muje kiga kitchen din ". banza tayi masa taki cewa komai hakazalika taki tashi hatta abincin da ya kawo bata ci ba ya zuba mata Ido har kusan minti biyar kome ta tuna tayi zumbur ta mike tsaye tana dubansa yayi gaba ta biyosa a baya har cikin had'ad'd'en kitchen din ."