← Book details Kuskuren Baya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 30 OF 160

Sashe 30

Kuskuren Baya Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Mika  jaguwa yayi  had'e da salati Ya  sake  kwakumeta tsam  ajikinsa yana sauke  numfashi a hankali kmr bazai bud'e Idanunsa ba amman dole ya bud'e sakamakon wayarsa dake Kiran sallah alamun lokacin sallah  yayi  ya bud'e tsumammamun idanunshi ya kunna wutar d'akin wanda yasa ta d'an motsa tana shigewa jikinsa hade da d'aura hannunta akan chest Kuma daidai nipples dinsa sauri d'auke numfashi yayi gabansa na faduwa  yayi shiru na tsawon lokaci yana tunaninta abubuwa dayawa akan yarinyar ya d'an dade kwance idanunshi biyu sannan ya  cire hannunta a chest dinsa ya sauko a natse ya karasa Inda wayoyinsa suke ya d'auki daya yana dubawa karfe bakwai saura na safe bai so  wannan lokacin ya taddashi a hotel din ba shi daya so tun asuban fari ya bar hotel din Kai tsaye bayi ya shiga ya fara da sakarwa jikinsa ruwa sannan ya dauro alwala ya fito ya saka kayansa ya Kalli gabas ya tadda sallah byn ya idar ya mike ya Isa Inda take kwance ya Kai hannuwansa tsakiyar kafafunta yana shafawa a hankali ta bud'e idanunta sakamakon jin damshin ruwan hannunsa na ratsata idanunshi cikin nata yace "tashi kiyi sallah lokaci na tafiya ta janyo bargo ta lullu'be jikinta sosai dan babu komai ajikinta  muryarta can kasa tace "okay  ka  miko min  towel na d'aura "Dan Allah malama  ki  tashi kije dauka karki bata min lokaci  ya k'arasa maganar a fusace  shagwabe fuska tayi kmr zatayi kuka  "babu komai ajikina fa tsaki yaja ya mike ya janyo towel ajikin kofar bayi ya jefa mata  a fuska  ta d'aura ta   soma k'okarin  saukowa  "kiyi sauri please Ina da appointment ya fad'a kwayar idanunshi na kanta  bata ce Komai ba ta nufi bayi yabi bayanta da kallo yana kallon every step of her komai nata dabam  ne ta had'u sosai ilarta dai rashin kunya har ta  shige bayi idanunshi na kanta  itama sai data yi wanka sannan ta dauro alwala ta fito a lokaci da yake waya da anas "karka damu ku bani minti ashirin yanzu zaku gani murmushi yayi yace "Kai anas me yasa ka fiyye damun kanka nace maka ba abinda kake tunani bane  shikenan koma dai menene ba abinda kake zato  bane  ya katse Kiran ya kira ammina Inda yake sheida mata Yana da aiki me mahimmancin da zashi shi da abokan aikinsa yana bukatar adduarta"Allah ya tsareku yasa ayi aiki cikin nasara amman dan Allah kabi a hankali kasan Kai ne rayuwarmu sannan  da zarar ka kammala da komai kazo
naganka karka ce sai karshen sati zaka zo gbdy "karki damu ammi inshallahu bazan Kai ba me zan taho Miki dashi ?".Shiru tayi  tana tunanin kafin daga baya tace "komai ka kawo amminka zatayi farinciki murmushi yayi yace "shikenan my happiness murmushi tayi daga bangarenta ta sake Aiko masa da addua komai dare idan na dawo zan kiraki karki yi bacci har sai Kinga kirana kinji ammina  tace "to Adnan inshallahu zan jira kiranka   sun d'auki  minti biyar suna waya har da kannensa ,sanda tanweer ta kammala shirinta taja ta tsaya tana kare masa kallon tsab  yana matukar burgeta yadda bai wasa da lamarin mahaifiyarsa  da kannensa a dan zamanta dashi ta fahimci yadda yake mugu mugun son mahaifiyarsa har sanda ya k'araso gareta ya riko tsintsiyar hannunta tana can duniyar tunani   kumatunta ya ja kadan tayi firgib  ta dawo natsuwarta tana sauke ajiyar zuciya  tsurawa juna idanu sukayi batare data ce masa komai ba
ya  nufi hanyar  fitowa daga d'akin daita tana  biye  dashi ."

Yana  fitowa haraban hotel din idanunshi suka ci karo da motar alqali  murfin motar a bude  wasu mutane na tsaye suna duba cikin motar ,sai lokacin ya tuna da yasa a tsare masa shi ,Kai  tsaye gurin motarsa ya nufa ya bude wa  tanweer gaban mota ta shiga  ta zauna ya rufe ya zagaya ya shiga bangaren direba ya shiga ya zauna ya tadda motar yana fitowa ya sawa motar wuta kamar Wanda zai tashi sama "kabi a hankali please  Ina matukar son rayuwata  domin  tana da matukar mahimmanci ga iyaye saboda nice duniyarsu  "Ina  da mahaifiya da kanne day day har guda uku  mafi soyuwa a zuciyata bazan so suyi  maraicina ba bare ki fada min  maganar banza yayi mgnr a tsawace yana dukan stearing motar shiru tayi tana zance zuci kafin daga bisani ta motsa  labbanta  a hankali  "kana son mahaifiyarka  da kannenka   sosai  ?" tayi maganar tana kallonsa da gefen Ido da kmr bazai yi mgn ba sai dai mahimmancin su ya wuce ya banzatar da  amsar  dan haka yace "kwarai  kuwa  ina matukar son mahaifiyata  da kannena  so na  gaskiya  son da bana Jin akwai wani mahalikin da yake wa ahlinsa "Amman shi ...."  maid your thought   karki  sake  furta komai akan  ahlina  ya fad'a yana  cigaba da murza stearing ,dole taja bakinta tayi shiru ".

cikin kankanin lokaci ya k'araso gida  Kai tsaye bangarensa ya wuce da tanweer ta tsaya tana dubansa "ki kwanta ki cigaba da baccinki nasan bai isheki ba "batun komawata  gida fa ?"zan maidake amman ba yanzu ba  ki bani lokaci tayi kicin kicin da ranta kamar wacce aka aikowa da sakon mutuwa  "gsky nifa na gaji wallahi gida nake bukata idan baka yarda ka maidani ba  zan bi ta kowani hanya na bar gidan nan  "ki gwada ki kigani idan hakan abu ne me sauki yayi mgnr tare da yin  shiru yana dubanta  dan tuni idanunta sun cicciko da ruwan hawaye "ban San me yasa kake min haka ba ,idan km kasan kana da dalilin rikeni ka fad'a min nasan zaman da nake yi amman bawai ka rikeni ba alhalin ni din ba muharamarka bace  ta k'arasa maganar tana jan numfashi da danne kukanta tabbas  jikina na bani akwai  sirrin da  kake boye min meye shi  Ina son sani ?".Tayi taku daya  biyu ta qaraso gabansa qirjinta na dokawa da matsanacin karfi ta cigaba da magana a natse zuciyarta na rawa "zuwa yanzu ya kamata ka sanar dani menene shi abinda kake k'okarin  boyewa " take jikinsa yayi sanyi kmr Wanda aka jefa cikin kankara "zuciyata ta fara jefo min abubuwa masu wuyar misaltuwa akanka  sai dai na shirya jin koma menene ta k'arasa maganar tana kuka dan ta kasa rike kukanta ."

ya Kai hannuwansa duka yana  qokarin zagaye kugunta ta zame jikinta  ta koma bakin gado ta zauna ta kife Kanta akan cinyarta  tana cigaba  da  kukanta ya k'araso ya janyo stood ya zauna a gabanta ya riko hannunta daya cikin nasa ta d'ago runannun idanunta ta zuba masa tana sauraron abinda zai ce sai daya furzar da iska mai zafi daga bakinsa sannan ya fara magana a natse kmr me koyon mgn  "kunnewanki  bazasu iya Jin dalili
ko sirrin dayasa nake rike dake a gidan  ba , hankalinki bazai iya dauka ba wallahi zuciyarki zata buga idan kikaji mafi alkhairinsa ki bar wannan maganar "na bar wannan maganar saboda me byn kana rike da rayuwata ka tsareni ka hanani naje ga iyayena alhalin suna cikin damuwar rashina ta k'arasa maganar tana fixge hannuwanta ya sake riko hannuwanta da sauri  "shikenan ki bani  lokaci kad'an  nasan dai bazaki sake d'aukar lakacin da kikayi tare dani  ba a gidan  nan ".  ya qarasa mgn Yana  goge mata  hawayenta dake tsiyaya a idanunta  tare da yin shiru yana  kallonta itama shi take kallo  zuciyarta  na zafi "to shikenan amman kayi min alfarma ka bani waya  Ina son Jin muryar iyayena ,Ina kwadayi jin muryarsu dan Allah karka ce a'a".
Chapter 30 · 0% Book details